Me ake nufi da annamimanci !!?? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 19 September 2017

Me ake nufi da annamimanci !!??

```ME AKE NUFI DA ANNAMĪMANCI!?```
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
الحمد لله رب العالمين والصلاة والسلام على رسول الله صلى الله عليه وسلم، وبعد السلام عليكم ورحمة الله وبركاتة،
.
_Ma'anar Annamīmanci kamar yanda Imamuz-Zahabi ya fassara mana acikin Kabā'ir shine  "Jefa magana acikin mutane (wato ka fadi magana a tsakanin mutane) wacce zata haddasa 6arna a tsakanin su, wato magana ce wacce mutum zaiyi ta a tsakanin wadansu mutane guda biyu wacce zata haddasa rikici a tsakanin su, wannan shine ma'anar Annamīmanci"_
.
_Hukuncin yin Annamīmanci kan malamai ya hadu cewa harāmun ne, wato kakaf musulman duniya sun yarda cewa Annamîmanci haramun ne, akwai dalilai masu yawa da shari'a ta kallesu ta haramta shi daga littafan musulunci Qur'āni da Hadīsi da kuma Ij'mā'ī na malamai,_
.
_Allah madaukakin sarki yace acikin suratul Qalam, cewa "Kada kabi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce"  kuma yace  "Mai zunɗe, mai yãwo da gulma"  kunga wadannan ayoyin sun tabbatar mana da cewa mai Annamīmanci da Gulma dukkan su wulakantattu ne, 'yan uwa sanya gaba tsakanin musulmi yana da had'ari ba karami ba kuma masu irin wadannan ayyuka basu shiga Al'jannah,_
.
_Hadīsi ya tabbata acikin Bukhari da Muslim cewa lallai Annabi Swalallahu Alaihi Wasallam yace "Mai Annamimanci bazai shiga Al'jannah ba"  a wani hadisin kuma Annabi Saw ya wuce ta wajen wasu kaburbura guda biyu, sak yace  "Lallai su anayi masu Azabah kuma ba wai anayi masu azaba bane saboda wasu manya-manyan zunubbai da suka aikata bane, aa kawai dai daya daga cikin su ya kasance baya tsarkaka ne daga fitsari, amma kuma dayan ya kasance yana uawo ne da Annamīmanci, sannan sai Annabi saw ya tsinki wani danyen ganye ya rabasu biyu sai ya rabasu akan wadannan kaburbura, wato ya dorasu akan wadannan kaburburan, sannan yace ina fatan a saukaka masu azaba, har zuwa lokacin da wannan ganyen zai bushe" kunga wannan cewa da Annabi saw yayi cewa ba manyan zunubai bane, to ai abinda yasa ya fadi haka shine ganin yanda mutane suka daukeshi ba komai ba, amma akwai riwayar data rabbatar da cewa yace lallai fa wannan babban zunubi ne,_
.
_An samu ruwaya daga Abī-Hurairah Allah ya kara masa yarda yace, Annabi Saw yace  "Mafi sharrin mutane zaizo da fuska biyu, wanda zaizo ga wadancan da wannan fuskar sannan kuma yaje ma wadancan da wata fuskar da kuma abinda ya kasance yana fitowa daga barshen sa (wato gulma ko Annamīmanci) acikin wannan duniyar, to kusani wallahi ranar Qiyāmah Allah zai sanya harshen sa acikin wuta!"     Abinda ake nufi da cewa mai fuska biyu shine wanda zaizo wajen wani daga cikin mutane yayi masu wata magana wacce batada alaqa da zamantakewar al'ummah sai dai magana ta Annamīmanci ko Gulma, sannan kuma sai ya koma wajen wadancan suma sai ya bayyana masu cewa gashi gashi har dai takan haka musiiba ta samu ayi fitina, wacce zata sanya hakan a samu gābā a tsakanin jama'a wannan shine Annamīmanci!_
.
_Acikin suratul Hujurāt aya ta 6 Allah yana cewa  "Yãkũ waɗanda sukayi ĩmãni! Idan fãsiqi Yãzo muku da wani babban lãbãri, to, ku nẽmi bayãni, dõmin kada ku cũci waɗansu mutãne a cikin jãhilci, sabõda haka ku wãyi gari a kan abin da kuka aikata kunã mãsu nadãma"   lallai wanda ya dauki Annamīmanci dabi'ar sa har yabar duniya a ranar Qiyamah yanaji yana gani za'a dika dībar ladansa ana baiwa wadanda yayi gulmar su da Annamîmanci, yana ji yana gani malā'iku suna dībar ladarsa kuma bai isa ya hana ba, sannan sai Allah ta'ala yayi umarni a jefashi acikin wuta, Allah ya tsare mu_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp


Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support