Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Thursday, 11 January 2018

Labari mai girgiza zuciya - Zauren fiqhu

LABARI MAI GIRGIZA ZUCIYA
*******************************
Abdullahi bn Almubarak (rah) yana daga cikin magabata na kwarai, kuma mutum ne Salihi.
Wata shekara bayan yayi niyyar tafiya aikin Hajji, sai ya fita domin yin ban-kwana da abokansa (Almajiransa) kafin tafiyarsa. Amma akan hanyar ne yaga wani abu wanda ya tada masa hankali ya firgitashi.
Ya hangi wata baiwar Allah tana tone juji (bola) tana tonowa wani MUSHEN KAZA wacce aka jefar. Ta daukota ta sanya a Qasan hammatarta, ta juya ta tafi aboye acikin duhu.
Sai yayi kiranta yace "Mai kikieyi ya ke baiwar Allah?!". Sai tace "Ya kai bawan Allah,  kyale halittu da mahaliccinsu. Domin Allah yana da sha'ani acikin lamarin halittunsa".
Sai Ibnul Mubarak yace mata "Ina yi miki magiya don girman Allah ki gaya min labarinki".
Sai matar tace masa "Amma wallahi ba don ka riga kayi mun magiya ba, da ban gaya maka halin da nake ciki ba".
Kafin ta fara gaya masa har hawaye ya fara zuba daga idanunta. Sai tace "Hakika mu Allah ya halatta mana cin mushe. Domin ni Bazawara ce Matalauciya. Kuma (ni) mahaifiyar 'ya'ya mata ne guda hudu".
"Mutuwa ta dauke Mahaifinsu mai kula dasu, Yanayi ya tsananta garemu, kuma dukiya ta Qare daga gareni. Kuma na kwankwasa kofofin mutane (wato na bibbi gidajen jama'a) amma ban samu wata zuciya mai tausayi daga wajensu ba".
"Sai na fita domin nemowa abinci ga 'Ya'yana wadanda wutar yunwa ta riga ta Qone musu hanta. Sai Allah ya azurtani da samun wannan mushen kazar da kake gani. Shin zakayi jayayya dani ne akanta?".
Daga jin wannan labari nan take sai Idanuwan Ibnul Mubarak suka rika zubda hawaye. Sai yace mata "Karbi wannan amanar".
Sai ya damka mata dukkan dunkiyar da yayi niyyar tafiya aikin hajjin nan da ita.
Sai Uwar marayun nan ta karba ta juya wajen 'ya'yanta tana godiya. Shi kuwa Ibnul Mubarak ya juya zuwa gidansa. Alhazai na garinsu kuma suka tafi suka sauke faralinsu sannan suka dawo.
Amma abin mamakin duk da cewar shi bai je aikin Hajji ba, amma duk Alhazan sun dawo suna yin godiya gareshi bisa hidimar da yayi  musu awajen aikin Hajji.
Suan cewa "Allah yaji Qanka Ya Kai Ibnul Mubarak! Babu wani wajen zama da muka zauna fache sai ka bamu wani abu daga ilimin da Allah ya sanar dakai. Kuma bamu ga wanda ya fika wajen bautarka ga Allah Ubangijinka ba, awajen aikin Hajjin nan na wannan shekarar".
Sai Ibnul Mubarak yayi mamaki kuma hankalinsa ya tashi game da al'amarinsa, da kuma al'amarinsu. Shi dai bai bar garinsa ba (ballantana ace har an ganshi awajen aikin Hajji). Kuma shi ba yaso ya bayyanar musu da sirrinsa. (wato ba yaso ya gaya musu cewar yayi sadaqah ne da kudinsa).
To da ya kwanta barci sai yaga wani kyakkyawan mutum wanda haske ke fita daga fuskarsa. Yana ce masa "AMINCIN ALLAH YA TABBATA AGAREKA YA KAI ABDULLAHI. SHIN BAKA SAN KO NI WANENE BA? AI NINE MASOYIN NAN NAKA MUHAMMADUR RASULULLAHI (SAWW) NINE MASOYINKA ADUNIYA DA LAHIRA, KUMA NINE MAI CETONKA ARANAR LAHIRA. ALLAH YA SAKA MAKA DA ALKHAIRI BISA ABINDA KAYI MA AL'UMMATA".
"YA KAI ABDULLAHI 'DAN MUBARAK! HAKIKA ALLAH YA GIRMAMAKA (YAYI MAKA KARAMCI) KAMAR YADDA KA GIRMAMA MAHAIFIYAR MARAYUN NAN. KUMA ALLAH YA RUFA MAKA ASIRI KAMAR YADDA KA RUFA ASIRIN MARAYUN NAN".
"HAKIKA ALLAH MADAUKAKIN SARKI YA HALICCI WANI MALA'IKA NE DA SIFFARKA. YA KASANCE YANA TAFIYA TARE DA ALHAZAN GARINKU AWAJEN GUDANAR DA AYYUKAN HAJJI".
"KUMA HAKIKA ALLAH YA BAMA KOWANNE ALHAJI LADAN AIKIN HAJJI GUDA 'DAYA NE. AMMA KAI KUMA ALLAH YA RUBUTA MAKA LADAN AIKIN HAJJI GUDA SABA'IN!!".
Allahu Akbar!! Ya jama'a kunji fa!!!. Ya ku masu alfahari da yawan aikin Hajji!! (Nayi arfa sau kaza! Naje Umrah sau kaza!! Nayi dawafi sau kaza!!).
In dai yardar Allah kuke nema, ku zagaya gidajen Marayu da Miskinai da Fakirai mana! Zaku samu yardar Allah anan!!
Ka kwashi Matanka da Qananan 'ya'yanka ka tafi dasu Umrah alhali Makwabcinka ko limamin masallacin Unguwarku, ko 'yan uwanka suna kwana da yunwa.. (Wallahi ba lallai ne Allah ya karbi Umrar taku ba).
Wallahi ladan ciyar da Mayunwata guda goma yafi ladan zuwa Umrarka. Wasu daga cikin magabata suna cewa :
"Loma guda daya wacce aka sanya acikin cikin Mayunwaci, tafi alkhairi fiye da gina masallatan juma'a guda dubu".
Ka bar Makobcinka ko 'dan uwanka acikin yunwa da talauci, amma kaje kana LABBAIKAL LAHUMMA LABBAIKA". (Kai kanka kasan Allah ba zai amshi gaisuwarka ba).
Wannan Qissar tana nan acikin Sifatus Safwah na Ibnul Jawzee.
DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990 (10-01-2017).
In sha Allahu daga nan kafin kamawar watan Ramadhan Zauren Fiqhu zai kafa wani bangare mai suna GIDAUNIYAR MARAYU wacce in sha Allahu zamu tara wani abu atsakaninmu domin ciyar da marayu da Miskinai alokacin Azumi. Sannan da kulawa da majinyata marassa galiho. In sha Allahu.
Allah shi taimakemu ameeen.
Share:

Fa'idodin sadaqah - Zauren fiqhu


FA'IDODIN SADAQAH [DAGA ZAUREN FIQHU]
*********************************************
Ya kai 'Dan uwa Musulmi!! Ya ke 'Yar uwa Musulma!! Shin ko kun san cewa sadaqah tana da Mutukar amfani arayuwar 'Dan Adam?
Bari kuji wasu daga cikin fa'idodin dake cikinta :
1. Sadaqah wata Qofa ce daga kofofin samun shiga Aljannah.
2. Acikin dukkan ayyukan lada, Sadaqah tana daga sahun gaba. Kuma mafificiyar sadaqah ita ce "Ciyar da abinci domin Allah".
3. Sadaqah tana inuwantar da Ma'abotanta aranar Alqiyamah, Kuma tana 'Yantar dashi daga shiga Wuta. (Gwargwadon yawan sadaqarka, shine gwargwadon ni'imar da zaka shiga aranar Alqiyamah).
4. Sadaqah tana bushe fushin Ubangiji. (Allah yana son masu yinta, don haka ba zai yi fushi da kai ba).
5. Sadaqah tana kiyaye mutum daga Azabar Qabari.
6. Sadaqah ita ce mafificiyar kyautar da zakayi ma Mamacinka.
7. Sadaqah, Ubangiji ne ke rainonta har sai ranar Alqiyamah za'a nuna maka ladanta.
8. Sadaqah tana tsarkake zuciya daga Qazantar nan ta rowa da kyashi.
9. Sadaqah tana janyo maka soyayyar Allah da soyayyar Mala'ikunsa da Soyayyar bayin Allah.
10. Sadaqah tana janyo maka ninninkuwar ladan ayyukanka.
11. Sadaqah tana janyo maka hasken fuska aranar Alqiyamah.
12. Sadaqah tana janyo maka farin ciki anan duniya da kuma lahira.
13. Sadaqah tana zama dalilin yayewar damuwarka. Kuma tana kiyayeka daga bakin ciki akan abinda ya wuce.
14. Sadaqah tana kiyayeka daga Firgita aranar Alqiyamah.
15. Sadaqah tana janyo kankarewar zunubanka, da kuma gafarar laifukanka.
16. Sadaqah tana janyo ma masu yinta su samu kyakywar cikawa da imani aranar Mutuwarsu.
17. Sadaqah tana sanya Mala'ikun Allah su rika yi maka addu'ar alkhairi.
18. Masu yin sadaqah suna daga cikin mafifitan mutane awajen Allah.
19. Sadaqah tana sanya albarka acikin dukiyarka. Sannan ta tsare dukiyarka daga kowacce irin asara.
20. Sadaqah tana da albarka. Kuma da wanda ya fitar, da wanda aka wakilta ya bayar, da wanda ya mika, da wanda ya rarraba duk suna cikin ladanta.
21. Ma'abocin yawaita sadaqah, yana da alkawarin samun lada mai yawa tare da babban sakamako awajen Ubangijinsa.
22. Yana daga cikin siffofin masu tsoron Allah, zaka iske suna ciyar da dukiyarsu domin Allah,
23. Sadaqah tana daga cikin manyan alamomin Kyauta da karamci.
24. Sadaqah babbar dalili ce wajen samun karbuwar addu'o'inka, da yayewar bakin cikinka.
25. Sadaqah tana kiyaye masu yinta daga afkawa cikin bala'i.
26. Sadaqah sau daya (in dai an yita domin Allah) tana toshewa kofofi saba'in na Musibu da miyagun abubuwa tun anan duniya.
27. Sadaqah tana Qara maka tsawon rai da albarkar rayuwa da albarkar dukiya.
28. Sadaqah tana janyo maka samun nasara tare da taimakon Ubangiji acikin dukkan abinda kasa agabanka.
29. Sadaqah tana sanyawa ka samu gagarumar nasara akan Maqiyanka da mahassadanka. Kuma kaidinsu ba zai cuceka ba.
30. Idan wani ciwo yana damunka har ka rasa maganinsa, to yawaita sadaqah. In sha Allah ita Sadaqah magani ce, waraka ce, kuma kariya ce daga dukkan cututtuka.
31. Sadaqah garkuwa ce daga sharrin 'barayi, ko gobara, kuma tana kiyaye masu yinta daga mummunar cikawa.
32. Sadaqah ladanta yana tabbatuwa awajen Allah. Koda dabbobi kayi wa sadaqar, ko tsuntsaye, ko Qwaruka.
33. Babbar sadaqar da zaka fara gabatarwa ayanzu, ita ce kayi "sharing" (wato ya'da) wannan rubutun daga Zauren Fiqhu ba tare da goge koda harafi guda daga ciki ba.
Idan kayi haka da niyyar sadaqah, to duk wanda ya gani ya karanta kaima kana da lada akansa.
An gabatar da karatun ne a ZAUREN FIQHU WHATSAPP (31-12-2016).
Share:

Dausayin iyali 002 - Dr.Mansur Ibrahim Sokoto


*DAUSAYIN IYALI 002*
Matsayin Mata da Hakkokinsu a Musulunci
Littafin *Dr. Mansur Sokoto*
Matsayin Mata Kafin Zuwan Musulunci
Abu ne da tarihi ya tabbatar cewa, Macce ba a dauke ta a matsayin
kammalallen dan Adam ba kafin zuwan Musulunci. Domin kuwa an
mayar da ita kamar Haja wacce ake saye kuma ake sayarwa, ake kuma
gadon ta kamar yadda ake gadon gida ko gona ko duk wata kaddara
da Namiji ya mutu ya bar ta. Akan umurci Macce ta yi Zina don ta kawo
kudi, kuma ana aurar da ita ne yadda aka ga dama, ba tare da neman
zabinta ko ma shawartar ta ba.
A da Namiji yakan auri ko Mata nawa yake so kuma ya ga dama kamar
yadda yake iya mallakar riga da hula ko nawa yake so.
A wasu sassan duniya ba a yarda Macce mutum ce ba ma sam. Misali,
a qasar Rasha Malaman addini sun ba da fatawar cewa, Macce najasa
ce, matsayinta daya ne da na Kare.
A yankin Larabawa, zamanin Jahiliyya, uba yakan sayar da diyarsa.
Yakan kuma rufe ta cikin qasa babu gaira babu dalili. Kawai dai
haifuwar ta ba abin farin ciki ba ne balle ai alfahari. Budurwa tana goge
gumi daga fuskar babanta a lokacin da yake haqa ramin rufe ta, amma
ita ba ta sani ba.
Kashe Macce - kafin zuwan Musulunci - ba wani babban laifi ba ne da
har za ayi maganar Qisasi ko Diyya a kan sa.
A qasar Indiya akan qone Macce ne tare da mijinta idan ya mutu,
alhalin tana da ranta da lafiyarta. Wannan ya sa sau da yawa Macce
takan kashe kanta bayan mutuwar mijinta irin mutuwar da take ganin
ta fi mata sauqi, don kauce ma wannan baqar mutuwa da mummunan
bala'i.
Malaman addinai biyu da ake a da su a lokacin wadan da suka samo
koyarwarsu daga manyan Annabawa ba su tabuka komai a kan wannan
- Yahudawa - mabiyan Addinin Annabi Musa Alaihis Salam sun dauki
Macce a matsayin najasa duk lokacin da take Haila. Ba za su ci abincin
da ta dafa ba, ba kuma za su kusance ta ba. A maimakon haka sai su
kafa ma ta rumfa a bayan gida - kamar yadda ake turke Akuya - su riqa
ba ta ruwa da gurasa har sai lokacin da ta gama al'ada sannan ta dawo
cikin gida.
- Su kuma Kiristoci duk da ba su nuna qyamar ta a wannan lokaci.
Kuma ma har saduwa suke yi da ita a lokacin da take Haila. Amma ba
za mu dauka cewa sun mutunta ta ba tun da yake suna kallon ta a
matsayin ita ce ummul-haba'isin duk wani laifi da sharri da cuta da ake
yi a duniya. Kuma wai, ita ce qofar shiga wuta. Suna kafa hujja da
cewa, wai, ita ce ta bai wa Annabi Adam (Alaihis Salam) shawarar cin
bishiyar da Allah ya hana shi har ta jawo ma su uqubar fita daga gidan
aljanna.
*Kusaurari cigaba da izinin Allah*
Gabatarwa a social Media
*Ibrahim Nasidi Baban Ilham*
Share:

Dausayin iyali 004 - Dr.Mansur Ibrahim Sokoto



*DAUSAYIN IYALI 004*
Matsayin Mata da Hakkokinsu a Musulinci
Littafin *Dr. Mansur Sokoto*
Kai, wace daraja muke nema ma Macce bayan abinda kowa ya sani a
tarihi ne, Macce guda daya ce ta yi sa’ayi tsakanin Safa da Marwa tana
nemar ma danta ruwan sha, amma Shari’ar Musulunci ta mayar da
wannan sa’ayin nata a matsayin wani rukuni daga cikin rukunan
Musulunci shi ne aikin Hajji? Tare da haka aka yafe wa Mata yin
Sa’ayin, aka ce Maza kawai za su yi. Kamar yadda aka yafe ma wani
mutum zuwa Jihadi saboda ya raka matarsa wurin aikin Hajji. Sahih Al￾Bukhari (3006) da Sahih Muslim (1344).
Kula da iyali, da ciyar da su abinci, yana da wani gurbi na musamman
wanda ya zarce na sauran wasu ayyuka na neman lada da neman
shiga aljanna. Ban da wannan ma, kasancewa tare da su, da faranta
ransu ta hanyar rashin yin nisa da su, shi ma abu ne mai girman lada.
Mu dubi girman ladar kasancewa a birnin Makka da yin salloli masu
ninkin daraja da lada a cikin ta, amma duk da haka Annabi Sallallahu
Alaihi wa Sallam yake cewa: “Idan dayanku ya kammala aikin Hajjinsa,
to ya gaggauta komawa gida wajen iyalansa. Domin wannan ya fi
girman lada a gare shi”. Sahih al-Jami’ (732)
*Kusaurari cigaba da izinin Allah*
Gabatarwa a social media
*Ibrahim Nasidi Baban Ilham*.
Share:

Dausayin iyali 003 - Dr.mansur ibrahim sokoto


*DAUSAYIN IYALI 003*
Matsayin Mata da Hakkokinsu a Musulunci
Littafin *Dr. Mansur Sokoto*
*Macce 'Yar Gatan Musulunci*
Addinin Musulunci shi ne ya qwato ma Macce dukkan haqqoqinta, ya
hana a zalunce ta, ya tabbatar mata da mutuntaka da daraja, ya sanya
mata rabo a cikin gado, ya ce duk aikin lada idan ta yi shi tana da lada
kamar Namiji.
Har a mintunansa na qarshe a duniya, Manzon Allah Sallallahu Alaihi
wa Sallam ya kasance yana wasici ga al'ummarsa da su kula da
haqqen Mata. Yana cewa:

""استوصو"ا بالنساء خيرا"
“Ina umurnin ku da ku kyautata kula da mata”. Sahih Al-Bukhari
(5185).
A musulunci, da zaran ka haifi 'ya Macce to ka samu wani babban
dalilin shiga aljanna. To ballai kuma wanda ya samu biyu.
Hadisi ya zo a cikin Sahih Al-Bukhari daga uwar Mummunai A’isha
Radhiyallahu Anha tana ba da labarin wata baquwa da ta zo bara a
gidanta tana neman abin da za ta jefa a bakin salati. Tare da ita akwai
yara tagwaye guda biyu. Sai ta dauko dabino qwara daya ta ba ta. Sai
matar ta raba dabinon biyu ta ba ‘yan tagwayenta. Wannan abin ya ba
ni sha’awa, har na fada ma Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam. In
ji ta. Sai ya ce,”Ai duk wanda Allah ya jarabce shi da ‘ya’ya mata ko
kadan ne kuma ya kyautata ma su, za su zamo ma sa kariya daga
shiga wuta”. Sahih Al-Bukhari (1418) da Sahih Muslim (2629).
A daya Hadisin na cikin Sahihu Muslim daga Anas Radhiyallahu Anhu
Annabi Sallallahu Alaihi wa Sallam cewa ya yi: “Wanda ya kula da
‘ya’ya mata biyu har suka balaga zai zo a ranar Alqiyama muna tare
da shi kamar haka”. Sai ya gwama yatsunsa wuri daya.
Wannan a matakin farko na haifuwar Macce da rainon ta kenan. Idan ta
girma aka yi ma ta aure Musulunci ya ce, ita ce ta kammala rabin addinin mijinta. Idan kuwa ta haifu sai aka ce aljannar ‘ya’yanta na
qarqashin qafafunta. A nan ba ina nuni ne da Hadisin da aka sani sosai
ba, shi ne: “Aljanna tana qarqashin qafafun iyaye Mata”.
Wannan Hadisi da'ifi ne, kuma ma babu shi a littafan Hadisi sai dai na
Tarihi irin su "Al-Kamil" na Ibnu Adiy, da na Uqaili. Amma akwai Hadisin
Mu'awiya bn Jaahimata wanda Imam An-Nasa'i da Hakim suka ruwaito
cewa, wani mutum ya zo wurin Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa
Sallam yana neman izininsa don ya tafi Jihadi. Sai Annabi Sallallahu
Alaihi wa Sallam ya tambaye shi, ko mahaifiyarka tana raye? Ya amsa
ma sa, eh. Sai ya ce:
"To, ka lizimce ta. Domin Aljanna na qarqashin qafafunta".
Wannan kam ingantaccen Hadisi ne babu tantama. Imam Nasa’i (2/54)
da Hakim (4/151) da dabarani (1/225) duk sun fitar da shi. Kuma
Hakim da Dhahabi da Mundhiri (3/214) duk sun inganta shi. A
ma’anarsa kuma ba shi da banbanci da wancan.
Hadisin da ya fi wannan inganci shi ne wanda ya ce, uwa Macce tana
da haqqoqi uku, a lokacin da uba Namiji yake da haqqi guda daya. Ga
yadda Hadisinyake: Wani mutum ya zo wurin Manzon Allah Sallallahu
Alaihi wa Sallam sai ya tambaye shi, wa ya fi dacewa a duniya in
kyautata ma? Sallallahu Alaihi wa Sallam ya ce,”Mahaifiyarka”. Ya ce,
sai kuma wa ye? Ya ce,”Mahaifiyarka”. Ya sake tambaya, sannan wa?
Ya ce, ”Mahaifiyarka”. Sai kuma wa? Sallallahu Alaihi wa Sallam ya ce,
“Sannan Mahaifinka”. Sahih Al-Bukhari (5626).
Kai, wace daraja muke nema ma Macce bayan abinda kowa ya sani a
tarihi ne, Macce guda daya ce ta yi sa’ayi tsakanin Safa da Marwa tana
nemar ma danta ruwan sha, amma Shari’ar Musulunci ta mayar da
wannan sa’ayin nata a matsayin wani rukuni daga cikin rukunan
Musulunci shi ne aikin Hajji? Tare da haka aka yafe wa Mata yin
Sa’ayin, aka ce Maza kawai za su yi. Kamar yadda aka yafe ma wani
mutum zuwa Jihadi saboda ya raka matarsa wurin aikin Hajji. Sahih Al￾Bukhari (3006) da Sahih Muslim (1344).
*Kusaurari cigaba da izinin Allah*
Gabatarwa a social media
*Ibrahim Nasidi Baban Ilham*
Share:

