Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday, 30 October 2018

HUKUNCIN KOYAN ILIMIN TAURARI !!! Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum Dr. dafatan anwuni lafiya, Allah yasa haka amin.
Akwai wani abu mai kama da ilimi kuma kamar tsafi ta wani fuskar. A turanche ana kiran sa Astrology, har akwai Makarantu da ake karantar da course din a Jami'a, kama daga degree, masters har P.hd, wasu kuma suna sana'a dashi a kasashen waje, ta bangaren bada shawarwari.
Abin ya dogara ne da sanin taurari, juyawar duniya, rabe raben ruhi da sauransu. Sun raba ruhin Dan Adam gida hudu, akwai; Ruwa, Kasa, Iska da kuma Wuta.
Ko wane ruhi yana tare da wasu taurari wadanda ake ganesu ta hanyar sanin ranar haihuwar mutum. Masu irin wadannan ilimin suna iya fadan halin mutum, kuma a mafi yawanchin lokuta yana zama daidai. Suna bada shawarwari gameda abinda mutum zaiyi, har suna fadawa mutum chewa lura da taurari ko makamanchin haka, yanada sa'a a wuri kaza, ko kuma bashida sa'a. Suna fadan chewa wane yanada taurarin nasara ko kuma wani abu mai kama da haka.
Ina bibiyar abin a mafi yawanchin lokuta, har nafara fahimtan  wasu abubuwa gameda hakan.
Minene matsayin sharia

*Amsa*

Wa alaikum assalam, To dan'uwa  yin irin wannan nau'i na ilimin taurari haramun ne yana kuma iya kaiwa zuwa ga shirka, saboda  Camfi ne da kuma da'awar sanin Gaibu, wanda Allah ya kebanta da shi.

Imamu Katadah yana  cewa: "Allah ya halicci taurari ne saboda abubuwa guda uku kawai:

*1.* Gane hanya, kamar yadda Allah ya fada a suratu Annahl aya ta(16)
وعلامات وبالنجم هم يهتدون

*2.* Ado ga saman duniya.
*3.* Jifan kangararrun Shaidanu masu sato Ji daga sama, Allah madaukakin sarki yana cewa a suratul mulki aya ta (5)
ولقد زينا السماء الدنيا بمصابيح وجعلناها رجوما للشياطين.

Yin amfani da Taurari wajan gane Nasara ko rashinta harka ce ta Bokaye, kuma Allah bai tanade su don yin hakan ba, yana kuma kaiwa zuwa hallaka.

Ya halatta ayi amfani da ilmin Taurari wajan gane Alkibla da kuma tabbatar da maslahohin addini.
Don neman karin bayani duba Alkaulu al-mufid 2/102 da kuma Al-mulakkas fi-sharhi kitabittauhid (236)
Allah ne mafi sani

*Amsawa

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*

17/10/2018

Share:

HUKUNCIN KOYAN ILIMIN TAURARI !!! Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum Dr. dafatan anwuni lafiya, Allah yasa haka amin.
Akwai wani abu mai kama da ilimi kuma kamar tsafi ta wani fuskar. A turanche ana kiran sa Astrology, har akwai Makarantu da ake karantar da course din a Jami'a, kama daga degree, masters har P.hd, wasu kuma suna sana'a dashi a kasashen waje, ta bangaren bada shawarwari.
Abin ya dogara ne da sanin taurari, juyawar duniya, rabe raben ruhi da sauransu. Sun raba ruhin Dan Adam gida hudu, akwai; Ruwa, Kasa, Iska da kuma Wuta.
Ko wane ruhi yana tare da wasu taurari wadanda ake ganesu ta hanyar sanin ranar haihuwar mutum. Masu irin wadannan ilimin suna iya fadan halin mutum, kuma a mafi yawanchin lokuta yana zama daidai. Suna bada shawarwari gameda abinda mutum zaiyi, har suna fadawa mutum chewa lura da taurari ko makamanchin haka, yanada sa'a a wuri kaza, ko kuma bashida sa'a. Suna fadan chewa wane yanada taurarin nasara ko kuma wani abu mai kama da haka.
Ina bibiyar abin a mafi yawanchin lokuta, har nafara fahimtan  wasu abubuwa gameda hakan.
Minene matsayin sharia

*Amsa*

Wa alaikum assalam, To dan'uwa  yin irin wannan nau'i na ilimin taurari haramun ne yana kuma iya kaiwa zuwa ga shirka, saboda  Camfi ne da kuma da'awar sanin Gaibu, wanda Allah ya kebanta da shi.

Imamu Katadah yana  cewa: "Allah ya halicci taurari ne saboda abubuwa guda uku kawai:

*1.* Gane hanya, kamar yadda Allah ya fada a suratu Annahl aya ta(16)
وعلامات وبالنجم هم يهتدون

*2.* Ado ga saman duniya.
*3.* Jifan kangararrun Shaidanu masu sato Ji daga sama, Allah madaukakin sarki yana cewa a suratul mulki aya ta (5)
ولقد زينا السماء الدنيا بمصابيح وجعلناها رجوما للشياطين.

Yin amfani da Taurari wajan gane Nasara ko rashinta harka ce ta Bokaye, kuma Allah bai tanade su don yin hakan ba, yana kuma kaiwa zuwa hallaka.

Ya halatta ayi amfani da ilmin Taurari wajan gane Alkibla da kuma tabbatar da maslahohin addini.
Don neman karin bayani duba Alkaulu al-mufid 2/102 da kuma Al-mulakkas fi-sharhi kitabittauhid (236)
Allah ne mafi sani

*Amsawa

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*

17/10/2018
Share:

Friday, 28 September 2018

Labarin Yajuju wa majooju - Zauren Fiqhu



LABARIN YAJUJU WA MAJOOJU


***********************************
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM

Tsira da aminci su tabbata bisa Mafi girman matsayi acikin dukkan halittun Allah, Shugabanmu Annabi Muhammadu Tare da iyalan gidansa tsarkaka da Sahbbansa zababbu.

Yau in sha Allahu muna tare da daliban ZAUREN FIQHU WHATSAPP (3) kuma zamu gudanar da darasinmu akan tarihin wasu Qabilu ne wadanda yanzu haka suna nan da ransu. Amma ba zasu bayyana ba, sai akarshen zamani. Sunansu YAJOOJU WA MAJOOJU.

Acikin Alqur'ani, Allah ya bamu labarin tafiye tafiyen da Sarki Dhul-Qarnaini yayi.

Acikin tafiye tafiyen nasa, yaje wajen da rana take faduwa, sannan yaje yaje mahudarta.

Sannan a tafiyarsa ta uku kuma yaje chan karshen duniya, kusa da bangon duniya.

Achan din ne mutanen wajen suka kawo masa Qara. Suka ce masa :

"YA KAI DHUL QARNAINI, HAKIKA YAJOOJU DA MAAJOOJU MASU 'BARNA NE ADORON QASA. SHIN KO ZAMU SANYA MAKA WANI HARAJI (WANDA ZAMU BAKA) DOMIN KA SANYA WATA KATANGA ATSAKANINMU DA TSAKANINSU?".

Shi kuma sai yace "ABINDA UBANGIJINA YA BANI, SHINE YAFI ALKHAIRI. KU DAI KAWAI KU TAIMAKENI DA QARFI (KARFIN JAMA'A)  ZAN SANYA WATA KATANGA MAI QARFI TSAKANINKU DA TSAKANINSU".

Daga nan Dhul-Qarnaini ya kama aiki, ya gina wata Katafariyar katanga ta Qarfe da dalma, wacce tafi Qarfin wadannan mutanen su haurata.

SHIN SU WANENE YAJOOJU WA MAJOOJU??

Bari mu leka cikin litattafan Tafseeri da hadisan Manzon Allah (saww) domin mu binciko labarinsu.

Al Imam Alqurtubiy (rah) daya daga cikin jerin Manyan Malaman tafseeri, yace "An samo hadisai da labarai dangane da fitowarsu da kuma siffofinsu. Kuma cewa suna daga cikin 'ya'yan YAFITHU ne.

Sayyiduna Abu Hurairah (rta) ya ruwaito daga Manzon Allah (saww) yana cewa:

"An haifa ma Annabi Nuhu ('ya'ya guda uku) SAAMU, da HAAMU, da YAFITHU.

Shi samu shine ya haifi Larabawa da Mutanen Farisa (Iran kenan) da kuma mutanen Ruum (turawa kenan). Kuma akwai alkhairi acikinsu.

Shi kuma YAFITHU shine ya haifi YAAJOOJ da MAJOOJU da Turkawa da mutanen Saqalib, amma babu alkhairi acikinsu.

Shi kuma HAAMU shine ya haifi Qibtawa (mutanen Misra) Da Barbar (berbers, wasu mutanen daji ne, masu tsananin Yaki) da kuma Bakaken fata".

Abu Sa'eed Alkhudriy (ra) ya riluwaito daga Manzon Allah (saww) yana cewa:

"(Su Yajooju wa Majooju) Mutum guda daga cikinsu ba zai mutu ba, har sai bayan ya haifi 'Ya'ya Maza guda dubu daga cikin tsatsonsa.

Imamul Qushairiy ya ambato Abu Sa'eed Alkhudriy yana cewa "SU QABILU ASHIRIN DA BIYAR NE ABAYAN SU YAJUJU WA MAJUJU. MUTUM GUDA DAGA CIKINSU DA KUMA CIKIN YAJOOJU WA MAJOOJU BA ZAI MUTU BA, HAR SAI NAMIJI GUDA DUBU SUN FITA DAGA CIKIN TSATSONSA.

Lallai bisa ga wadannan hadisan zamu iya cewa indai kowanne mutum guda daga cikinsu yana haifar mutum dubu, to lallai ba Qaramin yawa ne dasu ba.

Abdullahi bn Mas'ud (ra) yace: "Na tambayi Manzon Allah (saww) dangane da Yajooju wa Majooju, Sai shi Mai tsira da aminci) yake cewa :

"SU YAJUJU WA MAJOOJU AL'UMMATAI NE GUDA BIYU. (WATO YAJOOJU DABAN, MAJOOJU MA DABAN).

