HUKUNCIN SALLAR IDI A RANAR JUMU'AH!!! DAGA KWAMITIN BINCIKE NA ILIMIN ADDINI DA FATAWA NA KASAR SAUDIYA ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 1 September 2017

HUKUNCIN SALLAR IDI A RANAR JUMU'AH!!! DAGA KWAMITIN BINCIKE NA ILIMIN ADDINI DA FATAWA NA KASAR SAUDIYA



HUKUNCIN SALLAR IDI A RANAR JUMU'AH!!! DAGA KWAMITIN BINCIKE NA ILIMIN ADDINI DA FATAWA NA KASAR SAUDIYA
ﻭﺑﻨﺎﺀ ﻋﻠﻰ ﻫﺬﻩ ﺍﻷﺣﺎﺩﻳﺚ ﺍﻟﻤﺮﻓﻮﻋﺔ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ، ﻭﻋﻠﻰ ﻫﺬﻩ ﺍﻵﺛﺎﺭ ﺍﻟﻤﻮﻗﻮﻓﺔ ﻋﻦ ﻋﺪﺩ ﻣﻦ ﺍﻟﺼﺤﺎﺑﺔ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﻢ ، ﻭﻋﻠﻰ ﻣﺎ ﻗﺮﺭﻩ ﺟﻤﻬﻮﺭ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻓﻲ ﻓﻘﻬﻬﺎ، ﻓﺈﻥ ﺍﻟﻠﺠﻨﺔ ﺗﺒﻴﻦ ﺍﻷﺣﻜﺎﻡ ﺍﻵﺗﻴﺔ : 1- ﻣﻦ ﺣﻀﺮ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﻌﻴﺪ ﻓﻴﺮﺧﺺ ﻟﻪ ﻓﻲ ﻋﺪﻡ ﺣﻀﻮﺭ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ، ﻭﻳﺼﻠﻴﻬﺎ ﻇﻬﺮﺍً ﻓﻲ ﻭﻗﺖ ﺍﻟﻈﻬﺮ، ﻭﺇﻥ ﺃﺧﺬ ﺑﺎﻟﻌﺰﻳﻤﺔ ﻓﺼﻠﻰ ﻣﻊ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﻓﻬﻮ ﺃﻓﻀﻞ . 2- ﻣﻦ ﻟﻢ ﻳﺤﻀﺮ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﻌﻴﺪ ﻓﻼ ﺗﺸﻤﻠﻪ ﺍﻟﺮﺧﺼﺔ، ﻭﻟﺬﺍ ﻓﻼ ﻳﺴﻘﻂ ﻋﻨﻪ ﻭﺟﻮﺏ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ، ﻓﻴﺠﺐ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻌﻲ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﻤﺴﺠﺪ ﻟﺼﻼﺓ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ، ﻓﺈﻥ ﻟﻢ ﻳﻮﺟﺪ ﻋﺪﺩ ﺗﻨﻌﻘﺪ ﺑﻪ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﺻﻼﻫﺎ ﻇﻬﺮﺍً . 3- ﻳﺠﺐ ﻋﻠﻰ ﺇﻣﺎﻡ ﻣﺴﺠﺪ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﺇﻗﺎﻣﺔ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﻴﻮﻡ ﻟﻴﺸﻬﺪﻫﺎ ﻣﻦ ﺷﺎﺀ ﺷﻬﻮﺩﻫﺎ ﻭﻣﻦ ﻟﻢ ﻳﺸﻬﺪ ﺍﻟﻌﻴﺪ ، ﺇﻥ ﺣﻀﺮ ﺍﻟﻌﺪﺩ ﺍﻟﺘﻲ ﺗﻨﻌﻘﺪ ﺑﻪ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﻭﺇﻻ ﻓﺘﺼﻠﻰ ﻇﻬﺮﺍ . 4- ﻣﻦ ﺣﻀﺮ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﻌﻴﺪ ﻭﺗﺮﺧﺺ ﺑﻌﺪﻡ ﺣﻀﻮﺭ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﻓﺈﻧﻪ ﻳﺼﻠﻴﻬﺎ ﻇﻬﺮﺍً ﺑﻌﺪ ﺩﺧﻮﻝ ﻭﻗﺖ ﺍﻟﻈﻬﺮ . 5- ﻻ ﻳﺸﺮﻉ ﻓﻲ ﻫﺬﺍ ﺍﻟﻮﻗﺖ ﺍﻷﺫﺍﻥ ﺇﻻ ﻓﻲ ﺍﻟﻤﺴﺎﺟﺪ ﺍﻟﺘﻲ ﺗﻘﺎﻡ ﻓﻴﻬﺎ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ، ﻓﻼ ﻳﺸﺮﻉ ﺍﻷﺫﺍﻥ ﻟﺼﻼﺓ ﺍﻟﻈﻬﺮ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﻴﻮﻡ . 6- ﺍﻟﻘﻮﻝ ﺑﺄﻥ ﻣﻦ ﺣﻀﺮ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﻌﻴﺪ ﺗﺴﻘﻂ ﻋﻨﻪ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﻭﺻﻼﺓ ﺍﻟﻈﻬﺮ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﻴﻮﻡ ﻗﻮﻝ ﻏﻴﺮ ﺻﺤﻴﺢ، ﻭﻟﺬﺍ ﻫﺠﺮﻩ ﺍﻟﻌﻠﻤﺎﺀ ﻭﺣﻜﻤﻮﺍ ﺑﺨﻄﺌﻪ ﻭﻏﺮﺍﺑﺘﻪ، ﻟﻤﺨﺎﻟﻔﺘﻪ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻭﺇﺳﻘﺎﻃﻪ ﻓﺮﻳﻀﺔً ﻣﻦ ﻓﺮﺍﺋﺾ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﻼ ﺩﻟﻴﻞ، ﻭﻟﻌﻞ ﻗﺎﺋﻠﻪ ﻟﻢ ﻳﺒﻠﻐﻪ ﻣﺎ ﻓﻲ ﺍﻟﻤﺴﺄﻟﺔ ﻣﻦ ﺍﻟﺴﻨﻦ ﻭﺍﻵﺛﺎﺭ ﺍﻟﺘﻲ ﺭﺧﺼﺖ ﻟﻤﻦ ﺣﻀﺮ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﻌﻴﺪ ﺑﻌﺪﻡ ﺣﻀﻮﺭ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ، ﻭﺃﻧﻪ ﻳﺠﺐ ﻋﻠﻴﻪ ﺻﻼﺗﻬﺎ ﻇﻬﺮﺍً . ﻭﺍﻟﻠﻪ ﺗﻌﺎﻟﻰ ﺃﻋﻠﻢ . ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﻧﺒﻴﻨﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﻭﺳﻠﻢ . ﺍﻟﻠﺠﻨﺔ ﺍﻟﺪﺍﺋﻤﺔ ﻟﻠﺒﺤﻮﺙ ﺍﻟﻌﻠﻤﻴﺔ ﻭﺍﻹﻓﺘﺎﺀ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻌﺰﻳﺰ ﺑﻦ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﺁﻝ ﺍﻟﺸﻴﺦ .. ﺍﻟﺸﻴﺦ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﻦ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟﻐﺪﻳﺎﻥ .. ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺑﻜﺮ ﺑﻦ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﺃﺑﻮ ﺯﻳﺪ .. ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺻﺎﻟﺢ ﺑﻦ ﻓﻮﺯﺍﻥ ﺍﻟﻔﻮﺯﺍﻥ Gini akan hadisai da suka kai zuga Manzan Allah , da Ãsãr da suka zo daga sahabbai masu yawa Allah ya yarda da su, da kuma abinda jamhurin ma'abuta ilimi suka tabbatar a fik'hunsu lallai kwamitinnan tana bayyana hukunce hukuncennan masu zuwa:
1- Wanda ya halarci sallar idi anyi masa rangwame rashin halartar sallan juma'ah, zai sallaci azahar , in yayi riki karfi yayi sallar juma'ah tare da mutane shi yafi.
 2-wanda bai samu sallar idi ba wannan rangwamen bata kunsheshiba (shafeshi ba) , sabo da haka wajabcin Juma'ah bata fadi a kansaba, ya wajaba a kansa tafiya zuwa masallaci don sallar juma'ah, inbai samu adadin da ake kulla sallar juma'ah da shiba sai ya sallaci Azahar a matsayin juma'ah.
3- yana wajaba akan limamin masallacin juma'ah ya je don tsayar da sallar juma'ah na wannan yinin, don wadanda suke son halarta su halarta, da kuma Wanda bai bai samu halartar idi ba. In adadin da ake kulla sallar juma'ah sun halarta, in basu halartab sai suyi azahar.
 4- Wanda ya halarci sallar idi kuma ya bi rangwaman rashin halarta juma'ah: zai sallaceta a matsayin azahar bayan shigan lokacin Azahar.
 5- ba'a shar'anta kiran sallah a wannan lokaci ba sai a masallatan da ake tsayar da sallar juma'ah, ba'a shar'anta kiran sallan ga sallar Azahar din wannan yinin.
 6- maganar cewa: lallai Wanda ya halarci sallar idi: sallar juma'ah ta fadi gareshi a wannan yinin: maganace da ba ingantacceba, saboda haka malamiai suka suka kaurace masa suka yi hukunci da kuskurensa da kadaitakarsa, saboda sabawa sunnah da yayi da fadar da wani farali daga cikin farillai ba tare da daliliba, Ta iya kasancewa mai wannan maganar mas'ala daga sunnoni da Ãsar bai iso gareshiba, Wanda tayi rangwame ga Wanda ya halarci idi ba sai ya halarci sallar juma'aba , lallai ya wajaba a kansa ya sallaceta a matsayin Azahar. Allah madaukakin Sarki shine mafi Sani. Allah kayi salati da aminci ga Annabi Muhammd da iyalan gidansa da sahabbansa. Kwamitin tsababace don bincike na Ilimi da bada fatawa (kasar saudiya) Jagorori: :
1- Shiekh Abdul'aziz Bini Abdillah Ãli Shiekh. 2-Shiekh Abdullahi bini Abdirrahman Algaidãn. 3- Shiekh Bakr bini Abdillah Abu zaid. 4- Shiekh Salih bini fauzãn Alfauzãn. Fasara: IBRAHIM
ABU RADIYAH ANNIGERY.

KUCI GABA DA KASANCEWA DA WANNAN SHAFIN MUNA GODIYA GA ZIYARAR DA KUKE KAWOMA MANA MUN GODE.
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support