September 2017 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 30 September 2017

(Mp3)Al-qunut:Alaramma Ahmed Ibrahim sulaiman kano



AL-QUNUT AL-QUNUT

Tare da:
Alaramma Ahmed sulaiman ibrahim kano

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya
Share:

Hukuncin yin anko a musulunci

*HUKUNCIN YIN ANKO A MUSULUNCI*

*Tambaya*
.
Assalamu Alaykum.
Dan Allah malam menene hukuncin anko da ake yi a biki.shin ya halatta.
.
*Amsa*
.
Anko al'ada ce ta mutane bata da alaqa da addini, saboda haka in dai ba wata barna ta bayya a cikinsa ba babu laifi.
Shari'ar musulunci ta ba al'adun mutane mahimmanci da kula.
Abin da zai iya maida anko ya zama bai halasta ba kamar: mata sui shigar maza ko akasi, ko ya zama akwai bayyana tsaraici. , ko makamancin haka.
.
Allah ya fi sani.

*BIKIN SAUKAR AL-QURNI*
.
*Tambaya*

Assalamu Alaykum.
Dan Allah malam menene sharia tace akan bikin saukar Al-qur'aani? Sai kaga a yi taro harda bada allo.da dai sauransu
.
*Amsa*
.
Babu laifi ayi bikin saukar Qur'ani, domin abu ne na maslaha ita kuwa shari'a tana kula da maslaha a rayuwar mutane.
Wannan saukar na qarfafar wasu suma su dage su sauke ko haddace Qur'anin nan gaba.
Kwamitin bada fatawa na din-din -din na Qasar Saudia ya ce babu laifi in an aikata haka.

Allah ya fi sani.
*Amsawa : ✍*

*MAL. BASHEER LAWAL MUHAMMAD ZARIA.*



*Daga  ZAUREN FIQHUS SUNNAH*
Share:

(Mp3)The angels and jinn - Bilal Philips

Abu Ameenah Bilal Philips, is a Jamaican-born Canadian Muslim teacher, speaker, and author who lives in Qatar. He appears on Peace TV, which is a 24-hour Islamic satellite TV channel.

LECTURE LECTURE 

(The angels and jinn )

With:-
Sheikh abu ameenah Bilal philips

Share:

(Mp3)The prophet - Bilal philips

Abu Ameenah Bilal Philips, is a Jamaican-born Canadian Muslim teacher, speaker, and author who lives in Qatar. He appears on Peace TV, which is a 24-hour Islamic satellite TV channel.

LECTURE LECTURE 

(The prophet )

With:-
Sheikh abu ameenah Bilal philips

DOWNLOAD AUDIO NOW
Share:

(Mp3)Judgment day- the heaven & hell - Bilal Philips

Abu Ameenah Bilal Philips, is a Jamaican-born Canadian Muslim teacher, speaker, and author who lives in Qatar. He appears on Peace TV, which is a 24-hour Islamic satellite TV channel.

LECTURE LECTURE 

(Judgment day- the heaven & hell)

With:-
Sheikh abu ameenah Bilal philips

DOWNLOAD AUDIO NOW


Share:

Illolin gulma 06

```★★★ILLOLIN GULMA★★★```
~~~~~~~~~~6~~~~~~~~~~
*Zauren SA'ADATUL-MUSLIM*
.
_Cigaba_
.
_Akwai wani hadisi da Annabi saw yake bayar da labari akan abinda zai faru a ranar Alqiyāmah, yake cewe  "Mutum ne za'azo dashi ranar tashin Al'qiyamah gashi yayi sallah cikakka kuma yayi azumi cikakke kuma ya bayar da dukiyar sa a hanyar Allah, wata kīla ma yaje aikin hajji, gashi a filin qiyamah ayyuka na kwarai Alhamdulillah, to amma dai matsalar sa itace ya zagi wannan sai a dibi ladarsa a baiwa wanda ya zaga, haka kuma kuma yayi ma wani Qazafi shima nan sai a dībi ladarsa a baiwa wanda yayi ma Qazafin, haka kuma yaci dukiyar wani shima nan a debi ladan sa a baiwa wanda yaci dukiyar sa, haka kuma yayi gulmar wani shima anan a debi ladarsa a baiwa wanda yayi gulmar, haka kuma ya zubar da jinin wani shima nan sai a debi ladarsa a baiwa wanda ya zubar da jinin sa, haka kuma ya bugi wani shima a debi ladansa a baiwa wadanda ya zalunta, a haka malā'iku zasuyi ta dībar ladansa ana rarrabarwa amma bai isa ya hana ba, sai a samu gashi da yana da lada amma fa sun kare saboda zaluncin daya aikata yau gashi ya koma ziro, Annabi yace wannan mutumi shine fallasashshe wanda asirinsa ya gama tonuwa kai karshen Al'amari dai makomar sa itace wutar jahannama!" Allah ya tsare mu_
.
_'Yar uwa kamar yadda muka fada a baya cewa Allah ta'āla ya haramta gulma, to ga wani hadisi mai tsoratarwa wanda Abū-Hurairah ya jiyoshi daga Annabi saw, Lallai Annabi saw yace  "Lallai mutum zaiyi tayin magana da wata kalma wacce Allah ya yarda da ita, ba tare da yasani ba ko yanaga ba komai bane to kuma saboda wanban kalmar da yake furtawa sai Allah ya ta'ala ya daukaka darajarsa da ita wannan kalmar,  sannan kuma yace lallai wani bawan Allah, wato wani mutum zaiyi tayin wata magana da wata kalma wacce take acikin abinda Allah ya hana wato Allah bayason kalmar kuma shi da yake amfani da wannan kalmar a tunanin sa ba komai bane amma a haka ita wannan kalmar sai ta zama sanadin sa na shiga wutar jahannama!"  Wannan hadisi ne ingantacce yana cikin Sahīhul Bukhāri hadīsí  na 6478 sannan yana cikin Musnad da Imām Ahmad mujalladi na 2 shafi na 334,  wallahi 'yan uwa daga cikin kalmomin da Allah bayaso Gulma tana cikinsu,_
.
_Lallai dan uwa na da kuma ke 'yar uwa ta ku karkade kunnuwan ku kuji abinda zan sanar daku, wannan abin da zan fada yanzu shi yakamata mutane su dika fadawa 'yan uwansu idan sunzo masu da labari sannan zamu doshi kadan daga magabata muji abinda suka nuna mana dangane da illar harshe da kuma musībar gulma, ku kasance kuna fada ma 'yan uwanku cewa  *Dukkan mu ko ni kaina ko kai ko ke dukkan mu kakaf dinmu duk wanda yasan idan zaiyi magana acikin mu amma kuma yasan ba alkhairi bace to kawai yayi shirū mu abinda mukafi so kenan domun tanan ne zamu samu kāriya daga musība da take tattare da Gulma*     An samu inganracciyar riwaya daga Ibn Umar yana cewa  "Kashedin ku da yawan magana,"  haka kuma Imāmun-Nakha'ī yana cewa  "Mafi yawan mutane sun hallaka saboda yawan dukiya da kuma yawan magana"_
.
_Har wayau an samu asar daga Imamu Annakha'i yake cewa  "Lallai yawaita magana  a wajen da babu wata bukatar hakan, yana sanya kekashewar zuciya,"  ida kika fito gidan wance ina zaki gidan wance!  Wallahi idan ka bībiya babu abinda takeyi sai gulma, kawai ita ta zama uwar Gulma a gari bata anan bata acan ke kuwa!?    An samu wata riwaya daga salman Allah ya kara masa yarda wani mutum yace ma Salmān kayi min wasiyya yakai Salmān, a lokacin da Salmān ya tashi bashi amsa sai yace masa "Kada ka kuskura ka dika yin magana!  Sai wannan mutum yace to ni kuwa ya zanyi da jama'a dangane da bukatu na yau da kullum idan naqi nayi magana, yana fadar haka sai Salmān yace masa to kuwa kasani idan dai har zakayi magana to kayi magana da gaskiya, banda Gulma ko Annamīman ci ko karya aa kayi magana da gaskiya ko kuma kayi shiru inji Salmān Allah yayi masu rahamah_
.
 _Zamu dakata anan sai mun hadu a darasi na gaba_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp ‬