Kowacce Al'ummah daga cikinsu tana Qunshe da wasu Al'ummatai (ko Qabilu) guda dubu dari hudu (400,000 tribes). Kuma kowacce al-ummah babu wanda yasan iyakar yawansu sai dai Allah".

"KUMA MUTUM GUDA DAGA CIKINSU BA ZAI MUTU BA, HAR SAI BAYAN AN HAIFA MASA MAZAJE GUDA DUBU DAGA CIKIN TSATSONSA, KOWANNENSU YANA DAUKE DA KAYAN YAQI".

Sai wani Sahabi yace "Ya Rasulallahi, Siffanta mana su mana!".

Sai yace : "SU NAU'I UKU NE (KAMANNIN HALITTARSU).

1. AKWAI WADANDA SUKE (DA TSAWO) MISALIN BISHIYAR NAN TA URZU. WATA BISHIYA CE NAI TSAWON ZIRA'I 'DARI DA ASHIRIN.

2. SAI KUMA WASU NAU'I WADANDA TSAYINSU DA KAURINSU DUK 'DAYA NE - WATO ZIRA'I GUDA. (TSAWONSU ZIRA'I DAYA, KAURINSU MA HAKA).

3. SAI KUMA WANI NAU'IN WADANDA SUKE (DA MANYAN KUNNUWA) SUNA SHIMFIDA KUNNE 'DAYA SUYI KAFITA DASHI.

'DAYA KUNNEN NASU KUMA SUYI MAYAFI DASHI".

BA ZASU WUCE TA KUSA DA WATA GIWA KO NAMAN DAJI, KO ALADE (AL-HANZIR) BA, FACHE SAI SUN CINYESHI.

KUMA DUK WANDA YA MUTU DAGA CIKINSU MA, CINYESHI SUKE YI (WATO SUNA CIN NAMAN 'YAN UWANSU).

NA GABANSU SUNA KASAR SHAM, 'YAN BAYANSU KUMA SUNA KHURASAN (WATO AFGHANISTAN).

ZASU SHANYE KOGUNAN GABASHIN DUNIYA, KUMA ZASU SHANYE BUHAIRATUT TABRIYYAH (WANI KOGI NE A KASAR FARISA).

AMMA ALLAH ZAI KANGESU DAGA SHIGA GARIN MAKKAH DA MADINA DA BAITUL MAQDIS".

Sayyiduna Aliyu bn Abi Talib (ra) yace: "akwai wasu nau'i daga cikinsu wadanda tsawonsu kamar kamu guda ne (wato tsawon yatsa guda biyu).

Suna da farata (farce) da kuma Hakora irin na Zakoki. Da jiki irin na dabbobi, suna kuka irin na Kuraye, kuma suba taruwa kamar yadda tattabaru sukeyi.

Suna da gashi duk jikinsu, wanda yake karesu daga Sanyi da zafi.

Suna da manyan kunnuwa guda biyu. Daya kunnen na gashi ne. Suna fakewa daga Sanyi acikinsa. 'daya kunnen kuma na fata ne. Dashi suke fakewa alokacin zafi.

Suna tonon wannan katangar, sai sun kusan tureshi sai kuma Allah ya mayar dashi kamar yadda yake.

Sai sunce gobe zamu tureshi "IN SHA ALLAHU TA'ALA". Sannan zasu tureshi, su fito (zuwa cikin duniya).

Mutane zasu tsere daga garesu acikin manyan katangu da benaye (saboda suna kashewa duk mutanen da suka kama, sannan su cinye namansa 'danye).

Daga nan sai su rika harba kibiyoyinsu zuwa sararin samaniya, sai adawo musu da kibiyoyin chakude da jini.

Daga nan sai Allah ya sanya musu wata chuta (mai kamar tsotsa) a wuyansu, ya hallakar dasu.

Manzon Allah (saww) yace "NA RANTSE DA WANDA NUMFASHINA KE HANNUNSA, DABBOBIN DA SUKE DORON QASA SAI SUN QOSHI SUNYI KITSE SOSAI DAGA CIN NAMAN YAJOOJU WA MAJOOJU DA KUMA JININSU

Imamu Ahmad da Tirmiziy, da Ibnu Maajah ne suka ruwaitoshi.

Abu Sa'eed Alkhudriy (ra) yaji Manzon Allah (saww) yana cewa:

"Za'a bude ma Yajooju wa Majooju Qofa su shigo cikin duniya, kamar yadda Allah ya fada, "SUNA TAFIYA DA SAURI TA CIKIN DUKKAN SASANNI".

Mutane zasu firgita su gudu daga garesu, zasu fake daga garesu acikin katangu da birane. Kuma zasu taho da dabbobinsu ma tare dasu.

Mutanen Yajooju wa Majooju din zasu yi yawo adoron Qasa, zasu shanye duk ruwan dake doron Qasa.  Wani daga cikinsu zai wuce ta kusa da wani kogi, sai yace "Da chan kuwa, akwai ruwa anan wajen".

Bayan kowanne mutum ya riga ya buya daga garesu, sai wani daga cikin YAJOOJU WA MAJOOJU yace : "Wadannan duk Mazaunan doron Qasa ne, mun gama dasu. Saura yanzu mazauna cikin Sammai".

Sai wani daga cikinsu ya harba kibiyarsa zuwa sama, sai adawo masa da ita, tana jike da jini. Suna cikin wannan halin sai Allah ya turo musu da wata irin chuta awuyansu, kamar tsutsotsin nan na Aljaraad zasu kama wuyansu. Zasu mutu, ko motsinsu ba Za'a ji ba.

(Imamu Ahmad ne ya ruwaito).

Awata ruwayar kuma, Annabi Eisa (as) shine zai yi addu'a sai Allah ya turo da Mala'iku suzo su kawar da Gawarwakin YAJUJU WA MAJUJU din, bayan sun cika duniya da warinsu.

Anan zamu tsaya sai a karatu na gaba. In sha Allahu zamu dauko wani batun mu tattauna akai.

DAGA ZAUREN FIQHU WHATSAPP (3). 05/09/2015.
Share:

