Illolin gulma 03 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 30 September 2017

Illolin gulma 03

```★★★ILLOLIN GULMA★★★```
~~~~~~~~~~3~~~~~~~~~~
*Zauren SA'ADATUL-MUSLIM*
.
_Muna magana akan gulma da kuma Illolin ta wanda yanzu Zamu cigaba in Allah ya yarda_
.
_Jama'a kada mu manta fa musulmi Allah ta'ala ya daukaka darajarsa, ta 6angaren jininsa haramun ne wani musulmi ya zubar masa haka kuma dukiyar musulmi haramun ne wani dan uwa musulmi yaci, haka kuma mutuncin musulmi harāmun ne wani dan uwa ya zubar masa, kai komai ma na musulmai haramunne akan kowwane musulmi, to amma bari muji maganar Allah ta'ala akan gulma kuma muji yaya Annabi saw ya fassara mana ma'anar kalmar gulma, Allah ka tsare mu_
.
_Allah madaukakin sarki yana cewa acikin suratul Hujurāt aya ta 12,_
.
*يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اجْتَنِبُوا كَثِيرًا مِّنَ الظَّنِّ إِنَّ بَعْضَ الظَّنِّ إِثْمٌ ۖ وَلَا تَجَسَّسُوا وَلَا يَغْتَب بَّعْضُكُم بَعْضًا ۚ أَيُحِبُّ أَحَدُكُمْ أَن يَأْكُلَ لَحْمَ أَخِيهِ مَيْتًا فَكَرِهْتُمُوهُ وَاتَّقُوا اللَّهَ ۚ إِنَّ اللَّهَ تَوَّابٌ رَّحِيمٌ*
.
_'Yan uwa wallahi Gulma tana cikin Kabā'ir saboda Allah cewa yayi   "Yãkũ waɗanda sukayi ĩmãni! Ku nĩsanci abu mai yãwa na zato. Lallai sãshen zato laifi ne, Kuma kada ku yi rahõto, kuma kada sãshenku yãyi gulmar sãshe. Shin, ɗayanku nã son yã ci naman ɗan'uwansa yanã matacce? To, kunkĩshi (cin nãman). Kuma ku bi Allah da taqawa, Lallai Allah Mai karɓar tũba ne, Mai jinkai"     'yan uwa kunga Allah cewa yayi  "Kada sashen ku yayi Gulmar sashe"  kenan umarni ne akeyi mana anan, to amma kada na tari numfashin ku bari muji yanda Annabi Saw ya fassara mana cikakkiyar ma'anar kalmar Gulma!_
.
_Hadisi ya tabbata acikin sahīhu Muslim hadisi na 2589 Annabi saw ya tambayi sahabban sa Allah ya kara masu yarda  cewa  "Shin ko kunsan me ake nufi da Gulma kuwa? Sahabbai suka bayar da amsa cewa Allah da Manzon sa ne kadai suka sani, sai Annabi saw yace masu  "Ka ambaci dan uwanka da abinda idan yana nan ka ambata ranshi bazaiji dadi ba, Annabi yace wannan shine abinda akece ma Gulma, wato magana ce wacce idan 'yar uwanki tana wajen sai kika fadi wannan magana akanta to ranta bazataji dadi ba,  sai wani daga cikin sahabbai yace, "To kuma idan abinda nafada akansa gaskiya ne fa?  Sai Annabi saw ya bashi amsa da cewa idan abinda ka fada akan dan uwanka gaskiya ne! To hakīka kayi gulmarsa, idan kuma abinda kafada akan sa ba haka bane to kayi masa kage inji Annabi Muhammad saw,"   dan uwa kadaiji fa Annabine ya fassara cikakkiyar ma'anar Gulma, to mu ya muke a yau?_
.
_Zamu dakata anan sai mun hadu a darasi na gaba_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp ‬
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support