Monday, 8 January 2018

Alkaki da Ruwan Zuma - Dr.mansur ibrahim sokoto



ALKAKI DA RUWAN ZUMA

Fitowa ta 001

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinqai
Godiya ta tabbata ga Allah. Tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta.
Gabatarwa
Da yawa daga cikin mutane suna tsammanin malaman Sunna da suka ce
a kame baki daga kutsawa a cikin rikittan da suka faru a tsakanin iyayenmu
Musulmin farko sun faxi haka ne don suna son a voye gaskiya. Wannan kuwa
kuskure ne babba.
Tarihin magabata, musamman ma dai almajiran Manzon Allah Sallallahu
Alaihi wa Sallam na da banbanci da sauran tarihin mutane baki xaya. Dalili kuwa
shi ne, ba zaka iya raba tarihinsu ba da na maigidansu wanda shi ne Allah ya
xora ma alhakin tarbiyyar su da shiryar da su zuwa ga gaskiya.
Dalili na biyu kuma shi ne kasancewar su mutanen da Allah ya zava kuma
ya fifita su albarkacin zamowar su tare da amintaccen Allah; masu ba shi
shawara, masu taimakon sa, masu bin sa sallah, masu ba shi zakka, masu
tanyon sa jihadi, masu ba shi aure, masu maqwautaka da shi, kuma waxanda
tarihi ya tabbatar sun fifita shi a kan kowa da kowa. Kai, har ma sun kashe
iyayensu da danginsu a wajen kariyar sa. Haka ma duk abin da suka mallaka na
duniya sun sadaukar da shi domin wannan farin masoyi da basu tava haxa kowa
da shi ba.
Wannan magana ba na-ji-na-ji ba ce, maganar Allah ce. Mutum har ya kan
yi mamakin irin yadda wannan lamari zai shige ma wasu duhu alhalin ga shi nan
varo varo a wurare cikin Alqur'ani da ba su qirguwa.
Sahabbai mutane ne kamar kowa ta fuskar cewa suna iya yin kuskure ko
laifi. Amma banbancinsu da sauran mutane shi ne, suna da tsarkin zuciya da
shaidar Alqur'ani. Ba ni zaton wannan magana ta buqaci a kafa mata hujja, sai fa ga wanda ba shi da wata masaniya sam sam game da Alqur'ani. Don haka idan
sun yi kuskure to, sun samu yafewar Allah da tabbacin su yardaddu ne, 'yan
aljanna.1
 Wannan shi ne dalilin da ya sa malaman Sunna suka fifita kame baki
daga faxin abin da ya gudana a tsakanin Sahabbai domin bakin rijiya ba wurin
wasar makaho ne ba. Wanda kuwa duk ya shagaltu da neman kurakuransu da
ayubbansu zai wayi gari yana raina su ko ya qyamace su alhalin Allah ya umurce
shi da darajanta su da qaunar su da yi ma su addu'a. Ka ga a nan shi ne ya faxa
ruwa. Daga cikin abin da ke nuna mana cewa, ba wai nufin malamai shi ne a
voye gaskiya ba, zamu ga ai duk tarihin nan da suka ce mu kame baki daga ce-
ce-ku-ce a kan sa su suka rubuta shi, ba su voye komai daga cikinsa ba,
sawa'un mai daxi da maras daxi, na gaskiya da na qarya. Sun hikaito mana ko
wanne a matsayin ruwaya da aka faxa kuma sun kawo wanda ya faxe ta.
Dalili na uku da ya sanya malaman Sunna sukar wannan matsayi shi ne
la'akari da suka yi da yadda tarihi ya gauraya da ra'ayoyi da son zuciya na
Daikaiku da na qungiyoyi wadanda ba su jin ciwon fesa qarya don cimma wata
manufa, ko aibanta wani ko gwarzanta shi. Ga shi kuma tarihi bai samu irin
hidimar da Hadisin Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam ya samu ba na
cikakkiyar kulawa da tantancewa tare da banbanta ingantacce daga wanda ba
shi ba.
Bugu da qari kuma sai marubuta iri iri suka bayyana kowa da irin fassarar
da yake yi ma abin da ya auku. A dalilin haka, sai aka yi ta yi ma wasu riwayoyi
gyaran fuska, wasu aka sauya su, aka karkata alhairansu suka koma sharri,
wasu kuma aka qara masu matsayi suka kai inda ba su cancanta ba.

Duba alal misali: Suratul Hashri: 8-10 da Suratul Fathi: 18 da Suratul Mujadala: 22 da
Suratut Taubah: 100.

Littafin: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

Mu gamu a darasi na 2

25/4/1439
15/12/2017​

» Zauren Minbarin Malamai+2347037477743
Share:

Thursday, 4 January 2018

Shi'a: Kura da fatar Akuya 01 - Mal.Umar shehu zaria


*SHI'A: KURA DA FATAR AKUYA*

FITOWA TA 1

Imamu Malik Bn Anas, Rahimahullah, ya ce:

*_"Su wadannan mutane - 'Yan Shi'a - wasu mutane ne da suka yi nufin su ci mutuncin Manzon Allah, sallallahu' alaihi wa sallama, amma sai suka ga haka ba zai yiwu ba kai tsaye wannan ya sanya sai suke cin mutuncin Sahabbai don a ce Manzon Allah ba mutumin kirki ba ne, kuma don mutane su ce ai inda mutumin kirki ne da SahabbanSa ma sun zama mutanen kirki"_*. A duba al-Saarimul Masluul na Sheikhul Islam Ibn Taimiyyah shafi na 580.

Don haka, duk mai neman gamawa da duniya lafiya, to ya nisanci addinin Shi'a.

✍🏼Dan uwanku a Musulunci:
*_Mal Umar Shehu Zaria_*
03/01/2018.

Daga: *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*

Keep stay with us more updates is coming..... 
Share:

Friday, 29 December 2017

TARIHIN MATAYEN GIDAN ANNABI (SAWW) - KASHI NA BIYU

TARIHIN MATAYEN GIDAN ANNABI (SAWW) - KASHI NA BIYU.

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM

Salati da amincin Allah da albarkokinsa da rahamarsa su tabbata bisa Babban Masoyin Ubangijin Talikai. Annabin da Ubangijinsa ya tsarkake Garinsa da Nasabarsa da iyalan gidansa da Matayensa

Salatin ya hada da Sahabbansa da dukkan alayensa da mabiyansa har zuwa ranar da Qasa zata fitar da nauye-nauyen da take dauke dashi.

Idan Daliban ZAUREN FIQHU suna biye damu, awancan darasin mun kawo tarihin Babbar Uwargidan Manzon Allah (saww) wato Nana Khadeejah bintu Khuwailid (rta).

Yau kuma in sha Allah zamu dora da tarihin wacce take biye da ita wajen Shigowa wannan gidan Mai Albarka. wato Sayyidah Saudah (yardar Allah ta tabbata gareta).

NANA SAUDATU (RTA)

SUNANTA DA NASABARTA
*****************************
Nana Saudah (rta) ita ce mace ta farko wacce Ma'iki (saww) ya aura bayan rasuwar Nana Khadeejah (ra). Kuma nasabarta ita ce kamar haka :

Mahaifinta : Sunansa Zam'atu bn Qays, 'dan Abdu Shamsi, 'dan Abdu Wadd,  'dan Aamiru, 'dan Lu'ayyu 'dan Ghalibu.

Wato nasabarta ta hadu da ta Manzon Allah (saww) akan Kakansa Lu'ayyu bn Ghaalib.

MAHAIFIYARTA : Sunanta Ash-Shamoos bintu Qays bn Zayd. 'Yar Qabilar Banun Najjar ce daga garin Madina.