Sunday, 23 September 2018

Shin ko kunsan Cewa Sallar Jana'Iza kabbarorinta suna wuce 4

*JANA'IZA A MAHANGAR SUNNAH??-07!!*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*KITABU WAS SUNNAH*
.
.
*ﻣﺠﻠﺲ ﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ*
📓📔
Watsaps
08036222795
09031200070
.
.
...
Yau 09-04-1439 wacce tayi dai dai da, 27-12-2017, Cigaban Lekca mai taken *JANA'IZA A MAHANGAR SUNNAH:*
...
=
Wannan shine bayani na Bakwai:
=
=
*«ﺇِﻥَّ ﺍﻟْﺤَﻤْﺪَ ﻟِﻠَّﻪِ، ﻧَﺤْﻤَﺪُﻩُ ﻭَﻧَﺴْﺘَﻌِﻴﻨُﻪُ، ﻣَﻦْ ﻳَﻬْﺪِﻩِ ﺍﻟﻠﻪُ ﻓَﻠَﺎ ﻣُﻀِﻞَّ ﻟَﻪُ، ﻭَﻣَﻦْ ﻳُﻀْﻠِﻞْ ﻓَﻠَﺎ ﻫَﺎﺩِﻱَ ﻟَﻪُ، ﻭَﺃَﺷْﻬَﺪُ ﺃَﻥْ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻟَّﺎ ﺍﻟﻠﻪُ ﻭَﺣْﺪَﻩُ ﻟَﺎ ﺷَﺮِﻳﻚَ ﻟَﻪُ، ﻭَﺃَﻥَّ ﻣُﺤَﻤَّﺪًﺍ ﻋَﺒْﺪُﻩُ ﻭَﺭَﺳُﻮﻟُﻪُ*
_Bayan haka yanzu kuma kai tsaye zamu shiga bayanine gameda Sallar jana'iza, Ita sallar gawa fardu kifaya ce wato wasu suna dauke ma wasu, idan akayi mutuwa a gari ko unguwa sai wasu jama'a koda 'yan kadanne daga cikin mutanen wannan unguwar suka tsayu sukaima wannan gawar sallah to shikenan babu zunubi ko laifi akan sauran jama'a wadanda basuzo akayi wannan sallar dasu ba, Amma mutane guda biyu sukuma ba dole bane sai anyi musu sallar gawa. Nafarko shine yaro qarami wanda bai balaga ba, idan yaro karami ya rasu to ba dole bane sai kunyi mishi sallah, kuna iya rungumar gawar kawai kuje ku birneta ba tareda kunyi mata sallah ba, amma dai babu laifi idan kunyi sallar saboda akwai gagarumin lada wanda ake samu idan akayiwa gawa sallah kunga sai ku rabauta da wannan ladan, na biyu kuma shine shahidi wanda ya mutu a fagen jihadi shima wannan ba dole bane akanku sekunyi masa sallah, amma dai shima din kuna iya yin masa sallan dan ku samu ladanda ake samu bawai saboda yin sallar wajibi bane****_
      _Sannan kuma wannan sallar anso yazama ansamu a qalla sahu uku koda kuwa mutanen basuda yawa koda basu wuce mutane gomaba inso samune arabasu zuwa sahu uku, inkuma sunyi yawa to ana iya qara yawan sahun yafi uku*****_
      _Kuma ya halasta ayima gawa sallah acikin masallaci, amma bai halasta ayi sallar a tsakanin qaburbura ba, wato qabarine guda biyu ko sama da haka sai a ajjiye gawa a tsakaninsu sai ayimata sallah anan wajan wannan bai halastaba kenan dai zamuce baya halasta ayima gawa sallah acikin maqabarta****_
     _Sannan kuma idan gawar namijine to limamin zai tsayane saitin kansa idan kuma mace ce liman zai tsaya tsakiyarta daidai saitin qugunta****_
      _Yadda akeyin sallar kuwa shine: Anayin kabbara hudu, ko biyar ko shida ko bakwai ko takwas ko tara, amma anfi yin guda hudu sedai ana duba darajar mamacin da irin gwagwarmayar da yayi wajen cigaban addini sai ayi masa kabbarorin gwargwadon yadda akaga ya kamata walau biyar ko shidan har zuwa tara****_
       _Amma yanada kyau shi liman kafin afara sallah ya gayawa mutane cewa kabbara kaza zamuyi, sedai kuma fadin hakan ba dole bane akan liman amma dai kyautatawace dan susan abinda zakayi, sannan kuma yanada kyau kagaya musu bayan kowacce kabbara ga abinda ake karantawa saboda mafiya yawan mutane sallar kawai sukeyi amma basusan mene ake fadi abayan kowacce kabbara ba, wannan kuma yafarune saboda irin yadda mutane mukayi sakaci da karatu muka kauracewa malamai babu ruwanmu da yin sallah kamar yadda Annabi (s.a.w) ya koyar kawai dai munayin sallah ne kamar yadda mukaga wadansu mutane sunayi, wanda kuma hakan babu shakka kuskure ne yazama wajibi akanmu lallaine mutashi munemi ilimin addininmu saboda yazama duk ibadarda zamu aikata to munayintane akan basira dakuma haske na ilimi****_
        _Hujja kuwa akan cewa ana yin kabbarori sama da hudu a sallar gawa daga ciki akwai hadisi wanda Imamu Muslim ya ruwaito acikin littafinsa hadisi mai lamba 957, Abu Dawuda 3181, Tirmizi 1028, Ibnu Majahi 1505****_
       _Hujjarmu kuma akan cewa anayin  kabbarbari masu yawane da gwargwadon irin gudun muwarda mamacin yaba addini, Akwai hadisin Sallar gawar Imrana Dan Hussaini wanda Aliyu dan Aby Dalib ne yayi masa kabbarori tara, gakuma sallar gawar Sahlu dan Hanif wanda shima dai Aliyu dinne yayi masa sallah da kabbarori shida, sannan ya fuskanci mutane yace aishi Sahlu ya halarci yaqin badar, wannan hadisin yana cikin Ahkamul Jana'iz shafi na 113, Har ila yau kuma akwai sallar gawar Abu Qatada wadda itama dai Sayyidina Ali ne yayi kuma yaimasa kabbara bakwai shima Abu qatada ya halarci yaqin badar****_
      _Hakadai sayyidina Aliyu yakasance yanayin kabbarori shida zuwa sama akan duk sahabinda ya halarci yakin badar, amma sahabinda baije badar ba Aliyu yanayin masa kabbara biyar ne, Tabi'i kuma wanda ba sahabi ba Aliyu yanayi masa kabbara hudu****_
      _Kankat kuma idan muka duba hadisin Sallar gawar Sayyidina Hamza Annabi (s.a.w) yaimasa kabbarori guda tara shima, Imamu Dahawi ya ruwaito wannan acikin Sharhu Ma'anil Athar mujallad na farko shafi na 290*****_
=
=
_Zan tsaya anan saikuma darasi nagaba idan Allah yakaimu***_
.
_Almajirinku ne kamar kullun_
.
```Jameel Alhassan Haruna kabo```
.
_(Abu khausar)_
.
 .
Allah ta,ala ya tsaremu
.
.
.
Zaku iya samun shafinmu na facebook tawannan hanyar
https:/t/m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-1522000298067561/
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Subhanak Allahumma wabi hamdika ash hadu anla ila ha illa h anta astagfiruka  Wa,atubu ilaika
Share:

Thursday, 16 August 2018

[Audio] :- Karyarku 'Yan Shi'a Asirinku Ya Tonu - Sheikh Kabiru Haruna Gombe

Sheikh : _*MUHAMMAD KABIRU HARUNA GOMBE*_
( *Sakataren kungiyar Izala ta kasa*)


Asabar : *11 August 2018*


Wuri : *Masallacin Sultan Bello Kaduna*

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAUKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇🏼👇🏼👇🏼

DOWNLOAD AUDIO NOW

_*Kar  Ku  Sake  A  Baku  Labari .........*_

Ayi Sauraro  Lafiya  👂🏻



Share:

Wednesday, 8 August 2018

HUKUNCIN WANDA YA SADU DA MATARSA ACIKIN HAILA

HUKUNCIN WANDA YA SADU DA MATARSA ACIKIN HAILA :

TAMBAYA TA 2547
*******************
SALAMUN ALAIKUM MALAM MENENE HUKUNCIN WANDA YASADU DA MATARSHI TANA HAILA AMMA ARASHIN SANI ?

NAGODE MALAM.

AMSA
*******
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Allah Madaukakin Sarki ya haramta wa Mazaje saduwa da Matayensu alokacin da suke cikin jinin haila. Allah yace :

"SUNA TAMBAYARKA GAME DA JININ HAILA, KACE (MUSU) SHI NAJASA NE. KU NISANCI MATAYE ACIKIN FARJOJINSU KADA KU KUSANCESU (DA JIMA'I) HAR SAI SUNYI TSARKI".

(Suratul Baqarah ayah ta 223).

Kuma akwai hadisin da Manzon Allah (saww) yace Wanda yayi jima'i da matarsa alhali tana haila,  to sai yayi sadaqah da dinare guda (Kamanin naira dubu sittin ₦60,000).

Acikin Maluman Fiqhu akwai wadanda suka tafi bisa doron hadisin. Akwai kuma wadanda suka ce zai yi istighfari ne tunda ya aikata babban laifi. Amma babu kaffara akansa.

Imamun Nawawiy yace "Da ache mutum zai aikata haka (wato jima'i da mai haila) cikin Mantuwa ko rashin sanin cewa tana haila, ko rashin sanin haramcinsa to babu laifi akansa kuma babu kaffarah.

Amma idan mutum ya aikata hakan da gangan, tare da sanin cewa akwai hailar, da kuma sanin haramcinsa, to hakika ya dauki zunubi mai girma kuma wajibi ne gareshi ya tuba".

Kuma acikin maganar wajibcin yin kaffarar akwai zantuka guda biyu. Amma abinda yafi inganci shine babu kaffarah akansa".

WALLAHU A'ALAM.

DAGA ZAUREN FIQHU (30/07/2018  17/11/1439).
Share:

Tamabaya da Amsa :- Shin yana hallatta macce budurwa tashafa turaree Sannan tafito waje dashi??

*|```Assalamu alaikum*```
*```Malam ko ya hallatta macce budurwa tashafa turaree Sannan tafito waje dashi??*```



_*AMSA:*_
*******

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،


Haramun ne mace ta sanya turare ta fita inda wasu maza zasuji kamshinsa. Dalili kuwa shine:


ﺛﺒﺖ ﻋﻦ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺃﻧﻪ ﻗﺎﻝ: ﺃَﻳُّﻤَﺎ ﺍﻣْﺮَﺃَﺓٍ ﺍﺳْﺘَﻌْﻄَﺮَﺕْ ﻓَﻤَﺮَّﺕْ ﻋَﻠَﻰ ﻗَﻮْﻡٍ ﻟِﻴَﺠِﺪُﻭﺍ ﻣِﻦْ ﺭِﻳﺤِﻬَﺎ ﻓَﻬِﻲَ ﺯَﺍﻧِﻴَﺔٌ.
ﺭﻭﺍﻩ ﺍﻹﻣﺎﻡ ﺃﺣﻤﺪ‏(19212‏) ﻭﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ ‏(5126‏) ﻭﺣﺴﻨﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ.

_Ya tabbata daga *Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam)* yace idan mace ta sanya turare ta wuce ta gaban mutane (Maza) domin suji kanshin turaren ta, toh ita mazinaciya ce._