Share:

Illolin gulma 05

```★★★ILLOLIN GULMA★★★```
~~~~~~~~~~5~~~~~~~~~~
*Zauren SA'ADATUL-MUSLIM*
.
_Muna bayani akan Illolin Gulma Zamu cigaba in Allah ya yarda_
.
_Lallai dan uwa wajibi ne ka dika kiyaye harshen ka wajen fadin alkhairi Imamu Dabarānī ya ruwaito hadisi daga Aswad dan Asram Al-mahāribī yace ni kuwa sai nace ya manzon Allah kayi min wasiyyah, sai Annabi saw yace  "Shin ka kiyaye harshen ka?" Ni kuma sai na bashi amsa cewa " Ni kuwa mai zan kiyaye idan har ban kiyaye harshe na ba ya Annabin Allah? Sai Annabi yace  "Shin ka kiyaye hannuwan ka?  Ni kuwa sai na amsa da cewa "Me zan kiyaye idan ban kiyaye hannuwa na ba? Sai Annabi yace  "Kada ka kuskura kafadi wata magana da harshen ka sai dai abu mai kyau na alkhari kuma kada ka kuskura ka shimfida hannuwan ka sai dai zuwa ga aikin Alkhairi"  wannan hadisi ne Hasan Haisamī ya kawo shi acikin Maj'moo' mujalladi na 10 shafi na 303 hadisi ne ingantacce,  'yan uwa kunga wannan hadisin kai tsaye ya nuna mana haramcin gulma!_
.
_Kai wallahi ina sanar daku illar gulma,  cewa imanin dayanku baya inganta har sai mutum ya kiyaye harshen sa, 'yan uwa kada kuga kamar maganar tayi girma,  akwai hadīsī acikin Musnad na Imam Ahmad duk da wasu malaman Hadīsai sun raunata Hadīsin, hadisi ne na Anas Allah ya kara masa yarda yace Annabi Saw yace "Imanin bawa baya dai-dai tuwa har sai ya dai-daita zúciyar sa, to amma fa kusani zúciyar bawa bata dai-dai tuwa dole sai ya kiyaye harshen sa"  akwai wani hadisi wanda ya inganta  Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya kira magulmata da cewa  "Yaku wadanda sukayi Imani da Harshen su alhali zuciyar su batayi Imani ba? Sai Annabi yace sune wadanda suke yin Gulmar 'yan uwa, kuma suke wulakanta su_
.
_'Yar uwa kinji fa wadanda sukayi Imani da harshen su amma Zuciyoyin su basuyi imani ba sune magulmata!  To mu yanzu yaya muka dauki gulma, kamar yanda na fada maku cewa wallahi hatta wadanda suka siffantu da Ilimi acikin mālamai akan samu magulmata acikin su, 'yan uwa sai daifa mu nemi tsarin Allah, wallahi gulma tana da hatsari, kai wallahi bari kuji aljannah dakan ta ta'allaqa ne ga masu kiyaye harshe akwai Hadīsai acikin Bukhari da Muslim  Annabi saw yace  "Na lamince Aljannah ga duk wanda ya kiyaye harshen sa da kuma abinda yake a tsakanin cinyoyin sa (wato Al'aura)"   kunji kenan idan muka dauki wannan hadisin zamu fahimci cewa ashe ita kanta Aljannah mutum bazai sameta ba har sai ya kiyaye harshen sa,_
.
_' Yan uwa ga wani hadisi mai tsoratarwa da yazo acikin Sahīhul Bukhari Hadīsi na 6477 da kuma Muslim Hadīsī na 2988  hadisin Abu-Hurairah Allah ya kara masa yarda yace Manzon Allah saw yace  "Lallai mutum zaiyi tayin wata magana da wata kalma wacce baisan hatsarin dake cikin ta ba, bazai gushe ba sai wannan kalmar tayi sanadin shi na shiga wutar jahannama yana mai dawwama acikin ta wacce tsawon inda za'a saka shi yakai nīsan da yake tsakanin gabas da yamma"  wannan hadisin yana cikin littafin Jāmi'ul-Ulūm Wal-Hikam shafi na 217 karkashin sharhin hadīsī na 15,  to 'yar uwata yaya matsayin gulmar abokiyar zaman mu da muke yi bayan mun sani Allah ya haramta gulma!?_
.
_Sannan Akwai wani Hadīsi da Imam Tirmidī ya ruwaito acikin Sunan a babin Zuhdu hadisi na 2314 Annabi saw yace  "Lallai mutum zaiyi tayin magana da wata kalma shi a wajenshi wannan maganar da yake yi babu wani abu na laifi, a haka yake daukar kalmar ta sanadin wannan kalmar sai a jefashi acikin wuta wacce nīsan ta yakai tsawon shekara saba'in 70"  hadisi ne ingantacce daga Abu-Hurairah,   don haka nefa Annabi yace koda ace laifin dan uwanka ne ka ambata to kayi gulma,!_
.
 _Zamu dakata anan sai mun hadu a darasi na gaba_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp ‬


Share:

Illolin gulma 04

```★★★ILLOLIN GULMA★★★```
~~~~~~~~~~4~~~~~~~~~~
*Zauren SA'ADATUL-MUSLIM*
.
_Muna bayani akan gulma kuma mun fadi yanda Annabi saw ya fassara mana cikakkiyar kalmar gulma_
.
_Kunga kenan mu sai dai muce Allah ta'ala ya tsare mu, domin kuwa yanda muke yin mu'amala da gulma ya subhanallah,  'yar uwa ta dan uwa na Annabi ne fa ya fassara mana ma'anar kalmar gulma cewa, magana ce wacce zaka fada akan dan uwanka gashi kuma aikin sa ne fa kafada amma idan yana wajen ransa bazaiji dadi ba, to ida kuwa haka ne su waye yanzu basuyin gulma yaku ja'ama?  Mutum ne zaka sameshi gashi da siffa ta mutanen kirki amma kuma sai kasameshi da siffa ta magulmata,  kamar yanda mata suke mu'amalar 'yan uwansu a wannan bangaren har idan aka samu wata tana kokarin yi masu nasiha sai suce ai akinta ne da batayi ba da baza'a fada ba, 'yar uwa wallahi wannan Gulma ne Allah ya hana, domin kuwa Allah cewa yayi  "Kada sashin ku yayi gulmar sashi" don haka kalar wannan gulmar haramun ne inji Annabi Muhammad saw,_
.
_Lallai idan muka dauki wannan fassara ta Annabi saw akan gulma to ashe kunga kenan wajibi ne mu tsaya mu kiyaye harshen mu domin kuwa kada balā'i ya sauka akan mu, muna neman tsarin Allah_
.
_Al-Imam Al-Hasanul-Basary babban tabi'ī daga cikin tabi'ai Allah yayi masa rahama yana cewa  "Yin magana akan wannan matsal kala uku ce, wanda kuma kakaf dinsu harāmun ne abu na farko shine ita kanta Gība din wato Gulma!  Na biyu kuma Kazafi abu na uku itace Karya,"  wato labari ne yazo ya sameka cewa wanefa yana aikata kaza, kai kuma sai kadauki wannan labarin kana yadawa, to wallahi wadannan kakaf dinsu harāmun,  'yan uwa ayi hakuri zamu ambaci dalīlai kadan da suke tabbatar mana da haramcin wadannan abubuwa in shaa Allahu,_
.
 _Abu na farko da zamu fara ambata shine wani hadisi swahīhī wanda kowwannen mu yasan wannan hadisin wanda Imam Bukhari ya ruwaito hadisin mai lamba 6018 a babin Ladubba, shi kuma Imam Muslim a Babin Imāni hadisi na 47  shi kuma Imam Tirmidhī acikin Sunan Babin da yake magana akan Qiyāma hadisi na 2500 hadīsin Abdirrahman Ibn Sakhr wato Abu-Hurairah Allah ya kara masa yarda, yace lallai Annabi saw yace  "Duk wanda yayi Imāni da Allah da rana ta karshe  to ya fadi Alkhairi ko yayi shiru"   kunga kenan a karkashin wannan hadisin zamu fahimci cewa magulmata Imānin su da Allah ta'ala akwai saura ba cikakken Imani suke dashi baga Allah domin Annabi ne ya fada,  'yan uwa gulma fa tana da hadari, kawai dai mu nemi tsarin Allah Madaukaki,_
.
_Zamu dakata anan sai mun hadu a darasi na gaba_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp ‬