Wato Mahaifiyarta tana da kusancin nasaba da dangin Mahaifiyar Abdul Muttalib (Kakan Manzon Allah saww).

Nana Saudah tana daga cikin mata masu alfarma da girman Nasaba acikin Quraishawa. Kamar yadda Imam Zahabiy ya fada acikin littafinsa na tarihi.

Babban Malamin Tarihin Musuluncin nan wato Ibnu Sa'ad yace : Saudatu bintu Zam'ah da ita da Mijinta As-Sukraan bn 'Amru (ra) - 'dan Uwan babban Sahabin nan Suhaylu bn Amru (ra) suna daga cikin mutanen da suka fara karbar Musulunci. Kuma daga baya sukayi hijira tare zuwa Qasar Habasha.

(Aduba Tabaqat Alkubra na Ibnu Sa'ad, Juzu'i na takwas, Shafi na 57).

HIJIRARTA ZUWA HABASHA
*******************************
Kasancewar Nana Saudah tana daga cikin farko farkon shiga Musulunci, da ita da sauran Sahabban Manzon Allah (saww) sun fuskanci Tsanantawa da wulakantawa da chutarwa mai tsanani daga Kafiran Makkah.

Yayin da chutarwar ta tsananta, Sai Manzon Allah (saww) ya basu Umurnin cewa suyi hijira zuwa Qasar Habasha har sai abubuwa sun daidaita. Domin kuwa Sarkin Qasar yana da adalci kuma ba ya yarda da duk wani zalunci.

Don haka wasu daga cikin Sahabban sukayi Hijira zuwa chan Qasar Habasha din. Wasu sun tafi tare da iyalansu, wasu kuma su kadai suka tafi.

To ita Nana Saudah tayi hijirar tare da Mijinta As-Sukraan bn Amru tare da wasu mutum takwas daga Banu 'Amru.

Saboda Qarfin imani irin nata tun alokacin, ta kyale dukiyarta da iyayenta da dukkan abinda ta mallaka, ta tafi domin tseratar da Imaninta. Hakanan Allah yake jarrabar bayinsa Muminai domin ya Qarfafa imaninsu.

Suna chan suna zaune cikin aminci a Qasar Habasha, sai wani labari marar tushe ya iskesu cewar wai yanzu komai yayi kyau agarin Makkah, kafiran sun dena chutar da Muminai.

Jin haka yasa wasu da dama daga cikin masu hijirar suka dauko hanya suka dawo gida.

Suna shigowa garin Makkah sai suka tarar ashe labarin nan da aka basu ba haka abin yake ba.

Nan take suka fara fuskantar matsaloli fiye da da. Kuma kafiran suka Qara Qaimi wajen tsananta musu.

Shi kuwa Mijin Nana Saudatu tun akan hanyar dawowa gida ya kamu da rashin lafiya. Don haka basu jima sosai da komowa ba, sai Allah ya karbi ransa (Allah shi Qara masa yarda).

Shi kuma Manzon Allah (saww) babu dadewa Matarsa wacce yake ji da ita, wato Nana Khadeejah bintu Khuwaylid (ra) ta rasu. Acikin shekara guda tare da baffansa Abu Talib.

Wannan rasuwar tasu ta zamo babbar abin bakin ciki sosai agareshi. Domin kuwa Abu Talib shine yake kareshi daga maganganun da kafiran suka gaya masa. Kuma sun kasa tasowa gadan-gadan domin dukansa ko Kasheshi saboda albarkacin suna ganin girman Abu Talib din.

Ita kuma Nana Khadeejah ita ke kwantar masa da hankali duk lokacin da ya shiga cikin damuwa. Kuma tana Qarfafarsa akan duk abinda zai gudanar.

Saboda hakane su kansu Sahabbansa maza da Mata suka rika tayashi bakin cikin wadannan rasuwar.

Watarana Manzon Allah (saww) yana zaune sai ga wata daga cikin Mataye Sahabbai tazo wajensa. Sunanta Khaulatu bintu Hakeem (Matar Uthman bn Maz'un rta).

Tace masa "Ya Rasulallahi lallai kana cikin damuwa game da mutuwar Khadeejah".

Yace mata "Kwarai kuwa. Ita ce Mahaifiyar 'Ya'yana, kuma Uwargidan wannan gidan".

Sai tace "Ya Rasulallahi ko zaka yi aure?

Sai yace "Wa zan aura?".

Sai tace "Akwai Budurwa, akwai kuma Bazawara, Sai wacce kake so".

Sai yace "Shin wacece Budurwar?". Sai tace "A'ishatu bintu Abubakrin, 'Yar mafi soyuwar Mutane agareka".

Sai yace "To wacece Bazawarar?". Sai tace "Saudatu bintu Zam'ah.  Wacce tayi imani da Manzancinka, kuma tana bin Umurninka".

Daga nan sai Ma'aiki (saww) yayi farinciki  kuma yayi mata izinin taje ta nema masa duk guda biyun.

Da farko ta shiga ta gidan Sayyiduna Abubakrin, sannan ta fito ta nufi gidan su Saudah (ra).

Ta shiga wajen Saudah tayi mata albishir tana cewa : "Hakika Ubangiji ya sanya albarkarsa da falalarsa agareki Ya ke Saudatu!".

Sai Nana Saudah tace "Menene ya faru?" sai tace "Ai Manzon Allah ne (saww) ya turoni domin in gaya miki yana so zai aureki".

Daga jin wannan sai murna ta lullubeta, tace ma Khaulah "Kije wajen Mahaifina ki shaida masa".

Anan zamu tsaya, sai a darasi na uku zamu ci gaba in sha Allahu. Da fatan ALLAH shi albarkaci dukkan daliban Zauren Fiqhu, Allah ya saka ma kowa da alkhairi. Allah shi bamu ikon koyi da magabatanmu na kwarai.