*Imam Ahmad ya ruwaito shi a hadisi mai lamba 19212.* da *Nisaa'i hadisi mai lamba 5126.*
_Albani ya inganta shi Cikin sahihul jami'i._


ﻋَﻦْ ﺯَﻳْﻨَﺐَ ﺍﻣْﺮَﺃَﺓِ ﻋَﺒْﺪِ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺑﻦ ﻣﺴﻌﻮﺩ، ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﺎ ﻭﻋﻦ ﺯﻭﺟﺎ، ﻗَﺎﻟَﺖْ: ﻗَﺎﻝَ ﻟَﻨَﺎ ﺭَﺳُﻮﻝُ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺻَﻠَّﻰ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻭَﺳَﻠَّﻢَ: ﺇِﺫَﺍ ﺷَﻬِﺪَﺕْ ﺇِﺣْﺪَﺍﻛُﻦَّ ﺍﻟْﻤَﺴْﺠِﺪَ ﻓَﻠَﺎ ﺗَﻤَﺲَّ ﻃِﻴﺒًﺎ.
ﺭﻭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ ‏(443).

_An karbo daga *Zainab* matar *Abdullahi Ibn Mas'ud* (radiyallahu anha Wa zaujaha) tace: *Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam)* yace damu; Idan dayanku zata tafi masallaci kada a shafa turare._
*Muslim ya ruwaito shi a hadisi mai lamba 443.*



والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_
Share:

Tuesday, 7 August 2018

Hukunce-Hukuncen Mai Takaba ?? Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

*HUKUNCE-HUKUNCEN MAI TAKABA*


*Tambaya:*

Assalamu alaikum wa rahmatullaah. gafarta Malam pls ayi mana bayani koda a takaice ne dangane da hukunce - hukuncen takaba... Na shiga wajen mahaifiya dazu, take cewa in tambaya mata Malamai tanadin shari'a akan wannan al'amari. Nagode


*Amsa:*

Wa alaikum assalam.To dan'uwa ina rokon Allah ya jikan mahafinku, akwai hukunce-hukunce  da suka shafi takaba, ga muhimmai daga ciki:

*1.* Mai takaba za ta zauna a gidan mijinta ba za ta fita ba, har sai ta gama iddarta, wacce take wata hudu da kwana goma, kamar yadda aya ta: 234 a suratul Bakara take nuni zuwa hakan .

*2.* Ba za ta saka kaya masu kyau ba, don haka za ta guji ado, kamar yadda hadisin Abu-dawud mai lamba ta: 2304, ya yi bayanin hakan.

*3.* Shari'a ta hana mai takaba ta sanya turare, kamar yadda hadisin Bukhari mai lamba ta: 5343, ya tabbatar da hakan,

*4.* Malamai suna cewa mai takaba ba za ta sanya tozali ba , kamar yadda hadisin Nasa'i mai lamba ta: 3565 ya bayyana hakan.

*5.*  An hana mai takaba yin lalle,  kamar yadda hanin ya zo a hadisin Abu-dawud mai lamba ta: 2304.

*6.* Idan wata bukata ta kama za ta iya fita daga gida, ko da rana ne ko da dare.

*7.* Za ta iya yin Magana da mazan da ba muharramanta ba, idan bukatar hakan ta kama, saidai ta guji, sanyaya murya, kamar yadda aya ta 32 a suratul-ahzab ta hana sanyaya murya ga wadanda ba muharramai ba.

*8.* Babu wani launi na kaya na musamman da aka shar'anta mata ta sanya, don haka, duk kayan da ba kwalliya a jikinsu ya halatta ta sanya su .

*9.* Za ta iya yin wanka da sabulun da yake ba mai kanshi ba .

*10.* Za ta iya zama ta yi hira da makusantanta, har ma za ta iya bude gashin kanta, idan su duka muharramanta ne .

*11.*  Bai halatta wani ya nemi auranta ba, har sai ta gama idda, saidai za'a iya yin jirwaye mai kama da wanka, kamar yadda aya ta 235 ta yi nuni zuwa hakan.

*12.* Idan mai takaba tana da ciki, to iddarta ita ce:  haife abin da take dauke da shi, kamar yadda hadisin Subai'a mai lamba ta: 5014 a Sahihul Bukhari ya tabbatar da hakan.

Allah ne mafi sani.

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*

27\3\2015
Share:

Sunday, 1 July 2018

Tufka da Warwara!!! Daga Dr.Muhammad Rabi'u R/lemo

*TUFKA DA WARWARA!!!*
Daga👇🏽
*Dr. Muhammad Rabi'u R/ Lemo*

Kullum ihu suke suna siffata malamai masu kira zuwa ga sunnah da bin tafarkin magabata da Yan Ikhwan, suna kira a nisance su, a nisanci majalisansu da wuraren karantarwarsu da wa'azinsu, amma su suna cikin jami'o'in da suke cike da yan Ikhwan din na hakika, kai! Har ma da wadanda suke zagin addinin da masu addinin, suna zama aji su karantar da su, amma su daidai suke yi, su ne salaf, alhali da yawa daga cikin malaman da suke suka da batawa suna sun yi karatu ne wurin manya-manya malaman sunnah, sun halacci majalisan su, sun zauna da su.
Haka nan da zaka dawo tarihin wadannan masu ihun ba a kan salafiyya malaman mu suke ba, zaka taras mafi yawancinsu ba su fahimci addini da ilimin addini ba, sai ta hanyar wadannan malamai ko almajiransu, su ne suka kama hannunsu zuwa ga ilimi da sunnah, amma yau su ne yan Ikhwan, wanda da zaka tambaye su tsakani da Allah, tunda kuke karatu wurinsu ko wurin almajiransu, sun taba kiranku ga wata kungiya wai ita Ikhwan, za su ce maka, a'a. To ta yaya yanzu suka zama yan Ikhwan.

Na rantse da Allah babu wani abu da suke sukan malaman mu da shi, suke siffata su da yan Ikhwan saboda shi, face sai ka samu, su da malaman da suke ganin su ne kadai yan salafiyya suna cikin irin wannan abun.

Dan uwa ka maida hankali ga karatunka, ka watsar da rudu da hayaniya.
Allah ka jikan malaman mu, wadanda suka kare rayuwarsu wajen yada sunnar Annabinka (S.A.W) irin su :  Sheikh Abubakar Mahmud Gumi, sheikh Isma'il Idris, Sheikh Ja'afar, Sheikh Albani Zari'a, da sauran malaman Sunnah. Ameen.

Daga
*ZAUREN FIQHUS SUNNAN* / *MINBARIN SUNNAH*
Share:

Thursday, 28 June 2018

Tambaya da Amsa :- Shin yana halatta ga Mutum bayan yayi zina da mace, kuma ya Aureta ??

*```Assalamu alaikum Malam yana halatta ga mutum bayan yayi zina da mace, yana halatta ya aure ta?*```


_*AMSA:*_
*******

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ


A shari'ance baya halatta ga mutum ya auri wacce yayi Zina da ita har sai sun tuba _*(Taubatan Nasuuhan)*_ su biyun.

*TUBA* yana tabbatuwa ne idan mutum yayi nadama akan abinda ya aikata da yin kyakkyawar niyyar bazai sake aikatawa ba.

Saboda haka idan sun tuba kuma sunyi nadamar abinda sukayi kuma sunyi alwashin bazasu sake aikatawa ba, to yana halatta agaresu suyi aure abisa ra'ayin mafi yawan malamai.

*Ibn Qudaamah (rahimahullah)* yace: Idan mace tayi Zina, to baya halatta ga Wanda yasani ya aureta har sai an cika sharudda biyu;
*1.* Ta gama iddarta.
*2.* Ta tuba daga Zinar da ta aikata
      Idan wadannan sharuddan sun cika, to ya halatta a aureta abisa ra'ayin lafiya yawan malamai, wannan shine ra'ayin Abubakar Al-siddiqu, Umar ibn Khaddab, Ibn Umar, Ibn Abbaas, Jaabir, Sa‘eed ibn Al-Musayyab, Tawoos, Jaabir Ibn Zayd, Ata’, al-Hasan, Ikrimah, Az-Zuhri, ath- Thawri, Ash-Shaafa‘i, Ibn Al- Mundhir da Ashaab ar-ra’y.
_*(All-Mughni , 7/108.)*_


والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_
Share:

Tambaya da Amsa:- Menene Hukuncin mata masu huda Hanci ??

*```ASSALAMU ALAIKUM!!!*```
*```MENENE HUKUNCIN MATA MASU HUDA HANCI??*```



_*AMSA:*_
********


وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ


An tambayi _*Shaykh Muhammad Saalih Al-Uthaymeen (Rahimahullah)*_ gameda Huda Hanci da Huda kunnuwa da ake yiwa yara mata saboda suyi kyau? Sai yace:
Ra'ayin da yake daidai shine babu laifi akan Huda kunne, saboda daya daga cikin dalilan huda kunne shine sanya halatattun kayan ado (Yan Kunne). An san cewa mata sahabbai sunada yan kunne da suke sanyawa a kunnuwansu.

Zafin ciwon hudawar mai sauki ne, kuma idan anyi huduwar ne a lokacin da yarinya tana karama, yafi saurin warkewa.


Abinda ya shafi *HUDA HANCI* kuma bazan iya tina cewa malamai sunce wani abu akan Huda Hanci ba, amma dai wani nau'in ne na canza halitta da gurguntawa idan muka kalli fuskar daga wajenta, duk dayake wasu basa kallonsa ta wannan fuska.

Idan mace tana acikin kasa ko gari Wanda sanya kayan ado a Hanci ana kallonsa wani nau'i ne na kwalliya da ado, to, babu wani abin laifi ga huda Hanci.
_*(Majmu'ul Fataawa Ibn Uthaymeen, shafi na 11, tambaya ta 69).*_



والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_
Share:

Wednesday, 27 June 2018

Maganin Fitsarin Kwance daga Zauren Fiqhu

MAGANIN FITSARIN KWANCE :

TAMBAYA TA 2161
****************
Assalamu'alaikum Malam muna lafia, ya aiyuka ya Dalibai? Allah yayi mana jagoranci na alheri. Amin.

Malam Dan Allah a taimaka mana da maganin fitsarin kwance, wata  diyar yar'uwata ce ta kusa shekara 10 take fama dashi.

Sannan kuma ina barar addu'arka data dalibanka akan Allah ya kawo mani mijin aure mafi alheri. Amin. Jazakallahu Khair. Pls hide my I. D.


AMSA
***
Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Ita wannan matsalar ana iya shawo kanta ne ta hanyoyi guda biyu kamar haka :

