Dausayin iyali 004 - Dr.Mansur Ibrahim Sokoto ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Thursday 11 January 2018

Dausayin iyali 004 - Dr.Mansur Ibrahim Sokoto



*DAUSAYIN IYALI 004*
Matsayin Mata da Hakkokinsu a Musulinci
Littafin *Dr. Mansur Sokoto*
Kai, wace daraja muke nema ma Macce bayan abinda kowa ya sani a
tarihi ne, Macce guda daya ce ta yi sa’ayi tsakanin Safa da Marwa tana
nemar ma danta ruwan sha, amma Shari’ar Musulunci ta mayar da
wannan sa’ayin nata a matsayin wani rukuni daga cikin rukunan
Musulunci shi ne aikin Hajji? Tare da haka aka yafe wa Mata yin
Sa’ayin, aka ce Maza kawai za su yi. Kamar yadda aka yafe ma wani
mutum zuwa Jihadi saboda ya raka matarsa wurin aikin Hajji. Sahih Al￾Bukhari (3006) da Sahih Muslim (1344).
Kula da iyali, da ciyar da su abinci, yana da wani gurbi na musamman
wanda ya zarce na sauran wasu ayyuka na neman lada da neman
shiga aljanna. Ban da wannan ma, kasancewa tare da su, da faranta
ransu ta hanyar rashin yin nisa da su, shi ma abu ne mai girman lada.
Mu dubi girman ladar kasancewa a birnin Makka da yin salloli masu
ninkin daraja da lada a cikin ta, amma duk da haka Annabi Sallallahu
Alaihi wa Sallam yake cewa: “Idan dayanku ya kammala aikin Hajjinsa,
to ya gaggauta komawa gida wajen iyalansa. Domin wannan ya fi
girman lada a gare shi”. Sahih al-Jami’ (732)
*Kusaurari cigaba da izinin Allah*
Gabatarwa a social media
*Ibrahim Nasidi Baban Ilham*.
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support