An gudanar da karatun ne a ZAUREN FIQHU WHATSAPP (3) Ranar Juma'a 12 ga November 2015.
Share:

MAFI TSADAR ADDU'O'I (12) DA SUKA ZO A HADISAN MANZON ALLAH (S.A.W)

MAFI TSADAR ADDU'O I GUDA (12) DA SUKA ZO A HADISAN MANZON ALLAH (S.A.W)

1. LA'ILAHA ILLAHUWA WAHADAHU LA SHARIKA LAHU LAHUL MULKU WA LAHUL HAMDA WA HUWA ALA KULLI SHAY'IN QADIR (10 ko 100)

Manzon Allah (S.A.W) yace wanda ya fadi wannan 100 za a kankare masa zunubai dari kuma za a rubuta masa kyawawan aiki dari Kuma a wannan rana bawani da zaizo da wani aikin alheri kamar nasa sai wanda ya fadi fiye da abinda ya fada kuma za tsareshi daga sharrin shaidan da duk wani abun qi Kuma yace babu wani zikiri ko addu'a kamar Hailala

2. LA'ILLA HA ILLAHUWA MALIKUL HAQQUL MUBIN. (100)

Manzon Allah(S.A.W) yace duk wanda ya fadi wanann sau dari a rana bashi ba talauci kuma za'a tsareshi daga fitinar kabari

3. BISMILLAHI RAHAMANI RAHEEM, LA HAULA WALA QUWATA ILLA BILLAHIL ALIYUL AZEEM. (100)

Manzon Allah(S.A.W) ya cewa da Sayyadina Aliyu ba wanda zai fadi wannan kalmomi duk wata masifa ko bala'i duk rintsi sai ya fita.

Annabi Alaihisalam yace wanda yake karanta Lahaula bashi ba talauci kuma kanzi ce daga kanzi na aljanna tana toshe kofofi saba'in na bala'i da cuta mafi kankanta ciki shine bacin rai da damuwa kuma yace: duk wanda samun arziki yayi masa wuya to ya yawaita yin LAHAULA...

Kuma duk wanda yake karanta BISMILLAH (21) bayan isha'i cutar annoba ko ta dauka bazata taba kamashi ba kuma bazai mutuwar fuju'a ba

4. SUBAHANALLAHI WA BI HAMDIHI. (100)

Shine Tasbihin Annabi Nuhu shi kuma mala'iku suke Allah yake arzuta dukkan halitta dashi.

5. HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKIL(450)

Shine Tasbihin da Annabi Ibrahima yayi lokacin da aka jefa shi wuta Allah ya mayar masa da ita sanyi itace Shabai sukayi lokacin yaqin Badar Annabi yayi nasara kuma basu ji tsoron kafirai ba duk da sunfisu yawa.

6.  LA ILA HA ILLA ANTA SUBAHANAKA INNI KUNTU MINAL ZALIMIN (sau 41 ko 100)

Manzon Allah(S.A.W)  yace: "Addu'a Annabi Yunusa lokacin da ke cikin kifi babu wani mumini da zai roki Allah wani abu dake damunsa face Allah ya maganata masa kuma yace Ismullahil Azeem sunan Allah da in Aka addu'a yake amsawa kuma idan aka rokeshi yake bayarwa itace addu'a Annabi Yunusa.

7. ASTAGFURULLAHA LAZI LA'ILA HA ILLAHUWAL HAYYUL QAYYUM WA ATUBU ILAIHI. (100)

Manzon Allah(S.A.W) yace: Ba wanda zai fadi haka fache an gafarta masa zunubansa koda sun kai kunfar kogi. kuma Alqawarin Allah ne a cikin Suratul hudu duk wanda ya lazumci Istigfari zai jiyar dashi da dadi kuma yabashi arziki kan arziki(zai samu budi)  kuma zai bashi girma akan girma Daukaka

8. SUBAHANALLAHI WABI HAMDIHI SUBAHANALLAHIL AZEEM ASTAGFRULLAH(100 kafin Asubah)

Wani Sahabi yazo wajen Manzon Allah Alaihisalam yayi masa kukan duniya ta juya masa baya(talauci)  yasanar dashi tasbihin Mala'iku sai Annabi yasanar dashi yace ya dingayi shi bayan raka'a tainul fajar kafin Asubah bai gushe ba sai da ya dawo wajen Annabi Alaihisalam yace Allah yabashi duniya (arziki)  har ya rasa inda zai kaita

9. YA HAYYU YA QAYYUM LA'ILA HA ILLA ANTA(sau41)

Imamu Shafi'i(Rahimahullah) yayita mafarki da Annabi sai watarana sai yace shin kasanar dani wani abu da Allah zai dinga haskaka mani kuma ya raya zuciyata akan imani(ibada)  sai Annabi ya sanar dashi wannan ya dingayi kafin Asubah ko bayan Asubah sau 41 (Saboda haka ba wanda zai lazumceta sai yazama mai maida hankali akan ibada kuma yazama wanda mutane zasu dinga jin maganarsa kuma abin so a cikinsu

10. SUBAHANALLAHI(33) WAL HAMDULLAHI(33) WAL LAHU AKBAR(34) da dare kafin bacci

Wannan shine Tasbihin da Annabi ya bawa Sayyada Fatimah lokacin da ta nemi Annabi ya bata hadimi sai ua snaar da ita wannan tasbihi da ta dingayi kullum kafin ta kwanta bacci shine mafi alkhairi gareta da yabata hadimi

11. SUBAHANALLAHI(10) WALHAMDULLAHI(10) WALLAHU AKBAR(10) bayan Salloli biyar

Watarana Ummu Sulaim tazo wajen Annabi Alaihisalam tace ya sanar da ita wani abu da zata dinga rokon Allah dashi sai yace tayi wannnan tasbihin sai ta roki Allah bukatarta za ace anzartar anzartar (wato an amsa mata abinda ta roka)

12. SALATIN ANNBI (10 ko 100 ko 500 ko 1000 har abinda yayi sama)

Manzon Allah(S.A.W)  yace: "wanda bukatarsa tayi masa wahalar samu to  ya yawaita salati gareni lalle yana tafiyar da damuwa da bakin ciki da kuncin rayuwa kuma yana yawaita arziki da kuma biyan bukatu.