MAGANI : A nemi kwayoyin habbatus sauda, a rika yiwa yaro hayaki dasu. Kuma yana dan tsugunawa akan hayakin. Sannan kuma a rika gauraya masa habbatus sauda din yana shan cokali guda tare da zuma. Ko kuma ya shafe jikinsa da man Habbatus sauda din wanda akayi tofi acikinsa. In sha Allahu zai dena.

2. ADDU'A : Arika tofa masa wannan addu'ar, ko kuma akoya masa ya rika yinta da kansa, ko kuma a rubuta masa ajikin takarda ya sanya ajikinsa yayin da zai kwanta.

Kamar yadda aka ruwaito daga Abdullahi bn Amru bn Al-As Sahabin Manzon Allah (saww) yana rataya ma 'ya'yansa Qanana wannan addu'ar. Gata nan kamar haka :

"أعوذ بكلمات الله التامات من غضبه وعقابه ومن شر عباده و من همزات الشياطين و أن يحضرون".

'A'udhu bi kalimatil Laahit tammati min ghadhabihee wa 'iqabihee wa min sharri ibadihee wa min hamazatish shayateen wa an yahdhurooni.

FASSARA : Ina neman tsari da cikakkun kalmomin nan na Allah daga fushinsa da Uqubarsa, kuma daga sharrin bayinsa, kuma daga sharrin fizge-fizgen shaitanu, kuma (ina neman tsarinsa) kada su halartoni.

In sha Allahu koda babban mutum ne yake fama da matsalar fitsarin kwance, in dai ya lazimci wadannan abubuwan tare da gaskatawa zai ga biyan bukatarsa.

WALLAHU A'ALAM.

Muna rokon Allah da albarkar sunayensa da siffofinsa da kalmominsa, ya baki Miji nagari. Ya tsare miki mutuncinki da imaninki dake da dukkan dalibanmu da 'yan uwanmu Mata marassa aure. Ameeen.

DAGA ZAUREN FIQHU.
Share:

Tambaya da Amsa :-Hukuncin yin sallar jam'i A Gida !!! Dr. Jamilu yusuf zarewa

*_HUKUNCIN YIN SALLAR JAM'I A GIDA !!!_*

*_Tambaya_*

Assalamu alaikum.  Malam mene hukuncin sallar  namiji da ba ya son zuwa masallaci  jam'i saidai ya tara iyalinsa a gida ayi sallah tare?


*_Amsa_*
Wa alaikum assalam

To 'yar'uwa Malamai sun yi sabani game da sallar jam'i a masallaci.

1. A wajan malaman Malikiyya zuwa sallar jam'i sunna ne saboda fadin Annabi S. A.W. "Sallar jama'a tafi sallar mutum daya da lada ashirin da bakwai" hadisin yana nuna ingancin sallar wanda ya yi sallah shi kadai, tun da an tabbatar masa da lada daya.

2. Ya wajaba yin sallah a masallatai a cikin jama'a saboda fadin Annabi (SAW)  "Na yi niyyar na yi umarni a tsayar da sallar jam'i, ni kuma na je na kona gidajan wadanda ba Sa halarta sallah a masallaci" wannan ita ce maganar Malamai da yawa.
Ibnu-Mas'ud yana cewa: "Babu wanda yake kin zuwa sallar jam'i sai munafiki, wanda aka san  shi da munafunci,  akan kawo mutum ranga-ranga ba shi da lafiya a tsayar da shi a tsakanin Sahu".
Wani Makaho ya zo wajan Annabi (SAW)  ya nemi ya yi masa izni ya yi sallah a gida saboda ba shi  da Jagora, ya ba shi izni,  bayan ya tafi sai ya Kira shi ya ce masa kana jin kiran sallah? sai ya ce E, sai ya ce to ka amsa".

Allah yana cewa a Suratul Bakara aya ta (43): "Kuma ku yi sallah tare da masu yin sallah"

A bisa dalilan da suka gabata za mu fahimci cewa: Yin sallar jam'i a masallaci shi ne abin da Shari'a ta zo da shi, kuma wajibi ne ga wanda yake da iko, tun da ga shi har Annabi (SAW) ya yi niyyar zai kona gidan wadanda ba sa halarta.
Idan akwai nisa tsakaninsa da masallaci ko kuma yana da lalura ba za'a ce ya aikata haramun ba in ya yi sallah a gida tare da iyalansa saboda fatawar Malikiyya da ta gabata da kuma aya ta karshe a suratul Hajj wacce take nuna sauki da rashin kunci a addinin musulunci.

Allah ne mafi sani.

*_Dr. Jamilu Zarewa_*

27/06/2018

Daga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*
Share:

Tuesday, 26 June 2018

Tambaya da Amsa :- Idan mutum ya rasu ya bar Mata guda daya1 da 'ya'ya maza guda uku 3 da 'ya mace guda daya1, kuma ya bar dukiya ta miliyan takwas da dubu 'dari biyar (8.5million). Ya Kason kowa zai kasance?

*```Assalamu alaikum*```
*```Tambaya na shine:*```
*```Idan mutum ya rasu ya bar Mata guda daya1 da 'ya'ya maza guda uku 3 da 'ya mace guda daya1, kuma ya bar dukiya ta miliyan takwas da dubu 'dari biyar (8.5million). Ya Kason kowa zai kasance?*```




_*AMSA:*_
*******

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،



Abu Na farko daza'a aiwatar akan dukiyar mamaci shine biyan bashi da wasiyya, kafin a shiga gundumar rabon gado.


Idan namiji ya rasu yabar mata daya da yara maza uku (3) da 'ya mace daya.
Idan wadannan sune magadansa kadai wadanda ya bari.

To anan kason matar zai kasance 1/8 (Sumuni) Na dukiyar da yabari, 'yarsa daya mace za'a bata Rabin kason namiji daya.
Kamar yadda Allah ya fada acikin Suratun Nisaa'i ayah ta 11 da 12.

ﻳُﻮﺻِﻴﻜُﻢُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻓِﻲ ﺃَﻭْﻟَﺎﺩِﻛُﻢْ ۖ ﻟِﻠﺬَّﻛَﺮِ ﻣِﺜْﻞُ ﺣَﻆِّ ﺍﻟْﺄُﻧْﺜَﻴَﻴْﻦ

Allah yana yimuku wasiyyah acikin 'ya'yanku, namiji yanada rabon mata biyu.........(Nisaa'i 11)


ﻭَﻟَﻬُﻦَّ ﺍﻟﺮُّﺑُﻊُ ﻣِﻤَّﺎ ﺗَﺮَﻛْﺘُﻢْ ﺇِﻥْ ﻟَﻢْ ﻳَﻜُﻦْ ﻟَﻜُﻢْ ﻭَﻟَﺪٌ ﻓَﺈِﻥْ ﻛَﺎﻥَ ﻟَﻜُﻢْ ﻭَﻟَﺪٌ ﻓَﻠَﻬُﻦَّ ﺍﻟﺜُّﻤُﻦُ ﻣِﻤَّﺎ ﺗَﺮَﻛْﺘُﻢْ ﻣِﻦْ ﺑَﻌْﺪِ ﻭَﺻِﻴَّﺔٍ ﺗُﻮﺻُﻮﻥَ ﺑِﻬَﺎ ﺃَﻭْ ﺩَﻳْﻦ

........Kuma (Su Matan) sunada rubu'i daga abinda kuka bari (Na dukiya) idan reshe ('ya'ya) bai kasance ba gareku, to, idan kuwa reshe ya kasance gareku, to sunada sumuni (1/8) daga abinda kuka bari, daga bayan wasiyya wanda kukayi ko kuma bashi (debt)............(Nisaa'i 12).

Reshe acikin ayah ta 12 yana nufin 'ya'ya. Idan miji ya mutu yabar mata ita kadai babu 'ya'ya, to rabon ta shine 1/4.

Idan kuma akwai 'ya'ya to rabonta shine 1/8 kamar yadda ya tabbata a ayar.

A tambayar mu ta sama. Namiji ya rasu yabar masu gadonsa kamar haka:
1. Mata daya
2. Yara Maza uku (3)
3. Yarinya daya

Sannan yabar kudi naira miliyan takwas da dubu dari biyar:
N8,500,000

Ga yadda kason kowa zai kasance:

MATA
******
Za'a bata 1/8 Na N8,500,000
Shine ya kama miliyan daya da dubu sittin da biyu da naira dari biyar.

====N1062500


Idan an cire rabon matarsa, za'a bar N7,437,500.

Anan maza uku ne, kowanne kashi biyu za'a bashi, mace kuma kashi daya.

Idan ka hada kashi biyu sau uku zai baka kashi shida.
       (2×3)=6

Sannan a tara da kashi daya Na mace zai bamu kashi bakwai
6+1=7

Yanzu zamu raba N7,437,500 zuwa gida bakwai

(N7,437,500/7)==N1062500.

Mace kashi daya
Kowanne namiji kashi biyu.

Kashi biyu zai bamu
1062500+1062500
      ==N2,125,000


YARA MAZA
**************
Kowannensu zai samu " Naira Miliyan biyu da dubu dari da ashirin da biyar"

======N2,125,000


'YARSA MACE
***************
Zata samu "Naira miliyan daya da dubu sittin da biyu da naira dari biyar"

======N1,062,500.




والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_
Share:

Sunday, 20 May 2018

Hikimomin da Azumi ya kunsa....Dr.jamilu yusuf zarewa

*HIKIMOMIN DA AZUMI YA KUNSA*

*Tambaya:*

Assalamu alaikum Don Allah malam a taimaka min da bayani game da sababin da yasa ake yin azumi??

*Amsa:*

Wa alaikum assalam Azumi ginshiki ne, daga cikin turakun musulunci, wadanda addinin musulunci, ba zai cika ba sai da su, Allah da manzonsa sun yi umarni da shi, saboda wasu muhimman manufofi, ga wasu daga ciki :

*1.* Samun tsoron Allah, saboda mai azumi yana barin abin da yake so saboda Allah, hakan zai sa, ya kara samun tsoron Allah.

*2.* Samun kariya daga Shaidan, saboda azumi yana takure hanyoyin Shaidan, wannan ya sa zunubai suke karanci a Ramadan.

*3.* Tuna talakawa da wahalar da suke ciki, saboda duk lokacin da mai kudi ya dandana yunwa zai tuna halin da talakawa suke ciki .

*4.* Sabawa rai wajen barin abin da take so, da kuma hakuri akan abin da take sha'awa.

*5.* Kankare zunubai da kuma samun daukakar daraja, saboda azumi yana gyara zuciya, da kuma rai.

*6.* Samun lafiyar jiki, saboda azumi yana kariya daga cututtuka masu yawa, kamar yadda likitoci suka tabbatar da hakan.

*7.* Ta hanyar azumi mutum zai saba da yin aikin don Allah, saboda azumi sirri ne tsakanin Allah da bawansa.
Allah ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
29/1/2013

Daga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*
Share:

Ramadhaniyyat@1439H [3] - Sheikh Dr. Muhd Sani Umar R/lemo

*Ramadhaniyyat@1439H [3]*

*Daga Sheikh Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*

Tahajjudi

Allah Ta'ala yana cewa:
(Da daddare kuwa sai ka yi tsayuwar dare da shi (Alqur’anin) qarin (daraja) ne gare ka, tare da qaunar Ubangijinka ya tashe ka a matsayin sha-yabo ("watau matsayin mai ceto"). Isra'i, aya ta 79.

