Nasiha:- Babana yace naje wurin dabbobi 4 bayan ya mutu!!! - Dr.jamilu zarewa ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 15 May 2018

Nasiha:- Babana yace naje wurin dabbobi 4 bayan ya mutu!!! - Dr.jamilu zarewa


*BABANA YA CE NA JE WAJAN DABBOBI GUDA HUDU BAYAN YA MUTU!!!.*

Wani Bawan Allah yayi wa Dansa nasiha da
Da yaje wajen wasu Dabbobi guda (4) Amma kar yaje sai bayan ya mutu!!!.

Dabbobin da ya umarce shi yaje wajen su- sune:-

1- Doki.
2- kiyashi.
3-Maciji.
4-Kare.

Bayan mahaifinsa ya
Rasu sai ya fara zuwa Wajen Doki yace, Baba yace in ya mutu in zo
Wajen ka, Doki yace Baban ka yana da hikima, kasan abinda
Yasa yace kazo
Waje na?

Yace a'a Sai Doki yace kalli inda nake zaune ya
Duba yaga wajen duk ya baci da kashinsa, Ga jikin sa duk datti, Sai yace kalli wancan
Matashin dokin👉🐴
Sai yaga wajensa a share anyi masa Wanka ga ciyawa mai
Kyau da ruwa- a gaban sa, sai Doki yace kaga yanzu ni Na tsufa bani da wani
Amfani shiyasa-aka Kyale ni a wulakance, Shi kuma Matashin
Doki yana da karfin jiki, Ana da bukatarsa shiyasa ake kula dashi dan haka BabanKa yana yi maka Nasiha da ka mori Kuruciyar ka wajen Abinda zai amfane ka,
Domin lafiyar ka da Kuruciyar ka mutane Suke bukata inka Tsufa ba ruwan kowa da kai.

Daga nan sai yaje wajen kiyashi 🐜yai
Masa bayani kamar Yanda yaiwa Doki- kiyashi yace, zo muje sukaje wajen mushan
Kyankyaso, yayi kokarin ya jawo shi shi kadai ya kasa, sai yaje ya kirawo yan'uwan sa, suna zuwa suka janye Shi.
yace Baban ka
Yana nufin komai
Zaka yi ka hada kai Da yan'uwan ka karkayi kai kadai.

Daga nan sai yaje wajen Maciji 🐍 ya Tarad dashi a cikin
Kogo a la6e yace, yanzu ma, yunwa nakeji, da zan futa a ganni
Kashe ni za'a yi, sai Dare yayi sahu ya dauke, nake futa, ba Wani abu, da ya jawo min wannan bakin Jini sai Bakina da
Harshena😛

Babanka yana nufin ka iya
Harshan ka, ka kiyayi barin zance.

Daga nan sai yaje wajen kare🐺 shima
Yai masa bayani, sai yace, zo muje cikin Gari, suna zuwa sai Yara suka fara jifan
Kare, da kyar suka sha, sai kare yaja shi
Wajen mafarauta suna Zuwa sai Suka fara Murna suna kiran sa
Da sunaye kala-kala Wannan ya jefa masa Nama wannan yana Shafa Shi yana Dariya😀😀.
sai kare Yace Baban ka yana
Nufin ka-kasance cikin Wadanda suke sonka Kuma, ake ganin
Mutuncinka, kuma Aka san Darajar ka, Kaga misali a kai na.

Allah yasa mu Amfana.

Ameen ya Allah

*Dr. Jamilu Zarewa*

Allah yabamu ikon Aiki da Abinda muka karanta.
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support