Kashe tsaka-tsaka abune mai kyau ga dalilai daga cikin hadisai. ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 19 September 2017

Kashe tsaka-tsaka abune mai kyau ga dalilai daga cikin hadisai.

```KASHE TSAKA ABUNE MAI KYAU```
………………………………………………
*Zauren SA'ADATUL-MUSLIM*
.
الحمد لله رب العالمين والصلاة السلام على رسول الله صلى الله عليه وسلم وبعد
.
_'Yan uwa addinin musulunci Addini ne mai tsafta da son zama lafiya, don haka ne ya shar'anta mana wasu ababe da suka halatta mutum ya kashe su daga ciki ma akwai wanda idan ka kashe kana samun lada, daga cikin wadannan halittu akwai tsaka! Wacce Annabi saw ya kira ta da cewa lallaifa ita tsaka algun-guma ce  wacce kuma Annabi saw ya tabbatar mana da cewa lallaifa dukkan wanda ya kashe tsaka a duka guda daya rak! To yana da lada dari (100)_
.
_Saboda illolin ta tun kafin wannan lokacin tsaka tana da illah, daga cikin illolin ta ita tsaka bakin ta kamar abin walda ne idan ta samu dan adam yana barci har ta samu dāma ta huta idanun sa a wannan sanadin yakan sanya mutum ya makance! Illolin ta yana da yawa wanda ba sai mun ambata suba anan, to amma dame ake kashe tsaka? Amsa itace ana kashe tsaka ne da dukkanin abinda ya samu na duka ba wai dole sai tsin-tsiya ba aa koda ace da takalmi ne ko wani abu na duka wanda za'ayi mata duka daya ta mutu shi akeso, idan ma kasamu dama ya halasta maka idan kaganta akan hanya kayi tsalle ka hau kanta ta mutu dukkan hakan ya halatta babu hani akai_
.
_Daga cikin laddubar kashe tsaka itace anaso a lokacin da kaga tsala sai kayi kwadayin kasheta to kayi basmala wato kace Bismillahi sai ka kai mata duka idan Allah ya kaddara ajalinta yayi shi kenan sai ka ambaci Allah ka kasheta, ko meye dalilin yin Bismillah a lokacin da mutum namiji ko mace yayi nufin kashe tsaka?  Dalili kuwa shine saboda Al'janu suna zama tsaka, kuma sukan zama kunamu (scorpions) sukan zama macizai (snake's) saboda haka ne Annabi yace mutum ya ambaci Allah a lokacin da mutum ya nufaci kashe tsaka!_
.
_Wanda wata cuta ta sameshi akan yawan kashe tsaka da yakeyi, ko yayita surutai akan ita tsakar kamar ya dika cewa tana zuwa masa idan yana barci har yakan gaza kwana a daki shin meye mafita!?  To bayanan da zamu iyayi anan shine zamuce tun farko a bangaren kashe wannan tsakar ba'abiyo ta wancan ladabin ba da muka ambata na kashe irin wadannan halittu wato yin Basmala a yayin kashe ta, kuma hakan zai iya faruwa saboda kwadayin lada da dan adam yake yi a wajen Allah sai yayi nufin kashe tsaka ashe bai sani ba aljani ne kuma sai Allah ya kubutar da Aljanin wato shi wannan mutumin baisamu damar kashe wannan tsakar ba, to shi kuma aljani da yaga ya kubuta shi kenan sai ya dika zuwa yana razana wannan bawan Allah din da daddare, ina mafita?_
.
_Mafita ga wannan matsalar itace wannan bawan Allah din ya yawaita karanta Alqur'ani mai girma da kuma yawaita addu'o'i na sunnah domin neman tsarin Allah daga wannan sharri na aljani, kamar yawaita karanta suratul-Baqarah acikin gidan da kuma kiyaye addu'o'i musamman addu'ar kwanciya barci da sauran su, kamar yin al'walah a lokacin da mutum zai kwanta barci, ta wannan hanyar in Allah ya yarda za'a samu waraka da lafiya, muna rokon Allah madaukaki mai yin hukunci da kuma buwayarsa da hikimarsa yabaiwa masara lafiya, lafiya kuma ya karemu daga sharrin shaidanu maza da mata, Allah ne mafi sani, mahaifiya ta tana fama da rashin lafiya don Allah ku sanya ta acikin addu'o'in ku Allah yasa mudace,_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support