A Makka ne Allah ya shar'ata wa Annabinsa (S.A.W) tsayuwar dare watau sallar "Tahajjudi". Wannan dalili ne da yake nuna falalar wannan salla. Domin Allah ya shar'anta Annabi (S.A.W) mafi girma kuma mafi falalar ayyuka a Makka. Shar'anta wani aiki tun a farkon Musulunci dalili ne dake nuna girmansa da falalarsa, saboda haka ne ma aka shar'anta Tauhidi tun a Makka, hakanan aka kuma shar'anta wasu daga cikin rukunan Musulunci tun a farko-farkon Musuluncin.
Share:

Audio:-Darasin Tafsirin Al-Qur'an na Watan Ramadan 1439/2018 - Dr.Muhammad SANI Umar R/Lemo

Darasin Tafsirin Al-Qur'an na Watan Ramadan 1439/2018

Rana ta 0(2)

Tare da Dr.Muhammad  SANI Umar R/Lemo

17-05-2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO A WAYOYINKU SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya.


Share:

Audio:-Ramadan Tafsir 1439/2018 ( Darasi na 2) - Sheikh Abdurrazaq Yahaya Haifan



Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 2

Tare da: Sheikh Abdurrazaq Yahaya Haifan

2/9/1439
18/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO A WAYOYINKU SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya.


Share:

Audio:-Ramadan Tafsir 1439/2018 (Darasi na 2) - Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 2

Tare da: Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo

2/9/1439
18/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO A WAYOYINKU SAIKUBSHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya.


Share:

Audio:-Ramadan Tafsir 1439/2018 ( Darasi na 1) - Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tare da: Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya.


Share:

Audio:- Ramadam Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) - Dr. Jabir Sani Maihula



Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tare da: Dr. Jabir Sani Maihula

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇


Ayi saurare Lafiya.


Share:

Audio:- Ramadam Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) - Sheikh Muhammad Kabiru Haruna Gombe

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tare da: Sheikh Muhammad Kabiru Haruna Gombe

2/9/1439
18/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya


Share:

Saturday, 19 May 2018

Audio:- Ramadam Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) - Sheikh Abdurrazaq Yahaya Haifan

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Suratul Ibrahim Ayah 1-5

Tare da: Sheikh Abdurrazaq Yahaya Haifan

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya.


Share:

Audio:- Ramadan Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) - Dr. Muhammad Mansur ibrahim sokoto

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Suratul Nur 1-2

Tare da: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

Malam yaja hankali sosai akan masifar da take fadawa Mazinci

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya
Share:

Friday, 18 May 2018

Audio:- Ramadan Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) -.Sheikh Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tare da: Sheikh Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya.
Share:

Audio:- Ramadan Tafseer 1439/2018(darasi na 1) - Mal. Umar shehu Zaria

TAFSIRIN RAMADAN 1439/2018

Darasi na 1

Daga bakin: _Umar Shehu Zaria_

Alhamis 1 Ramadan, 1439 (17/05/2018). Masallacin Aliyu Usman Kurmin Mashi, Kaduna.

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya


Share:

Audio:- Lecture A Ramadan - Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Lecture A Ramadan

Tare da: Sheikh Aminu Ibrahim daurawa

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi Saurare Lafiya


Share:

Audio:- Ramadam Tafseer 1439/2018 (darasi na 01) - Sheikh Musa Yusuf Asadussunnah

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tafsir Yamma

Tare da: Sheikh Musa Yusuf Asdusunnah

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya

Kuci gaba da kasancewa da wannan shafin akowa da yaushe

More Tafseer is loading 100%.......

Share:

Video:- Ya masu wadata zasu More Watan A Ramadan - Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

JAMI'AR RAMADAN [ZUWA GA MAWADATA]

YAYA MASU WADATA ZASU MORE A WATANA
RAMADAN

Daga👇
*SHEIKH AMINU IBRAHIM DAURAWA*

Domin sauko da wannan Video saiku shiga wannan blue Rubutu dake kasa👇👇👇

DOWNLOAD VIDEO NOW


Ayi saurare Lafiya

DAGA
ZAUREN FIQHUS SUNNA / MIMBARIN SUNNAH


Share:

Wednesday, 16 May 2018

Shin yana halasta a nemawa dan bidi'a gafara da rahamar Allah??

SHIN YA HALASTA A NEMAWA DAN BID'AH GAFARA DA RAHAMAR ALLAH?

Farko dai Aqeedar Al-Wala'u Wal Bara'u (Soyayya da kiyaya) ginshiki ne na Addini, wajibine Musulmi ya so 'yan uwanSa Musulmi kuma yaki kafirai kamar yadda wajibine Dan Salafiyyah yaso 'yan uwan sa kuma yaki 'yan bid'ah GWARGWADON ABINDA YAKE TARE DA SU NA BID'AH KAMAR YADDA ZAI SO SU GWARGWADON ABINDA YAKE TARE DA SU NA SUNNAH. Idan kuma bid'ar ta kafircine to wannan babu wani nau'i ko kaso na soyayya da yake da shi daga Musulmai.

Sai dai shi wannan kiyayyar ba a sake ake yin sa ba, akan yi dubi ne zuwa ga maslaha, wani lokaci bayyana shi kiyayyar shine Daidai, wani lokaci kuma kuskure ne sbd rashin maslaha dake ciki.

2- Nemawa dan bid'ar da bid'arSa ta kafircine gafara da rahamar Allah to, wannan kuskure ne kuma haramunne domin Allah Madaukaki ya hana.
Shaikhul Islam Ibnu Taimiyah yace:
من علم منه النفاق والزندقة فإنه لا يجوز لمن علم ذلك منه الصلاة عليه وإن كان مظهرا للإسلام.
الفتاوى الكبرى (3/18).
Wanda aka san Munafunci da Zindiqanci tattare da shi to, bai halasta ga wanda yasan hakan yayi masa sallah ba koda kuwa ya kasance yana bayyana Musulunci.

2- Dan bid'ar da bid'arSa bata kai ga kafirci ba to, ya halasta a nema masa gafara da rahamar Allah Madaukaki domin shi yana matsayin Musulmi mai sabo da zunubi ne.

Shaikhul Islam Ibnu Taimiyyah yace:
فكل مسلم لم يعلم أنه منافق جاز الاستغفار له، والصلاة عليه وإن كان فيه بدعة أو فسق لكن لا يجب على كل أحد أن يصلي عليه.
منهاح السنة (5/178).
Duk wani Musulmi da ba a san cewa shi Munafuki bane to nema masa gafara ya halasta, da kuma yi masa sallah koda kuwa akwai wani bid'ah ko fasikanci tattare da shi, sai dai bai wajaba akan kowa da yayi masa sallah ba.

Ina jin Sheik Rabee'i Almadkhaly yana da magana irin wannan yace:
أما الترحم على أهل البدع، فإنه يجوز الترحم عليهم، وهذا شيء عليه السلف الصالح ومنهم أحمد بن حنبل، ودل على ذلك نصوص من كتاب الله -تبارك وتعالى- ومن سنة رسول الله عليه الصلاة والسلام، والذي ينازع في هذا جاهل ضال، وصلى الله على نبينا محمد وعلى آله وصحبه وسلم.
شريط بعنوان: لقاء مع الشيخ في مسجد الخير.
Amma nemawa 'yan bid'ah rahama to, lalle ya halasta a nema musu rahama, wannan wani abune da magabata suke kansa, daga cikin su akwai Imam Ahmad dan Hanbal, kuma nassosa daga Littafin Allah da Sunnah sun yi nuni akan hakan, wanda yake jayayya a cikin hakan to shi JAHILI NE BATACCE".

Sbd haka duk wani nassi daga Magabata da yake nuna rashin halascin nemawa 'yan bid'ah gafara da rahama to, za a dauke su ne akan 'yan bid'ah din da bid'ar su ta kai ga kafirci.
Share:

Tuesday, 15 May 2018

Tambaya/Amsa:- Shin ya halasta ayiwa mutum Allurar Zazzabi a lokacin Azumi??


*```Assalamu alaikum*```
*```Malam shin ya halasta ayiwa mutum allurar Zazzabi lokacin da yake azumi? nagode*```


_*AMSA:*_
*******

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،


Ya halatta ga mai azumi ayi masa allura a lokacin da yake azumi da rana.

Amma bai halatta ba ayiwa mutum allurar abinci da rana lokacin da yake azumi. Domin wannan yana daukar hukuncin cin abinci ne da shan abin sha. Yin haka zai zama sanadin karya Azumin Wanda aka yiwa allurar (Allurar abinci ko abinsha). Saboda idan za'ayi allurar da daddare shine mafi a'alaa.

_*(Al-lajnatu al-da'imah lil buhuusil ilmiyyat wal ifta'a, 10/252).*_



والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_

Allah yasa mudace.
Share:

Nasiha:- Babana yace naje wurin dabbobi 4 bayan ya mutu!!! - Dr.jamilu zarewa


*BABANA YA CE NA JE WAJAN DABBOBI GUDA HUDU BAYAN YA MUTU!!!.*

Wani Bawan Allah yayi wa Dansa nasiha da
Da yaje wajen wasu Dabbobi guda (4) Amma kar yaje sai bayan ya mutu!!!.

Dabbobin da ya umarce shi yaje wajen su- sune:-

1- Doki.
2- kiyashi.
3-Maciji.
4-Kare.

Bayan mahaifinsa ya
Rasu sai ya fara zuwa Wajen Doki yace, Baba yace in ya mutu in zo
Wajen ka, Doki yace Baban ka yana da hikima, kasan abinda