Share:

Illolin gulma 03

```★★★ILLOLIN GULMA★★★```
~~~~~~~~~~3~~~~~~~~~~
*Zauren SA'ADATUL-MUSLIM*
.
_Muna magana akan gulma da kuma Illolin ta wanda yanzu Zamu cigaba in Allah ya yarda_
.
_Jama'a kada mu manta fa musulmi Allah ta'ala ya daukaka darajarsa, ta 6angaren jininsa haramun ne wani musulmi ya zubar masa haka kuma dukiyar musulmi haramun ne wani dan uwa musulmi yaci, haka kuma mutuncin musulmi harāmun ne wani dan uwa ya zubar masa, kai komai ma na musulmai haramunne akan kowwane musulmi, to amma bari muji maganar Allah ta'ala akan gulma kuma muji yaya Annabi saw ya fassara mana ma'anar kalmar gulma, Allah ka tsare mu_
.
_Allah madaukakin sarki yana cewa acikin suratul Hujurāt aya ta 12,_
.
*يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اجْتَنِبُوا كَثِيرًا مِّنَ الظَّنِّ إِنَّ بَعْضَ الظَّنِّ إِثْمٌ ۖ وَلَا تَجَسَّسُوا وَلَا يَغْتَب بَّعْضُكُم بَعْضًا ۚ أَيُحِبُّ أَحَدُكُمْ أَن يَأْكُلَ لَحْمَ أَخِيهِ مَيْتًا فَكَرِهْتُمُوهُ وَاتَّقُوا اللَّهَ ۚ إِنَّ اللَّهَ تَوَّابٌ رَّحِيمٌ*
.
_'Yan uwa wallahi Gulma tana cikin Kabā'ir saboda Allah cewa yayi   "Yãkũ waɗanda sukayi ĩmãni! Ku nĩsanci abu mai yãwa na zato. Lallai sãshen zato laifi ne, Kuma kada ku yi rahõto, kuma kada sãshenku yãyi gulmar sãshe. Shin, ɗayanku nã son yã ci naman ɗan'uwansa yanã matacce? To, kunkĩshi (cin nãman). Kuma ku bi Allah da taqawa, Lallai Allah Mai karɓar tũba ne, Mai jinkai"     'yan uwa kunga Allah cewa yayi  "Kada sashen ku yayi Gulmar sashe"  kenan umarni ne akeyi mana anan, to amma kada na tari numfashin ku bari muji yanda Annabi Saw ya fassara mana cikakkiyar ma'anar kalmar Gulma!_
.
_Hadisi ya tabbata acikin sahīhu Muslim hadisi na 2589 Annabi saw ya tambayi sahabban sa Allah ya kara masu yarda  cewa  "Shin ko kunsan me ake nufi da Gulma kuwa? Sahabbai suka bayar da amsa cewa Allah da Manzon sa ne kadai suka sani, sai Annabi saw yace masu  "Ka ambaci dan uwanka da abinda idan yana nan ka ambata ranshi bazaiji dadi ba, Annabi yace wannan shine abinda akece ma Gulma, wato magana ce wacce idan 'yar uwanki tana wajen sai kika fadi wannan magana akanta to ranta bazataji dadi ba,  sai wani daga cikin sahabbai yace, "To kuma idan abinda nafada akansa gaskiya ne fa?  Sai Annabi saw ya bashi amsa da cewa idan abinda ka fada akan dan uwanka gaskiya ne! To hakīka kayi gulmarsa, idan kuma abinda kafada akan sa ba haka bane to kayi masa kage inji Annabi Muhammad saw,"   dan uwa kadaiji fa Annabine ya fassara cikakkiyar ma'anar Gulma, to mu ya muke a yau?_
.
_Zamu dakata anan sai mun hadu a darasi na gaba_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp ‬
Share:

Illolin gulma 02

```★★★ILLOLIN GULMA★★★```
~~~~~~~~~~2~~~~~~~~~~
*Zauren SA'ADATUL-MUSLIM*
.
_Wannan shine bayani na biyu kuma muna magana akan Gulma_
.
_Gulma fa jama'a ina kara jaddada mana cewa wallahi gulma yanda ta yawaita acikin wannan Al'ummar babu maza ballan tana mata, kai babu manya ballan tana kanana, abin yakai ya kawo hatta acikin masallatayyar mu an mayar dasu wajaje na gulma, abin dai ya zama kamar wani Ibadah duk inda zakaji ance ga wani majalisi, to wallahi zaka samu ba majalisi bane wajen gulma ne, matsalar ba anan kadai ba hatta acikin makarantu na Islamiyya an mayar dasu sun zamo wajajen gulma, kai 'yan uwa abin fa kamar gāsa akeyi hatta a social media Facebook whats app da sauran wajajen fira akan samu zaure wanda kawai aikin su shine  gulma! mun samu wani lokaci da wuya kasamu mutum biyu zuwa uku sun zauna suna fira har su tashi basuyi gulman dan uwa musulmi ba, 'yan uwa abinfa yayi kāmāri da yawa sai dai mu nemi tsarin Allah daga wannan musifa ta Gulma_
.
_Cin naman 'yar uwarki shine ki ambaci wani al'amari nata wanda idan dai har tana nan kika ambaci wannan kalmar zataji haushi, wannan shine ma'anar gulma wato ma'nar gulma itace kaine zaka fadi wata magana akan dan uwanka idan har yana wajen kayi wannan maganar tofa zaiji haushi, wato idan kayi magana a bayan idon dan uwan ka wato bazai lamunce ba bazai yarda ba, gashi halin nata ne kika ambata amma dai idan har tana wajen ranta bazaiji dadi ba wannan fa shine ma'ana gulma,  'yan uwa saboda Illar Gulma Allah madaukaki bai barwa Annabi Saw ragamar haramta Gulma ba, shima da kansa sai da ya haramta mana yin gulma, Lā haula walā Quwwata Illā Billāh  'yan uwa mune fa muke karanta Alqur'ani mu mune Al'ummar Annabi Muhammad saw kuma ayar da Allah ya haramta gulmar 'yan uwa dani dake da ku masu karatu wallahi muna karanta wannan ayar, amma gaba daya bamuyin aiki da ita,_
.
_Gashi kuma sanin kanmu ne cewa dukkan inda muka samu umarni acikin alqur'ani to yin aiki da wannan umarnin wajibi ne, haka kuma dukkan inda muka samu wani hani acikin Alqurani tofah wannan hanin dole ne mu hanu matukar muna son mu samu rabo a ranar qiyamah, zamu dauki aya guda daya acikin Alqur'ani da Allah ya haramta gulma, daga nan sai mu dauki wasu takaitattun hadīsai da sukayi magana akan gulma,! Allah ta'ala ya shiryar damu,_
.
 _Zamu dakata anan sai mun hadu a darasi na gaba_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp ‬


Share:

Illolin gulma

```★★★ILLOLIN GULMA★★★```
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
*Zauren SA'ADATUL-MUSLIM*
.
*‫بسم الله الرحمن الرحيم‬ ‫الحمد الله رب العالمين و لا عدوان إلا على الظالمين و الصلاة و السلام على سيدنا محمد سيد المرسلين و إمام المتقين‬ ‫و على آله و صحبه أجمعين أما بعد يا إخوان ا Iلكرام السلام عليكم ورحمة الله وبركاته*
.
_'Yan uwa wannan wata lecture ce da zauren Sa'adatul-Muslim ta shirya maku domin tunatar da 'yan uwa maza da mata akan illoli da kuma musiibar da take tattare da gulma, wato cin naman 'yan uwa wanda muna fatan Allah ta'ala ya taimake mu, kuma ya bamu ikon fadar maku tsanysar gaskiya_
.
_'Yan uwa inaso ku sani lallai fa Gulma tana daya daga cikin manya-manyan zunubai wadanda suka zama ruwan dare game duniya,  wallahi acikin wannan Al'ummar mun dauki wadansu miyagul laifuka wadanda aikatasu musiba ne a garemu wanda har muke ganin ba komai bane a wannan zamanin namu, to lallai fa 'yan uwa kusani Gulma tana daya daga cikin laifuka wadanda muke aikatasu a yau, wadanda basuyin gulma acikin wannan Al'ummar nan 'yan kadan ne, muna neman tsarin Allah daga fadawa cikin masu irin wannan hali,_
.
_Jama'a wallahi tallahi yanda gulma ta yawaita acikin wannan Al'ummar kai yanda mutane suke mu'amala da Gulma a wannan zamanin namu wallahi kai kace hujja ce muka samu daga ayar Alqur'āni ko kuma hadisin Annabi saw, alhali kuwa Allah ta'ala ya haramta gulma acikin littafin sa,_
.
_Zamu dakata anan sai mun hadu a darasi na gaba_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp ‬


Share:

Baiwa 11 Da Allah Ya Yi Wa Sheik Ja'afar Yayin Rasuwarsa

Daga Rabi'u Maiwaya Limawa
1.  SHAHADA: Ya yi Shahada iri daya da ta Sayyidina Umar (R.A)
2. Ya rasu ranar Juma'a: Rasuwar Ranar Juma'a alama ce da ake kyautata wa Mutum zato ya samu dacewa.
3. Mahaddacin Alkur'ani ne: Ana kyautata zaton duk wanda ya haddace Alkur'ani Mai Girma ya kuma kiyaye shi ya yada shi. Zai samu rabauta ranar Lahira.
4. Kisan Gilla: Duk Muminin da aka yi wa kisan gilla ana sa ran laifukan sa sun rataya a wuyan wanda ya kashe shi.
5. Ya cika da kalmar SHAHADA: Kafin rasuwar sa an ji shi ya na maimaita kalmar La ila ha illallah Muhammadur Rasulullah
6. Dandazon Mutanen da suka halarci jana'izarsa: Ana kyautata zaton duk mamacin da mutane 40 suka halarci jana'izarsa wadanda ba sa shirka zai samu dacewa.
7. Ya rasu ya na Sallar Asuba. Sallar Asuba na daya daga cikin Sallah mai madaukakiyar daraja.
8. Limami ne shi: Jagorancin Sallah wata babbar baiwa ce da ke kusanta Bawa zuwa ga Allah.
9. Ya Karanta Suratul MA'ARIJ: Kafin a kai ga kashe shi ya karanta sura daga cikin Alkur'ani Mai Girma.
10. Ya Dago Daga SUJADA: Sai bayan da ya dago daga sujada sannan makisan sa suka fara harbin sa.
11.Ya Nemi Gafarar Mutane Kafin Rayuwar sa. (Duk wanda na yi wa ba daidai ba don Allah ya yafe min).
Ya Allah Ka amshi shahadar Malam Mu kuma Allah Ya azurta mu da yin shahada.
Share:

Miyasa idan an dauko gawa zakaga mutane nakan hanya suna tashi tsaye ??

```Assalamu alaikum
Malam tambayana shin wai meyasa in an taho da gawa zakaga mutane nakan hanya suna tashi tsaye```



_*AMSA:*_
*******

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،



ﻋَﻦْ ﻋَﺎﻣِﺮِ ﺑْﻦِ ﺭَﺑِﻴﻌَﺔَ ﻗَﺎﻝَ: ﻗَﺎﻝَ ﺭَﺳُﻮﻝُ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺻَﻠَّﻰ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻭَﺳَﻠَّﻢَ: ﺇِﺫَﺍ ﺭَﺃَﻳْﺘُﻢْ ﺍﻟْﺠَﻨَﺎﺯَﺓَ ﻓَﻘُﻮﻣُﻮﺍ ﻟَﻬَﺎ ﺣَﺘَّﻰ ﺗُﺨَﻠِّﻔَﻜُﻢْ ﺃَﻭْ ﺗُﻮﺿَﻊَ.
```(ﺭﻭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ،  958‏)```

_An karbo daga *Aamir Ibn Rabee'ah* yace: *Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam)* yace; Idan kunga Janaza (Gawa ana Wucewa da ita) Ku tashi tsaye gareta har sai ta shige gabanku ko an sanyata (a kabari)._
_*(Muslim, 958)*_


ﻋَﻦْ ﺍﺑْﻦِ ﺃَﺑِﻲ ﻟَﻴْﻠَﻰ: ﺃَﻥَّ ﻗَﻴْﺲَ ﺑْﻦَ ﺳَﻌْﺪٍ ﻭَﺳَﻬْﻞَ ﺑْﻦَ ﺣُﻨَﻴْﻒٍ ﻛَﺎﻧَﺎ ﺑِﺎﻟْﻘَﺎﺩِﺳِﻴَّﺔِ، ﻓَﻤَﺮَّﺕْ ﺑِﻬِﻤَﺎ ﺟَﻨَﺎﺯَﺓٌ ﻓَﻘَﺎﻣَﺎ، ﻓَﻘِﻴﻞَ ﻟَﻬُﻤَﺎ: ﺇِﻧَّﻬَﺎ ﻣِﻦْ ﺃَﻫْﻞِ ﺍﻟْﺄَﺭْﺽِ، ﻓَﻘَﺎﻟَﺎ: ‏(ﺇِﻥَّ ﺭَﺳُﻮﻝَ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺻَﻠَّﻰ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻭَﺳَﻠَّﻢَ ﻣَﺮَّﺕْ ﺑِﻪِ ﺟَﻨَﺎﺯَﺓٌ ﻓَﻘَﺎﻡَ، ﻓَﻘِﻴﻞَ: ﺇِﻧَّﻪُ ﻳَﻬُﻮﺩِﻱٌّ؟ ﻓَﻘَﺎﻝَ: ﺃَﻟَﻴْﺴَﺖْ ﻧَﻔْﺴًﺎ)
```ﺭﻭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ ‏(960)```

_An karbo Daga Inn Abi Lailah cewa: Lalle Qais ibn Sa'd da Sahla ibn Hunaifi sun kasance (suna Zaune) a Qaadisiyyah, sai aka wuce da gawa a gabansu, sai suka miqe tsaye, sai wasu sukace musu: "Cewa ita (wannan gawar) ta mutanen kasa ne (kafuran garin)" sai sukace *"(Lalle Manzon Allah sallallahu alaihi Wa sallam, an wuce da gawa saiya tashi tsaye, wasu sukace: Shin shi (gawar) ba bayahude bane??? Sai (Manzon Allah) yace: Toh shi ba rai bane??)*._
_*(Muslim, 960)*_

An so ga mutum idan aka wuce da gawa, ya tashi tsaye gareta, domin Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) yayi Umarni da haka, kuma ya aikata, sannan ya bari (ya daina tashi tsaye). Aikata tashin da kuma rashin tashi, rashin tashin domin ya bayyana cewa tsayuwar ba wajibi bace.

_*(Majmu'ul Fataawa Wa Rasaa'il na Ibn Uthaymeen, 17/112)*_




والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_
Share:

Shin watanni nawa miji zai'iya kauracewa matarsa ??

*SHIN WATANNI NAWA MIJI ZAI IYA KAURACEWA MATARSA TA SUNNA ?*

*Tambaya:*

Assalamu alaikum Tambaya  ita ce؛ shin Tsawon wani lokaci ne ya halatta miji ya kaurace wa matar shi ta sunna kuma wani Mataki ya dace ta dauka in har ya wuce period din da sharia ta halatta?.

*Amsa:*

Wa'alaykumussalam, Ya halatta ya kaurace mata tsawon watanni hudu kamar yadda Allah ya fadi a suratul Bakara aya ta: 226.

Bai halatta ya wuce hakan ba, in ya koma da kansa ya cigaba da saduwa da ita to Allah mai gafara ne game da abin da ya wuce, in har ba zai koma ba bayan watanni hudu sai ya sake ta kamar yadda aya ta 227 a cikin surar ta nuna hakan.                        

In ya ki komawa ya sadu da ita kuma ya ki saki sai taje wurin Alkali don ya bashi zabi tunda wata hudu ya cika ko ya dawo mata ko kuma ya sake.                          

