Shin wajibi ne azumin Ashura!?? Saadatul muslim ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Thursday 28 September 2017

Shin wajibi ne azumin Ashura!?? Saadatul muslim

```SHIN WAJIBI NE AZUMIN ĀSHURA? !```
...........................................
*Zauren SA'ADATUL-MUSLIM*
.
_Da sunan Allah mai rahama mai jin kai, Lallai azumtar ranar Ashura ba wajibi bane 'yan uwana sai dai wannan azumi ne wanda Annabi saw ya azumce shi kuma ya kwadaitar cewa a azumci wannan rana wato goma ga watan Al-muharram wanda yayi dai dai da ranar asabar mai zuwa in Shaa Allah, Annabi saw ya kwadaitar da ayi azumi a wannan rana ta Ashura wanda 'yan sha-biyu suke barnatar da jinainan su wajen saba ma Allah da kuma wahalar da kai, Imam Malik acikin Muwadda shafi na 163 karkashin Littafin Azumi hadisi na 824 yace Lallai labari yazo masa cewa lallai babban sahabin Annabi Umar dan Khaddab ya aika wajen Harith dan Hisham cewa lallai fa gobe itace ranar Ashura, don haka kayi azumi kuma ka umarci iyalanka cewa suyi azumi" 4 don haka wannan Sunnah ce amma fa mai karfi zamu ambaci hadisai guda biyu Akan haka in Allah ya yarda_
.
_Azumin a ranar Ashura Sunnah ce mai karfi Imam Bukhari ya ruwaito ingantaccen hadisi daga Ummuna Aisha Allah ya kara mata yarda tace, ranar Ashura ta kasance rana ce da Quraishawa suka kasance Suna azumtar wannan rana tun lokacin jahiliyyah, shi kuma Manzon Allah saw ya kasance yana azumtar wannan rana tun a jahiliyyah, lokacin da Annabi saw yazo garin Madinah sai yaci gaba da azumtar wannan rana kuma yayi umarni da cewa a azumce ta amma a lokacin da aka wajabta Ramadan sai ya kasance Ramadan shine Azumin da aka wajabta sai akabar azumtar Ashura ya zama Sunnah, duk wanda yaso ya azumci wannan rana ta Ashura wanda kuma yaso ya barta" (Bukhari 2002 Muslim 1125)_
.
_Hadisi ya inganta daga Abdirrahman dan Auwf Allah ya kara masa yarda yace lallai shi yaji Mu'awiyah bin Abi-sufyan a ranar Ashura a shekarar aikin hajji a lokacin shi yana Akan mimbari yana cewa "Yaku 'yan garin Madinah Ina malaman ku suke? naji Manzon Allah saw yana magana dangane da ranar Ashura cewa the" Wannan itace ranar Ashura kuma Allah bai wajabta maku Azumtar sa ba amma fa kusani ni Ina Azumi ga duk wanda yaso daga cikin ku to yayi Azumi, wanda kuma yaso daga cikin ku to yasha abin shansa, ma'ana yaci gaba da cin abincin sa" (Bukhari 2003 Muslim 1169)_
.
_Don haka dai 'yan uwa Sunnah ce kuma ku tunatar da' yan uwanku dangane da wannan Azumi na ranar goma ga watan Al-muharram domin su azumce shi kuma ayi don Allah domin neman yardan sa, Allah yasa mudace_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp


Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support