Yasa yace kazo
Waje na?

Yace a'a Sai Doki yace kalli inda nake zaune ya
Duba yaga wajen duk ya baci da kashinsa, Ga jikin sa duk datti, Sai yace kalli wancan
Matashin dokin👉🐴
Sai yaga wajensa a share anyi masa Wanka ga ciyawa mai
Kyau da ruwa- a gaban sa, sai Doki yace kaga yanzu ni Na tsufa bani da wani
Amfani shiyasa-aka Kyale ni a wulakance, Shi kuma Matashin
Doki yana da karfin jiki, Ana da bukatarsa shiyasa ake kula dashi dan haka BabanKa yana yi maka Nasiha da ka mori Kuruciyar ka wajen Abinda zai amfane ka,
Domin lafiyar ka da Kuruciyar ka mutane Suke bukata inka Tsufa ba ruwan kowa da kai.

Daga nan sai yaje wajen kiyashi 🐜yai
Masa bayani kamar Yanda yaiwa Doki- kiyashi yace, zo muje sukaje wajen mushan
Kyankyaso, yayi kokarin ya jawo shi shi kadai ya kasa, sai yaje ya kirawo yan'uwan sa, suna zuwa suka janye Shi.
yace Baban ka
Yana nufin komai
Zaka yi ka hada kai Da yan'uwan ka karkayi kai kadai.

Daga nan sai yaje wajen Maciji 🐍 ya Tarad dashi a cikin
Kogo a la6e yace, yanzu ma, yunwa nakeji, da zan futa a ganni
Kashe ni za'a yi, sai Dare yayi sahu ya dauke, nake futa, ba Wani abu, da ya jawo min wannan bakin Jini sai Bakina da
Harshena😛

Babanka yana nufin ka iya
Harshan ka, ka kiyayi barin zance.

Daga nan sai yaje wajen kare🐺 shima
Yai masa bayani, sai yace, zo muje cikin Gari, suna zuwa sai Yara suka fara jifan
Kare, da kyar suka sha, sai kare yaja shi
Wajen mafarauta suna Zuwa sai Suka fara Murna suna kiran sa
Da sunaye kala-kala Wannan ya jefa masa Nama wannan yana Shafa Shi yana Dariya😀😀.
sai kare Yace Baban ka yana
Nufin ka-kasance cikin Wadanda suke sonka Kuma, ake ganin
Mutuncinka, kuma Aka san Darajar ka, Kaga misali a kai na.

Allah yasa mu Amfana.

Ameen ya Allah

*Dr. Jamilu Zarewa*

Allah yabamu ikon Aiki da Abinda muka karanta.
Share:

Saturday, 24 February 2018

AUDIO : Falalar Boye Fushi Daga Sheikh Ja'afar Mahmud Adam Kano


Manzon Allah s.w.a Yana cewa duk wanda yake da damar nuna fushi amma boye  fushi a gobe kiyama Allah zai sashi aljannah yace zabi  wanda kake so a cikin Hurul'ini

Boye fushi kamar sadaki ne na hurul'ini a gobe kiyama.


Manzon Allah yasan abu ne mai matukar wuya mutum yana da damar nuna fushi amma hadiye shi saboda abu ne  mai matukar kuna a wajen hadiyewa balanata yanzu mutum na neman zalunci su kadai balanta an tabashi.

Kaji kamar baka ji ba, ka gani kamar baka gani ba lallai abu ne mai samama mutum daraja a gobe kiyama.

Babu masu boye wannan boye fushi sai masu hakuri da imani.

Ga Audion nan domin saurare

Download Audio here
Share:

Thursday, 22 February 2018

Wanda ya rasa wani Bangare na sallar janaza, ya zaiyi??



*WANDA YA RASA WANI BANGARE NA SALLAR JANAZA, YA ZAI YI?*

*TAMBAYA*
Assalamu alaikum, Allah ya karawa wannan zaure albarka inada tambaya kamar haka shin sallah Jana,iza Ana rama kabbarar da aka rasa, misali kamar idan ba,a Fara sallah da mutum ba har yayi missing din wani bangare daga cikin sallah idan liman ya sallame shima sai yarama.

*AMSA*
Wa alaikumus salaam, Dukkan wanda ya rasa wani bangare na sallan jana'iza zai dauki raka'ar da ya tarar a matsayin raka'ar shi ta farko, idan liman ya idar sai shi ya ciko.

Babban Malami, Sheikh Abdulaziz Bn Baaz, Rahimahullah, ya ce:

*_Sunna ga dukkan mutumin da ya rasa wani bangare na kabbarbari na sallan jana'iza, shi ne ya biya wadannan kabbarbari, saboda fadin Manzon Allah, sallallahu 'alaihi wa sallama: "Idan an tsayar da salla, to ku zo mata kuna tafiya kuma ku kasance masu natsuwa, duk abun da kuka riska ku sallata, abin da kuma ya kubuce muku to ku ciko"..._* A duba مجموع الفتاوى 13/149.

An tambayi Malaman لجنة الدائمة للإفتاء cewa:

Mene ne hukuncin mutumin da ya rasa kabbarori uku a sallan janaza sai ya riski kabbara daya?

Sai suka bayar da amsa da cewa:

*_Zai cike sallan janazan ta yanda zai yi kabbarori uku a matsayin ramuwa kafin a dauke janazar daga inda take..._* a duba fatawa ta 8/399.

Wallahu A'alam.

21/02/2018

Daga: *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*
Share:

Thursday, 11 January 2018

Labari mai girgiza zuciya - Zauren fiqhu

LABARI MAI GIRGIZA ZUCIYA
*******************************
Abdullahi bn Almubarak (rah) yana daga cikin magabata na kwarai, kuma mutum ne Salihi.
Wata shekara bayan yayi niyyar tafiya aikin Hajji, sai ya fita domin yin ban-kwana da abokansa (Almajiransa) kafin tafiyarsa. Amma akan hanyar ne yaga wani abu wanda ya tada masa hankali ya firgitashi.
Ya hangi wata baiwar Allah tana tone juji (bola) tana tonowa wani MUSHEN KAZA wacce aka jefar. Ta daukota ta sanya a Qasan hammatarta, ta juya ta tafi aboye acikin duhu.
Sai yayi kiranta yace "Mai kikieyi ya ke baiwar Allah?!". Sai tace "Ya kai bawan Allah,  kyale halittu da mahaliccinsu. Domin Allah yana da sha'ani acikin lamarin halittunsa".
Sai Ibnul Mubarak yace mata "Ina yi miki magiya don girman Allah ki gaya min labarinki".
Sai matar tace masa "Amma wallahi ba don ka riga kayi mun magiya ba, da ban gaya maka halin da nake ciki ba".
Kafin ta fara gaya masa har hawaye ya fara zuba daga idanunta. Sai tace "Hakika mu Allah ya halatta mana cin mushe. Domin ni Bazawara ce Matalauciya. Kuma (ni) mahaifiyar 'ya'ya mata ne guda hudu".
"Mutuwa ta dauke Mahaifinsu mai kula dasu, Yanayi ya tsananta garemu, kuma dukiya ta Qare daga gareni. Kuma na kwankwasa kofofin mutane (wato na bibbi gidajen jama'a) amma ban samu wata zuciya mai tausayi daga wajensu ba".
"Sai na fita domin nemowa abinci ga 'Ya'yana wadanda wutar yunwa ta riga ta Qone musu hanta. Sai Allah ya azurtani da samun wannan mushen kazar da kake gani. Shin zakayi jayayya dani ne akanta?".
Daga jin wannan labari nan take sai Idanuwan Ibnul Mubarak suka rika zubda hawaye. Sai yace mata "Karbi wannan amanar".
Sai ya damka mata dukkan dunkiyar da yayi niyyar tafiya aikin hajjin nan da ita.
Sai Uwar marayun nan ta karba ta juya wajen 'ya'yanta tana godiya. Shi kuwa Ibnul Mubarak ya juya zuwa gidansa. Alhazai na garinsu kuma suka tafi suka sauke faralinsu sannan suka dawo.
Amma abin mamakin duk da cewar shi bai je aikin Hajji ba, amma duk Alhazan sun dawo suna yin godiya gareshi bisa hidimar da yayi  musu awajen aikin Hajji.
Suan cewa "Allah yaji Qanka Ya Kai Ibnul Mubarak! Babu wani wajen zama da muka zauna fache sai ka bamu wani abu daga ilimin da Allah ya sanar dakai. Kuma bamu ga wanda ya fika wajen bautarka ga Allah Ubangijinka ba, awajen aikin Hajjin nan na wannan shekarar".
Sai Ibnul Mubarak yayi mamaki kuma hankalinsa ya tashi game da al'amarinsa, da kuma al'amarinsu. Shi dai bai bar garinsa ba (ballantana ace har an ganshi awajen aikin Hajji). Kuma shi ba yaso ya bayyanar musu da sirrinsa. (wato ba yaso ya gaya musu cewar yayi sadaqah ne da kudinsa).
To da ya kwanta barci sai yaga wani kyakkyawan mutum wanda haske ke fita daga fuskarsa. Yana ce masa "AMINCIN ALLAH YA TABBATA AGAREKA YA KAI ABDULLAHI. SHIN BAKA SAN KO NI WANENE BA? AI NINE MASOYIN NAN NAKA MUHAMMADUR RASULULLAHI (SAWW) NINE MASOYINKA ADUNIYA DA LAHIRA, KUMA NINE MAI CETONKA ARANAR LAHIRA. ALLAH YA SAKA MAKA DA ALKHAIRI BISA ABINDA KAYI MA AL'UMMATA".
"YA KAI ABDULLAHI 'DAN MUBARAK! HAKIKA ALLAH YA GIRMAMAKA (YAYI MAKA KARAMCI) KAMAR YADDA KA GIRMAMA MAHAIFIYAR MARAYUN NAN. KUMA ALLAH YA RUFA MAKA ASIRI KAMAR YADDA KA RUFA ASIRIN MARAYUN NAN".
"HAKIKA ALLAH MADAUKAKIN SARKI YA HALICCI WANI MALA'IKA NE DA SIFFARKA. YA KASANCE YANA TAFIYA TARE DA ALHAZAN GARINKU AWAJEN GUDANAR DA AYYUKAN HAJJI".
"KUMA HAKIKA ALLAH YA BAMA KOWANNE ALHAJI LADAN AIKIN HAJJI GUDA 'DAYA NE. AMMA KAI KUMA ALLAH YA RUBUTA MAKA LADAN AIKIN HAJJI GUDA SABA'IN!!".
Allahu Akbar!! Ya jama'a kunji fa!!!. Ya ku masu alfahari da yawan aikin Hajji!! (Nayi arfa sau kaza! Naje Umrah sau kaza!! Nayi dawafi sau kaza!!).
In dai yardar Allah kuke nema, ku zagaya gidajen Marayu da Miskinai da Fakirai mana! Zaku samu yardar Allah anan!!
Ka kwashi Matanka da Qananan 'ya'yanka ka tafi dasu Umrah alhali Makwabcinka ko limamin masallacin Unguwarku, ko 'yan uwanka suna kwana da yunwa.. (Wallahi ba lallai ne Allah ya karbi Umrar taku ba).
Wallahi ladan ciyar da Mayunwata guda goma yafi ladan zuwa Umrarka. Wasu daga cikin magabata suna cewa :
"Loma guda daya wacce aka sanya acikin cikin Mayunwaci, tafi alkhairi fiye da gina masallatan juma'a guda dubu".