Allah ne mafi Sani

✍🏼 *Amsawa:*

*_Dr Jamilu Yusuf Zarewa_*
10/02/2017

Daga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*


Share:

Friday 29 September 2017

Makarin Matsananciyar Sha’awa ...

*Makarin Matsananciyar Sha’awa ...*

☏+2348037538596

Assalamu alaikum wa rahmatullah, barkanmu da sake haduwa cikin wannan fili, da fatan Allah Ya amfanar da mu dukkan bayanan da zasu zo cikinsa, amin.

 *hanyoyin da matasa za su bi don magance matsalar matsananciyar sha’awa.*

 Dafatan Allah Ya sa wannan bayani ya isa ga duk masu bukatarsa kuma ya amfanar dasu, amin.

Lakanin karya dafin matsananciyar sha’awa
Hanyatar matashi zai bi don dakushe kaifin matsananciyar sha’awa:

 Yana da matukar alfanu ga matashi mai fama da matsananciyar sha’awa ya kasance koda yaushe akwai wani al’amari da ya sa a gabanshi ya ke aiwatarwa, ya tarkato aikin da bai son yi ko wanda yake ganin ya fi karfinsa ya yi ta yi, in kwakwalwarsa ta kasance
koda yaushe akwai abinda ke gabanta, a hankali za ta kone
kuzarin shaukinta har ya kasance babu kuzarin jin
motsuwar sha’awa kuma.

 *Matashi ya kiyayi zama haka nan ba ya yin komai*

 domin a irin wannan lokacin ne shedan kan lallabo ya tsirar da tunanin sha’awa cikin zuciya, in ko matashi na aiwatar da wani aiki kusan koda yaushe, to ko shedan ya tsirar masa da tunanin sha’awa, to wannan tunanin ba zai yi tasiri ba. Ko kallo ne matashi zai yi, to ya fi masa alheri ya kalli abubuwan karuwar ilimi, ba fina-finan labaran soyayya ba, ko na kide-kide da wake-wake, domin wadannan duk wasu abubuwan ne ma su hassasa ruruwar wutar sha’awa cikin jiki.


Yawan karfi da tsanantuwar sha’awa na iya zama alheri mara iyaka ga mai fama da su in dai ya gano dabarar da zai sarrafa su su haifar da alheri ga rayuwarsa maimakon su yi ta motsowa kodayaushe ba bisa ka’ida ba.

Kamar yadda na taba fada a wannan fili, sha’awa ba komai ce illa daya daga cikin shau’ukan dan’adam, kuma duk wani shauki na dan’adam na bukatar kuzari lokacin motsawarsa cikin jiki da zuciya. Sha’awa ta kasance ta fi kowane kuzari karfi a dalilin tana amfani da duka kalar kuzari ukun nan na jikin dan’adam, watau kuzarin aikin karfi, kuzarin ma’aikatar hankali, da kuzarin shau’uka a duk lokacin motsuwarta.

 Binciken masana kimiyya ya tabbatar dukkannin manyan mutane da suka shahara suka yi suna a duniya ta wani fanni, irin su manyan masana kimiyya, kirkira, masana hikimomi, manyan masu mulki, Allah SWT Ya wadatu su da yawan karfin sha’awa da yawan tsanantuwarta, amma sai basu biye ma son zuciyarsu sun konar da wannan dimbin kuzarin a banza ba wajen dulmiya cikin tunane-tunanen alfasha da neman mata, sai dai suka runka karkatar da wannan dimbin kuzarin sha’awarsu wajen aiwatar da muhimman abubuwa wadanda suka kawo ci gaba a rayuwar dan’adam a dalilin haka su kuma suka yi suna duniya ta sansu, ya kasance ana ambaton su har bayan ransu.

Don haka matashi ko magidanci mai tsananin
sha’awa ya kamata ya tashi ya mike kuma ya dage, ya juyar da wannan dimbin zinariyar sha’awar da Allah SWT ya azurta shi da ita zuwa ga wani abin da zai zama abin alfaharin gareshi da duk wani nashi.

Mu yi dubi zuwa ga manyan mutanen da suka yi suna da karfin su ba da karfin wasu ba, ko karfin zalunci, inda sun biye ma sha’awar su da
son zuciyarsu, lallai da basu kai ga wannan matsayi ba.

 Ba kuzarin da ya kai kuzarin sha’awa karfi, don haka in ya yi yawa ko in ba a bukatar shi wajen ibadar aure, ana iya juyar da shi a cimma wani tsayayyen buri na rayuwa, maimakon a yi barnarsa wajen bin mata ko a yi asararsa haka nan a
banza. Da fatan Allah Ya bada ikon dagewa, amin.

Duk lokacin da sha’awa ta motso ma mai fama da
matsananciyar sha’awa, to ya san yadda zai yi ya karkatar Da tunanin shi daga wannan sha’awar zuwa wani abin daban.

Misali,  duk lokacin da igiyar tunanin sha’awa ta bijirowa matashi, sai ya yi sauri ya tsinke ta, ta hanyar saka wani tunanin daban cikin zuciyarsa wanda bai da nasaba da sha’awa, misali,  sai mutum ya yi ma kansa wani abun da zai sa dole ma’aikatar hankalin sa ta sakki wancan tunanin ta koma ga abin da ke faruwa a jikin sa a wannan lokacin, misali, mutum na iya sanya robali (rubber band) a
hannunsa, sai ya ja shi da karfi ta yadda zata tsalle shi ya ji zafi sosai, ko ya ciji hannunsa, ko dan yatsan sa cizo mai zafi a duk lokacin da irin tunanin nan ya bijiro masa, dole kwakwalwa nan take ta yanke ta bar wancan tunani ta koma ga na jin zafi, domin kwakwalwar dai guda daya ce, zai yi wuya ta saurari abubuwa biyu masu karfi a lokaci daya!




Share:

Mu nisanci tsinuwa da la'antar yan'uwannmu

MU NISANCI TSINUWA DA LA'ANTAR YAN UWANMU

*Darasi na farko-1*


Abinda ake nufi da la'anta ko tsinuwa shine:-
*"Addua da fatan Allah ya nisantar da mutum daga rahamarsa,da fatan halaka da masifa a gareshi tare da fatan fishin Allah ya tabbata a gareshi"*.

Duk lokacin da ka ce Allah ka la'anci kaza ko wane,ko Allah ka tsinewa wane albarka,kana nufin Allah ya nisantar da shiga daga Rahamarsa ya kuma tabbatar da shi acikin Halaka da mafisa tare da haramta masa rahaam.

Wannan yasa Manzon Allah s.a.w yake gargadin mu da munisanci la'anta da yin tsinuwa ga yan uwanmu da dukkan sauran halittun Allah baki daya.

*DAGA CIKIN ILLOLIN LA'ANTA DA TSINUWA*

Manzon Allah s.a.w ya fadi illa da la'anta da tsinuwa suke janyowa mutum,ga kadan daga cikinsu;-

1-ILLA TA FARKO
*"La'antar abu da tsine masa,kamar kisan sane*

Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yana cewa;
*(.......Kuma dukkan wanda yake La'antar mai Imani,kamar kisansane)*.
@صحيح الإمام البخاري - ٥٧٠٠ ،صحيح الإمام مسلم -

Ma'anar kamar kisansane shine;
"La'antarsa kamar yana yi masa adduane da halaka da tabewa".
@فتح الباري - ١٠/٤٨٢ ) ].


2-ILLA TA BIYU
*"Mai yawan La'anta baya zama daga cikin masu bada Shaida da kuma masu ceto a gobe alqiyma*.

Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yana cewa;
*(Lallai masu yawan la'anta da tsinuwa,basu cikin masu bada shaida kuma basu cikin masu yin ceto a gobe alqiyama)*
@صحيح الإمام مسلم - ٥٧٠٠

3-ILLA TA UKKU
*Yawan la'anta da tsinuwa yana cikin abubuwan da suke saurin kai mutum shiga wuta*.

Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yana cewa;
*(Yaa ku taron mata, Lallai ku yawaita yin Sadaka domin naga mafi yawa daga cikin ku acikin wuta)*,"sai suka tambaye shi saboda me,sai yace;
*(Saboda kuna yawan la'anta da tsinuwa kuma kuma kafircewa mazajen auranku....)*
@صحيح الإمام البخاري - ٣٠٤ ، وأخرجه الإمام مسلم في صحيحه بنحوه من حديث ابن عمر رضي الله عنهما - ٨٠ ].

4-ILLA TA HUDU
*La'anta da tsinuwa laifine babba daga cikin manyan zunubai*

Daga Salmatu bnul Akwa'i رضي الله عنه yana cewa;
*"Mu sahabbai mun kasance idan muka ga mutum yana la'antar dan uwansa to muna ganinsa ya bude wata kofa daga cikin kofofin manyan zunubai"*
@المعجم الأوسط - 6849 ، وإسناده جيد.
5-ILLA TA BIYAR
*La'anta da tsinuwa haramunne*.

Imam Nawawy Allah yayi masa Rahama yana cewa;
*"Malamai sun hadu akan la'anta da tsinuwa haramunne"*.
@شرحه على مسلم - ١/٢٥٠
6-ILLA TA SHIDA
*Yawan la'anta baya cikin siffar mai Imani*

Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yana cewa;
*(Mai Imani baya sukar dan uwansa kuma baya la'anta da tsinewa dan uwansa,kuma mai Imani baya alfasha kuma baya mugunta)*
@ﺭﻭﺍﻩ ﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ ﻋﻦ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﻦ ﻣﺴﻌﻮﺩ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ ــ ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﺒﺮ ﻭﺍﻟﺼﻠﺔ ﺑﺮﻗﻢ 1900 ‏( ﺻﺤﻴﺢ ‏)ﺍﻧﻈﺮ ﺣﺪﻳﺚ ﺭﻗﻢ : 5381 ﻓﻲ ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ

7-ILLA TA BAKWAI
*Mai la'anta da tsinuwa bai kiyeye wasiyyar Manzon Allah ba*.

Daga Sahabi Jurmuzal Hajimy R.A yana cewa,nace Ya Manzon Allah kayi min Wasiyya,sai yace;
*(Ina yi maka wasiyyar kada kazama mai La'anta)*
@ﺭﻭﺍﻩ ﺃﺣﻤﺪ ــ ﻣﺴﻨﺪ ﺍﻟﺒﺼﺮﻳﻴﻦ ﺑﺮﻗﻢ 19757 ‏ ﺻﺤﻴﺢ ‏) ﺍﻧﻈﺮ ﺣﺪﻳﺚ ﺭﻗﻢ : 2542 ﻓﻲ ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ

Allah ne mafi sani.


Mu hadu a Darasi na gaba insha Allah.


Share:

Ziyarar da shaitan yakaima Annabi Nuhu (AS)

ZIYARAR DA SHAITAN YAKAI MA ANNABI NOUHU (AS).

Abul Faraj Ibnul Jawzee ya ruwaito tare da isnadinsa daga Abdullahi 'dan Umar 'dan Khattab (ra) yana cewa:

Alokacin da Annabi Nouhu (as) ya hau Jirginsa, sai yaga wani tsoho wanda bai san dashi ba. (Ashe Iblis ne La'ananne). Sai Annabi Nouhu (as) yace masa: "MENENE YA SHIGO DAKAI?".

Sai yace : "Na shigo ne domin in kama Zukatan Mutanenka. Har ya zama zukatansu suna tare dani, Jikkunansu kuma suna wajenka".

Sai Annabi Nouhu (as) yace masa "FITA, YA KAI MAQIYIN ALLAH!!!".

Sai yace: "Abubuwa guda biyar dasu nake hallakar da mutane. Zan baka labarin guda uku daga ciki, amma ba zan gaya maka sauran biyun ba".

Nan take sai Allah (SWT) yayi wahayi zuwa ga Annabi Nouhu (as) cewa: "BAKA DA BUKATAR JIN WADANNAN GUDA UKUN, GARA KA UMURCESHI YA GAYA MAKA GUDA BIYUN".

Da ya gaya masa hakan sai La'anannen yace : "(abubuwan nan guda biyu) dasu ne nake saurin hallakar da mutane, sune : HASSADA DA KUMA KWADAYI".

"Ita hassada ta dalilinta ne aka Tsine mun albarka, kuma aka mayar dani na zama Shaitani abin korewa daga rahamar Allah".

"Shi kuma KWADAYI, ta dalilinsa ne na samu biyan bukata-ta akan Annabi Aadamu (as) duk da cewa an halatta masa Aljannah baki dayanta. (Amma kwadayi yajashi zuwa ga cin bishiyar nan guda daya rak wacce aka hanashi yaci)".

ZAUREN FIQHU : 'Yan uwa mu guji wadannan Miyagun halaye guda biyu. Wallahi duk wanda yake aikata wadannan halayen sai ya Qaskanta awajen Allah da bayinsa.

Mafiya yawan husumar dake faruwa acikin gidajenmu da Unguwanninmu, HASSADA ce asalinsu.

Mafiya yawan laifukan da suka fi lalata al'ummah, kwadayi ne asalinsu. Kamar irin su Zina, Sata, Luwadi, madigo, Zamba, Ha'inci, Cin hanci, Zalunci, etc.

Allah shi kiyayemu don Qarfin ikonsa.

Wannan Nasiha tana zuwa ne daga ZAUREN FIQHU WHATSAPP - 1 (22-09-2015).

Kayi sharing zuwa ga Contacts dinka amma DON ALLAH kada ka chanza koda harafi guda daga wannan Sakon. Masu cin amanar Ilimi kuji tsoron Allah ku dena.


Share:

Thursday 28 September 2017

Shin wajibi ne azumin Ashura!?? Saadatul muslim

```SHIN WAJIBI NE AZUMIN ĀSHURA? !```
...........................................
*Zauren SA'ADATUL-MUSLIM*
.
_Da sunan Allah mai rahama mai jin kai, Lallai azumtar ranar Ashura ba wajibi bane 'yan uwana sai dai wannan azumi ne wanda Annabi saw ya azumce shi kuma ya kwadaitar cewa a azumci wannan rana wato goma ga watan Al-muharram wanda yayi dai dai da ranar asabar mai zuwa in Shaa Allah, Annabi saw ya kwadaitar da ayi azumi a wannan rana ta Ashura wanda 'yan sha-biyu suke barnatar da jinainan su wajen saba ma Allah da kuma wahalar da kai, Imam Malik acikin Muwadda shafi na 163 karkashin Littafin Azumi hadisi na 824 yace Lallai labari yazo masa cewa lallai babban sahabin Annabi Umar dan Khaddab ya aika wajen Harith dan Hisham cewa lallai fa gobe itace ranar Ashura, don haka kayi azumi kuma ka umarci iyalanka cewa suyi azumi" 4 don haka wannan Sunnah ce amma fa mai karfi zamu ambaci hadisai guda biyu Akan haka in Allah ya yarda_
.
_Azumin a ranar Ashura Sunnah ce mai karfi Imam Bukhari ya ruwaito ingantaccen hadisi daga Ummuna Aisha Allah ya kara mata yarda tace, ranar Ashura ta kasance rana ce da Quraishawa suka kasance Suna azumtar wannan rana tun lokacin jahiliyyah, shi kuma Manzon Allah saw ya kasance yana azumtar wannan rana tun a jahiliyyah, lokacin da Annabi saw yazo garin Madinah sai yaci gaba da azumtar wannan rana kuma yayi umarni da cewa a azumce ta amma a lokacin da aka wajabta Ramadan sai ya kasance Ramadan shine Azumin da aka wajabta sai akabar azumtar Ashura ya zama Sunnah, duk wanda yaso ya azumci wannan rana ta Ashura wanda kuma yaso ya barta" (Bukhari 2002 Muslim 1125)_
.
_Hadisi ya inganta daga Abdirrahman dan Auwf Allah ya kara masa yarda yace lallai shi yaji Mu'awiyah bin Abi-sufyan a ranar Ashura a shekarar aikin hajji a lokacin shi yana Akan mimbari yana cewa "Yaku 'yan garin Madinah Ina malaman ku suke? naji Manzon Allah saw yana magana dangane da ranar Ashura cewa the" Wannan itace ranar Ashura kuma Allah bai wajabta maku Azumtar sa ba amma fa kusani ni Ina Azumi ga duk wanda yaso daga cikin ku to yayi Azumi, wanda kuma yaso daga cikin ku to yasha abin shansa, ma'ana yaci gaba da cin abincin sa" (Bukhari 2003 Muslim 1169)_
.
_Don haka dai 'yan uwa Sunnah ce kuma ku tunatar da' yan uwanku dangane da wannan Azumi na ranar goma ga watan Al-muharram domin su azumce shi kuma ayi don Allah domin neman yardan sa, Allah yasa mudace_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp


Share:

Ashura da tasu'a - Sa'adatul-muslim