Ka bar Makobcinka ko 'dan uwanka acikin yunwa da talauci, amma kaje kana LABBAIKAL LAHUMMA LABBAIKA". (Kai kanka kasan Allah ba zai amshi gaisuwarka ba).
Wannan Qissar tana nan acikin Sifatus Safwah na Ibnul Jawzee.
DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990 (10-01-2017).
In sha Allahu daga nan kafin kamawar watan Ramadhan Zauren Fiqhu zai kafa wani bangare mai suna GIDAUNIYAR MARAYU wacce in sha Allahu zamu tara wani abu atsakaninmu domin ciyar da marayu da Miskinai alokacin Azumi. Sannan da kulawa da majinyata marassa galiho. In sha Allahu.
Allah shi taimakemu ameeen.
Share:

Fa'idodin sadaqah - Zauren fiqhu


FA'IDODIN SADAQAH [DAGA ZAUREN FIQHU]
*********************************************
Ya kai 'Dan uwa Musulmi!! Ya ke 'Yar uwa Musulma!! Shin ko kun san cewa sadaqah tana da Mutukar amfani arayuwar 'Dan Adam?
Bari kuji wasu daga cikin fa'idodin dake cikinta :
1. Sadaqah wata Qofa ce daga kofofin samun shiga Aljannah.
2. Acikin dukkan ayyukan lada, Sadaqah tana daga sahun gaba. Kuma mafificiyar sadaqah ita ce "Ciyar da abinci domin Allah".
3. Sadaqah tana inuwantar da Ma'abotanta aranar Alqiyamah, Kuma tana 'Yantar dashi daga shiga Wuta. (Gwargwadon yawan sadaqarka, shine gwargwadon ni'imar da zaka shiga aranar Alqiyamah).
4. Sadaqah tana bushe fushin Ubangiji. (Allah yana son masu yinta, don haka ba zai yi fushi da kai ba).
5. Sadaqah tana kiyaye mutum daga Azabar Qabari.
6. Sadaqah ita ce mafificiyar kyautar da zakayi ma Mamacinka.
7. Sadaqah, Ubangiji ne ke rainonta har sai ranar Alqiyamah za'a nuna maka ladanta.
8. Sadaqah tana tsarkake zuciya daga Qazantar nan ta rowa da kyashi.
9. Sadaqah tana janyo maka soyayyar Allah da soyayyar Mala'ikunsa da Soyayyar bayin Allah.
10. Sadaqah tana janyo maka ninninkuwar ladan ayyukanka.
11. Sadaqah tana janyo maka hasken fuska aranar Alqiyamah.
12. Sadaqah tana janyo maka farin ciki anan duniya da kuma lahira.
13. Sadaqah tana zama dalilin yayewar damuwarka. Kuma tana kiyayeka daga bakin ciki akan abinda ya wuce.
14. Sadaqah tana kiyayeka daga Firgita aranar Alqiyamah.
15. Sadaqah tana janyo kankarewar zunubanka, da kuma gafarar laifukanka.
16. Sadaqah tana janyo ma masu yinta su samu kyakywar cikawa da imani aranar Mutuwarsu.
17. Sadaqah tana sanya Mala'ikun Allah su rika yi maka addu'ar alkhairi.
18. Masu yin sadaqah suna daga cikin mafifitan mutane awajen Allah.
19. Sadaqah tana sanya albarka acikin dukiyarka. Sannan ta tsare dukiyarka daga kowacce irin asara.
20. Sadaqah tana da albarka. Kuma da wanda ya fitar, da wanda aka wakilta ya bayar, da wanda ya mika, da wanda ya rarraba duk suna cikin ladanta.
21. Ma'abocin yawaita sadaqah, yana da alkawarin samun lada mai yawa tare da babban sakamako awajen Ubangijinsa.
22. Yana daga cikin siffofin masu tsoron Allah, zaka iske suna ciyar da dukiyarsu domin Allah,
23. Sadaqah tana daga cikin manyan alamomin Kyauta da karamci.
24. Sadaqah babbar dalili ce wajen samun karbuwar addu'o'inka, da yayewar bakin cikinka.
25. Sadaqah tana kiyaye masu yinta daga afkawa cikin bala'i.
26. Sadaqah sau daya (in dai an yita domin Allah) tana toshewa kofofi saba'in na Musibu da miyagun abubuwa tun anan duniya.
27. Sadaqah tana Qara maka tsawon rai da albarkar rayuwa da albarkar dukiya.
28. Sadaqah tana janyo maka samun nasara tare da taimakon Ubangiji acikin dukkan abinda kasa agabanka.
29. Sadaqah tana sanyawa ka samu gagarumar nasara akan Maqiyanka da mahassadanka. Kuma kaidinsu ba zai cuceka ba.
30. Idan wani ciwo yana damunka har ka rasa maganinsa, to yawaita sadaqah. In sha Allah ita Sadaqah magani ce, waraka ce, kuma kariya ce daga dukkan cututtuka.
31. Sadaqah garkuwa ce daga sharrin 'barayi, ko gobara, kuma tana kiyaye masu yinta daga mummunar cikawa.
32. Sadaqah ladanta yana tabbatuwa awajen Allah. Koda dabbobi kayi wa sadaqar, ko tsuntsaye, ko Qwaruka.
33. Babbar sadaqar da zaka fara gabatarwa ayanzu, ita ce kayi "sharing" (wato ya'da) wannan rubutun daga Zauren Fiqhu ba tare da goge koda harafi guda daga ciki ba.
Idan kayi haka da niyyar sadaqah, to duk wanda ya gani ya karanta kaima kana da lada akansa.
An gabatar da karatun ne a ZAUREN FIQHU WHATSAPP (31-12-2016).
Share:

Dausayin iyali 002 - Dr.Mansur Ibrahim Sokoto


*DAUSAYIN IYALI 002*
Matsayin Mata da Hakkokinsu a Musulunci
Littafin *Dr. Mansur Sokoto*
Matsayin Mata Kafin Zuwan Musulunci
Abu ne da tarihi ya tabbatar cewa, Macce ba a dauke ta a matsayin
kammalallen dan Adam ba kafin zuwan Musulunci. Domin kuwa an
mayar da ita kamar Haja wacce ake saye kuma ake sayarwa, ake kuma
gadon ta kamar yadda ake gadon gida ko gona ko duk wata kaddara
da Namiji ya mutu ya bar ta. Akan umurci Macce ta yi Zina don ta kawo
kudi, kuma ana aurar da ita ne yadda aka ga dama, ba tare da neman
zabinta ko ma shawartar ta ba.
A da Namiji yakan auri ko Mata nawa yake so kuma ya ga dama kamar
yadda yake iya mallakar riga da hula ko nawa yake so.
A wasu sassan duniya ba a yarda Macce mutum ce ba ma sam. Misali,
a qasar Rasha Malaman addini sun ba da fatawar cewa, Macce najasa
ce, matsayinta daya ne da na Kare.
A yankin Larabawa, zamanin Jahiliyya, uba yakan sayar da diyarsa.
Yakan kuma rufe ta cikin qasa babu gaira babu dalili. Kawai dai
haifuwar ta ba abin farin ciki ba ne balle ai alfahari. Budurwa tana goge
gumi daga fuskar babanta a lokacin da yake haqa ramin rufe ta, amma
ita ba ta sani ba.
Kashe Macce - kafin zuwan Musulunci - ba wani babban laifi ba ne da
har za ayi maganar Qisasi ko Diyya a kan sa.
A qasar Indiya akan qone Macce ne tare da mijinta idan ya mutu,
alhalin tana da ranta da lafiyarta. Wannan ya sa sau da yawa Macce
takan kashe kanta bayan mutuwar mijinta irin mutuwar da take ganin
ta fi mata sauqi, don kauce ma wannan baqar mutuwa da mummunan
bala'i.
Malaman addinai biyu da ake a da su a lokacin wadan da suka samo
koyarwarsu daga manyan Annabawa ba su tabuka komai a kan wannan
- Yahudawa - mabiyan Addinin Annabi Musa Alaihis Salam sun dauki
Macce a matsayin najasa duk lokacin da take Haila. Ba za su ci abincin
da ta dafa ba, ba kuma za su kusance ta ba. A maimakon haka sai su
kafa ma ta rumfa a bayan gida - kamar yadda ake turke Akuya - su riqa
ba ta ruwa da gurasa har sai lokacin da ta gama al'ada sannan ta dawo
cikin gida.
- Su kuma Kiristoci duk da ba su nuna qyamar ta a wannan lokaci.
Kuma ma har saduwa suke yi da ita a lokacin da take Haila. Amma ba
za mu dauka cewa sun mutunta ta ba tun da yake suna kallon ta a
matsayin ita ce ummul-haba'isin duk wani laifi da sharri da cuta da ake
yi a duniya. Kuma wai, ita ce qofar shiga wuta. Suna kafa hujja da
cewa, wai, ita ce ta bai wa Annabi Adam (Alaihis Salam) shawarar cin
bishiyar da Allah ya hana shi har ta jawo ma su uqubar fita daga gidan
aljanna.
*Kusaurari cigaba da izinin Allah*
Gabatarwa a social Media
*Ibrahim Nasidi Baban Ilham*
Share:

Dausayin iyali 004 - Dr.Mansur Ibrahim Sokoto



*DAUSAYIN IYALI 004*
Matsayin Mata da Hakkokinsu a Musulinci
Littafin *Dr. Mansur Sokoto*
Kai, wace daraja muke nema ma Macce bayan abinda kowa ya sani a
tarihi ne, Macce guda daya ce ta yi sa’ayi tsakanin Safa da Marwa tana
nemar ma danta ruwan sha, amma Shari’ar Musulunci ta mayar da
wannan sa’ayin nata a matsayin wani rukuni daga cikin rukunan
Musulunci shi ne aikin Hajji? Tare da haka aka yafe wa Mata yin
Sa’ayin, aka ce Maza kawai za su yi. Kamar yadda aka yafe ma wani
mutum zuwa Jihadi saboda ya raka matarsa wurin aikin Hajji. Sahih Al￾Bukhari (3006) da Sahih Muslim (1344).
Kula da iyali, da ciyar da su abinci, yana da wani gurbi na musamman
wanda ya zarce na sauran wasu ayyuka na neman lada da neman
shiga aljanna. Ban da wannan ma, kasancewa tare da su, da faranta
ransu ta hanyar rashin yin nisa da su, shi ma abu ne mai girman lada.
Mu dubi girman ladar kasancewa a birnin Makka da yin salloli masu
ninkin daraja da lada a cikin ta, amma duk da haka Annabi Sallallahu
Alaihi wa Sallam yake cewa: “Idan dayanku ya kammala aikin Hajjinsa,
to ya gaggauta komawa gida wajen iyalansa. Domin wannan ya fi
girman lada a gare shi”. Sahih al-Jami’ (732)
*Kusaurari cigaba da izinin Allah*
Gabatarwa a social media
*Ibrahim Nasidi Baban Ilham*.
Share:

Archive

Unordered List

Support