```ASHURA DA TASU'A```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
*Zauren SA'ADATUL-MUSLIM*
.
_Da sunan Allah mai rahama mai jinkai, ranar Ashura itace ranar 10 ga watan Al-Muharram wato watan farko na sabuwar shekarar Musulunci wanda ya inganta daga Annabi Saw cewa ya azumci wannan ranar kamar yadda bayanin ya gabata, to ita kuma Tasu'a fa?   Ranar Tasu'a itace ranar 9 ga watan Al-Muharram wacce Annabi yayi nufin azumtar wannan ranar Amma Allah madaukaki bai kai Annabi Saw wannan lokaci ba, dalili kuwa hadisin Ibn Abbas wanda yake cewa "A lokacin da Annabi Saw yayi azumin Ashura kuma yayi umarni da cewa a azumci wannan ranar, sai mukace ya Manzon Allah lallai wannan rana ce wacce yahudawa da Nasara suke girmama ta, sai Annabi Saw yace, idan har shekara ta zagayo da yardan Allah zan azumci ranar 9 ga wata, (wato 9 ga watan Al-Muharram sannan ya azumci 10 ga watan)  Ibn Abbas yace Allah madaukaki bai kaddari Annabi Saw yakai shekarar ba, sai mutuwa tazo ma Annabi Saw"  Muslim da Abu-Dawuda ne suka ruwaito wannan hadisin, duba littafin Fiqhul-Muyassir na Sa'ad Yusuf shafi na 177,_
.
_'Yan uwa kunji inda azumtar 9 ga wannan wata na Al-Muharram ya samo asali wato ka azumci 9 da 10 ga wannan watan shi akafi so, amma ga wanda bashi da karfin yin azumi guda biyu a jere shi ko ita guda daya 1 rak kawai zata iya yi to tayi kokari tayi na 10 ga watan kada tace zatayi 9 tabar na 10 aa kawai mutum matukar shi guda 1 kawai zaiyi to yayi 10 ga watan wato Ashura shi yafi, sabanin 'yan sha-biyu da suke wasa da makami suna illata jikin su wannan ba koyarwar Musulunci bane da kuma Nawasib masu yin cika-ciki shima wannan babu shi a Musulunci abinda ya inganta shine yin wannan azumi guda biyu wato 9 da 10 ga wannan watan na Al-Muharram, wanda kuma a yanzu da nake wannan rubutun da safe yau Laraba wato Wednesday 7 ga watan Al-Muharram shekara ta 1439 wanda azumin Tasu'a zai kama ranar Juma'a shi kuma Ashura ranar Asabar, Allah ya bamu ikon yin Azumin don Allah, Allah yasa mudace_
.
*Hussaini Ibnu Taimiyyah Kuriga*
.
→ A yanzu haka zaku iya bibiyar zauren SA'ADATUL MUSLIM ta shafin sada zumunta dake Facebook ta cikin wannan link din
https://free.facebook.com/Saadatul-Muslim-Islamic-Group-Chat-1017855871594468/?ref=opera_speed_dial_freefb
.
→ Ga masu sha'awar shiga zauren SA'ADATUL MUSLIM sai su aiko da cikakken Suna da adreshi izuwa ga numbar mu +2348052975857 ta whatsapp


Share:

YAUSHE NE AZUMIN ASHURA DA TASU'A 1439/2017???!!!

*YAUSHE NE AZUMIN ASHURA DA TASU'A 1439/2017???!!!*

Assalamu alaikum, Duba da yanda ake yawan tambaya dangane da yaushe ne ranar azumin Ashura da Tasu'a na wannan shekara, ya sanya muka ga ya dace mu sanar da mutane cewa a bisa Sanarwa da masana wannan fanni suka yi kuma mai Alfarma Sarkin Musulmi ya sanar shi ne: Ashura da Tasu'a za su kasance ce ne ranar Asabar da Lahadi wato 30/09/2017 da 01/10/2017, in sha Allahu Ta'ala.

Kuma kamar yadda aka sani sunna ce ta Ma'aiki, sallallahu 'alaihi wa sallama, azumtar wannan rana.

Allah Ta'ala Ya sa mu dace.

✍🏼Dan uwanku a Musulunci:
*_Umar Shehu Zaria_*
27/09/2017.

Daga: *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*
Share:

(Mp3)Munafurci dodo (02) - Sheikh Muhammad adam albani zaria

MUNAFURCI DODO (02)

Tare da:
Sheikh Muhammad auwal adam albani zari

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.


Ayi saurare lafiya
Share:

Sahabbai manyan bayin Allah

*SAHABBAI MANYAN BAYIN ALLAH*

✍🏼 Rubutawa:
*_Malam Misbahu Saminu Madabo_*
26/09/2017.

Sune Qur'aani yake sauka ga Manzon Allah(saw) suna tare dashi.

 Idan basu fahimci hukunci ba,su tambaye shi ya basu amsa.

Idan Allah zai magana dasu ko magana akan su,sai yace dasu:

"ياايها الذين ءامنوا".

Suna zama da Annabi(saw) suci  Abinci,su sha abin sha tare,su Aura su kuma Aurar masa,suka kuma je dukkan Yaqi tare dashi,yana jagorantar su a Sallah da sauran ayyuka.

Kawai kai saboda kasa baqaqen kaya kana yawon banza a tituna,ko cikakkiyar magana ta minti 3 ba zaka iya ba da harshen Qur'aani(Larabci),sai iskanci da Mata da sunan Mut'ah.

Amma a hakan Shaidan yayi maka Khudubar wai kafi wa'yancan Imani da tsoron Allah,har ma kana Zagin su kana tsine musu.

Ke kuma qazama,kina wari saboda bin tituna ba wanka,amma a haka kike ganin wai kinfi Matan Manzon Allah(saw) da Matan Sahabbai(ra) imani da son Allah da Manzon sa(saw),saboda kawai Maza sun rarake ki da sunan Mut'ah.

Allah ka raba mu da shirme,iskanci da rashin mutunci da rashin hankali na Shi'a da 'yan Shi'a.

Allah ka kare mu ka kare imanin mu dana Zuriyar mu daga 6ata da ta6ewa!!!!!

Daga: *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*


Share:

Wednesday 27 September 2017

(Mp3)Munafurci dodo (01) - Sheikh Muhammad adam albani zaria

MUNAFURCHI DODO (01)

Tare da:
Sheikh Muhammad auwal adam albani zaria

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya
Share:

(Mp3)Lecture:Hukuncin mauludu - Sheikh Muhammad adam albani zaria

LECTURE LECTURE

HUKUNCIN MAULUDI

Tare da: Sheikh Muhammad adam albani zaria

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNA BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya
Share:

(Mp3)Lecture: Haba shehi - Sheikh Muhammad adam albani zaria

LECTURE LECTURE

HABA SHEHI

Tare da:
Sheikh Muhammad auwal adam albani zaria

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya
Share:

Tuesday 26 September 2017

(Mp3)Wa'azin minjibir - Sheikh kabiru Muhammad haruna gombe

WA'AZIN MINJIBIR

Tare da:
Sheikh kabiru Muhammad haruna gombe

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi sauraro lafiya
Share:

(Mp3)Ashura 11 - Sheikh Muhammad adam albani zaria

ASHURA 11

Tare da:
Sheikh Muhammad auwal adam albani zaria

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya
Share:

(Mp3)Ashura 10 - Sheikh Muhammad adam albani zaria

ASHURA 10

Tare da:
Sheikh Muhammad auwal adam albani zaria

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya
Share:

(Mp3)Ashura 09 - Sheikh Muhammad adam albani zaria

ASHURA 09

Tare da:
Sheikh Muhammad auwal albani zaria

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya
Share:

(Mp3)Ashura 08 - Sheikh Muhammad adam albani zaria

ASHURA 08

Tare da:
Sheikh Muhammad auwal afam albani zaria

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya
Share:

Monday 25 September 2017

Hukucin yin anko a musulunchi !! - Zauren fiqhus sunnah

*HUKUNCIN YIN ANKO A MUSULUNCI*

*Tambaya*
.
Assalamu Alaykum.
Dan Allah malam menene hukuncin anko da ake yi a biki.shin ya halatta.
.
*Amsa*
.
Anko al'ada ce ta mutane bata da alaqa da addini, saboda haka in dai ba wata barna ta bayya a cikinsa ba babu laifi.
Shari'ar musulunci ta ba al'adun mutane mahimmanci da kula.
Abin da zai iya maida anko ya zama bai halasta ba kamar: mata sui shigar maza ko akasi, ko ya zama akwai bayyana tsaraici. , ko makamancin haka.
.
Allah ya fi sani.

*BIKIN SAUKAR AL-QURNI*
.
*Tambaya*

Assalamu Alaykum.
Dan Allah malam menene sharia tace akan bikin saukar Al-qur'aani? Sai kaga a yi taro harda bada allo.da dai sauransu
.
*Amsa*
.
Babu laifi ayi bikin saukar Qur'ani, domin abu ne na maslaha ita kuwa shari'a tana kula da maslaha a rayuwar mutane.
Wannan saukar na qarfafar wasu suma su dage su sauke ko haddace Qur'anin nan gaba.
Kwamitin bada fatawa na din-din -din na Qasar Saudia ya ce babu laifi in an aikata haka.

Allah ya fi sani.
*Amsawa : ✍*

*MAL. BASHEER LAWAL MUHAMMAD ZARIA.*



*Daga  ZAUREN FIQHUS SUNNAH*

Share:

(Mp3)Muhadara: daga jahar kibbi - Sheikh kabiru Muhammad haruna gombe

WA'AZIN JAHAR KIBBI

Tare da:
Sheikh kabiru Muhammad haruna gombe

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya
Share:

(Mp3)Ashura 07 - Sheikh Muhammad adam albani zaria

ASHURA 07

Tare da:
Sheikh Muhammad auwal adam albani zaria

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi sauraro lafiya
Share:

(Mp3)Ashura 06 - Sheikh Muhammad adam albani zaria

ASHURA 06

Tare da:
Sheikh Muhammad auwal adam albani zaria

DOKIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya
Share:

(Mp3)Ashura 05 - Sheikh Muhammad adam albani zaria

ASHURA 05

Tare da:
Sheikh Muhammad auwal adam albani zaria

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi sauraro lafiya

Note: Zaku iya sauko da sauran wannan ASHURA DIN ANAN
ASHURA COMPLETE


Share:

Sunday 24 September 2017

(Mp3)Ashura 04 - Sheikh Muhammad adam albani zaria

ASHURA 04

Tare da:
Sheikh Muhammad auwal adam albani zaria

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya

Note: Zaku iya sauko da  Sauran wannan waazin na Ashura anan.
ASHURA COMPLETE

Share:

(Mp3)Ashura 03 - Sheikh Muhammad adam albani zaria

ASHURA 03

Tare da:
Sheikh Muhammad auwal adam albani zari

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya

Note: Zaku iya sauko da sauran wannan waazin na Ashura anan

ASHURA COMPLETE
Share:

Saturday 23 September 2017

(Mp3)Ashura 02 - Sheikh Muhammad adam albani zaria

ASHURA 02

Tare da:

Sheikh Muhammad auwal adam albani zaria

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya
Share:

(Mp3)Ashura 01 - Sheikh Muhammad adam albani zaria

ASHURA 01

Tare da:

Sheikh Muhammad auwal adam albani zari

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU DANNA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA.

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya

SHIGA NAN:(Mp3)Ashura 02 - Sheikh Muhammad adam albani zaria
Share:

GA WASU HANYOYI GUDA SHIDA WADANDA ZAKA IYA BINSU DON GYARA HALAYENKA

GA WASU HANYOYI GUDA SHIDA WADANDA ZAKA IYA BINSU DON GYARA HALAYENKA :

1. Cikakken imani na gaskiya tare da yawaita neman kusanci da Allah ta hanyar aikata dukkan abinda zai janyo kusancinka dashi. Ta hanyar kwatanta yin haka ne zuciya take samun kaifi, Kuma mutum yake samun saukin suluki (tafiya) bisa hanyar neman yardar Ubangijinsa.

2. - Zama tare da kulla abota da mutanen kirki masu kyawawan halaye. Domin kuwa abokai suna taka muhimmiyar rawa acikin tarbiyyar abokansu ta fuskar Mu'amala da kuma zama yau da kullum.

Shi yasa malamai suka ce ''Shi aboki mai jan abokinsa ne. Idan shi na kirki ne zai jashi zuwa alkhairi. Idan kuma shi na banza ne, to zai ja abokinsa ne zuwa ga sharri.

Wani Malami ya fa'da acikin waqa : "Kar ka tambaya game da halin mutum, Kai dai ka tambayi su waye abokansa?. Domin kowanne aboki yana koyi ne da abokansa".

3. Hanya ta uku ita ce : Ka rika yiwa kanka hisabi domin ita zuciya bisa hakikanin gaskiya an halicceta ne bisa dabi'ar yin umurni da munanan abubuwa. Kuma ita zuciya kullum kokarinta shine ta jaka zuwa ga sharri.

Don haka ka rika tuhumar zuciyarka kana yi mata hisabi kuma kana janta zuwa ga alkhairi. Kar ka zama mai binta duk inda ta jaka kamar jela, tana janka zuwa ga bin son ranta.

Imam Busiriy yace "Ita zuciya kamar Jariri take. Domin shi jariri idan ka kyaleshi kaci gaba da shayar dashi, sai ya girma bai dena son shan nono ba. Amma idan ka yayeshi shikenan sai ya yayu".

4. Na hudu shine : Ka yawaita jarraba aiki da kyawawan halaye madaukaka irin su Hakuri, juriya, Tawadhu'u, kyauta, biyayya, gaskiya, amana, sakin fuska, etc.

Alokaci guda kuma ka rika kokarin kauce ma miyagun halaye irin su Qarya, girman kai, rowa, ha'inci, taurin kai, riko, gaaba, hassada, etc.

Shi yasa Manzon Allah (saww) yace : "SHI ILIMI ANA SAMUNSA NE DA NEMAN ILIMI. SHI KUMA HAKURI DA HAKURKURTAR DA RAI".

5. Hanya ta biyar ita ce: Ka rika karanta tarihin magabata na kwarai kana jin yadda sukayi rayuwarsu cikin neman yardar Allah da guje ma sa'ba masa.

Domin karanta tarihinsu wata babbar hanya ce muhimmiya ta gyaran halaye domin zaka ji labari daga manyan Maluma wanda acikinsa zaka ji yadda halayensu da ladubansu yake.

6. Hanya ta shida ita ce: ka rika rokon Allah cewa ya baka kyawawan halaye, kuma ya rabaka da miyagun halayen dake tare da kai.

Yin wannan yana daga cikin manyan hanyoyin da zasu kaika zuwa ga kyautatuwar halaye.

Daga cikin addu'o'in da Manzon Allah (saww) yake yi akwai wacce yake cewa:

"YA ALLAH KA SHIRYAR DANI ZUWA GA MAFI KYAWUN HALAYE. DOMIN BABU MAI SHIRYARWA ZUWA GA MAFI KYAWUNTA SAI DAI KAI.

"KUMA KA JUYAR DA MAFIYA MUNINTA DAGA GARENI. DOMIN BABU MAI JUYARWA DAGA MAFI MUNINTA SAI DAI KAI".

Ya Allah muna Tawassuli da mafi kyawun halaye da dabi'u acikin bayinka don alfarmarsa ka kyautata halayenmu. Ka kiyayemu daga miyagun halaye.

DAGA ZAUREN FIQHU (06-08-2016).


Share:

Archive

Unordered List

Support