Allah kasa mu dace, Amin.

DAGA ZAUREN TAFSIR DA SUNNAH

Share:

Thursday, 21 December 2017

DAUSAYIN IYALI 002 - Dr. Mansur Ibrahim Sokoto


*DAUSAYIN IYALI 002*
Matsayin Mata da Hakkokinsu a Musulunci

Littafin *Dr. Mansur Sokoto*

 Matsayin Mata Kafin Zuwan Musulunci
Abu ne da tarihi ya tabbatar cewa, Macce ba a dauke ta a matsayin
kammalallen dan Adam ba kafin zuwan Musulunci. Domin kuwa an
mayar da ita kamar Haja wacce ake saye kuma ake sayarwa, ake kuma
gadon ta kamar yadda ake gadon gida ko gona ko duk wata kaddara
da Namiji ya mutu ya bar ta. Akan umurci Macce ta yi Zina don ta kawo
kudi, kuma ana aurar da ita ne yadda aka ga dama, ba tare da neman
zabinta ko ma shawartar ta ba.
A da Namiji yakan auri ko Mata nawa yake so kuma ya ga dama kamar
yadda yake iya mallakar riga da hula ko nawa yake so.
A wasu sassan duniya ba a yarda Macce mutum ce ba ma sam. Misali,
a qasar Rasha Malaman addini sun ba da fatawar cewa, Macce najasa
ce, matsayinta daya ne da na Kare.
A yankin Larabawa, zamanin Jahiliyya, uba yakan sayar da diyarsa.
Yakan kuma rufe ta cikin qasa babu gaira babu dalili. Kawai dai
haifuwar ta ba abin farin ciki ba ne balle ai alfahari. Budurwa tana goge
gumi daga fuskar babanta a lokacin da yake haqa ramin rufe ta, amma
ita ba ta sani ba.
Kashe Macce - kafin zuwan Musulunci - ba wani babban laifi ba ne da
har za ayi maganar Qisasi ko Diyya a kan sa.
A qasar Indiya akan qone Macce ne tare da mijinta idan ya mutu,
alhalin tana da ranta da lafiyarta. Wannan ya sa sau da yawa Macce
takan kashe kanta bayan mutuwar mijinta irin mutuwar da take ganin
ta fi mata sauqi, don kauce ma wannan baqar mutuwa da mummunan
bala'i.
Malaman addinai biyu da ake a da su a lokacin wadan da suka samo
koyarwarsu daga manyan Annabawa ba su tabuka komai a kan wannan

- Yahudawa - mabiyan Addinin Annabi Musa Alaihis Salam sun dauki
Macce a matsayin najasa duk lokacin da take Haila. Ba za su ci abincin
da ta dafa ba, ba kuma za su kusance ta ba. A maimakon haka sai su
kafa ma ta rumfa a bayan gida - kamar yadda ake turke Akuya - su riqa
ba ta ruwa da gurasa har sai lokacin da ta gama al'ada sannan ta dawo
cikin gida.
- Su kuma Kiristoci duk da ba su nuna qyamar ta a wannan lokaci.
Kuma ma har saduwa suke yi da ita a lokacin da take Haila. Amma ba
za mu dauka cewa sun mutunta ta ba tun da yake suna kallon ta a
matsayin ita ce ummul-haba'isin duk wani laifi da sharri da cuta da ake
yi a duniya. Kuma wai, ita ce qofar shiga wuta. Suna kafa hujja da
cewa, wai, ita ce ta bai wa Annabi Adam (Alaihis Salam) shawarar cin
bishiyar da Allah ya hana shi har ta jawo ma su uqubar fita daga gidan
aljanna.


*Kusaurari cigaba da izinin Allah*

Gabatarwa a social Media
*Ibrahim Nasidi Baban Ilham*
Share:

DAUSAYIN IYALI - Dr.mansur ibrahim sokoto



*DAUSAYIN IYALI*
Matsayin Mata da Hakkokinsu a Musulunci Fitowa ta 001
Littafin Dr. *Mansur Sokoto*
Gabatarwa
Addinin musulunci kammalallen addini ne, wayayye, kuma wanda ya
game duk sassan rayuwa, sannan ya dace da kowane zamani da
kowace al’umma. Ko kuma ma mu ce, kowane lokaci da kowane
zamani sun dace shi.
Babu wani tsari ko wata doka da suka kai kyan tsari da dokar Musulunci
ballatana su wuce shi. Addini ne da Allah mahaliccin bayi ya tsara
komai a cikin =ad a yadda bayin Allah za su samu nagartacciyar
rayuwa idan suka bi tafarkinsa.
Mata su ne rabin al’umma. Kuma rabi ne mai muhimmanci. Domin su
ne masu haifuwar Mazan da Matan duka. Amma kuma an dade ba a
gano daraja da matsayin wannan jinsi na Bil-Adama ba.
Kyakkyawan zatona shi ne wannan nazari zai ba da dogon haske, kuma
a taqaice kan wannan batu.
*Kusaurari cigaba da izinin Allah*
Gabatarwa a Social Madia *Ibrahim Nasidi Baban Ilham*
Share:

Monday, 18 December 2017

Ba'a Yi Duniya Don Manzon Allah S. A. W Ba!!! Dr Jamilu Yusuf Zarewa



*_Tambaya_*

Assalamu alaykum Don  Allah Dr, shin ya Halatta ace anyi duniya don manxon Allah?

*_Amsa_*
Wa alaikum assalam,

Ba'a yi mutanan duniya don Manzon Allah ba, an yi mutanan duniya ne don su bautawa Allah.
Allah madaukakin sarki yana cewa a cikin suratu Azzariyat aya ta (56) "Ban halicci  mutum da Aljan ba sai dan su bauta min, bana bukatar wani arziki a wajansu kuma bana bukatar su azurta ni"
Ayar da ta gabata ta bayyana dalilin da yasa Allah ya halicci mutane da Aljanu, wato bautawa Allah da kuma tsayar da tauhidi.

Babu wani nassi ingantacce yankakke wanda ya nuna an yi duniya saboda Manzon Allah S.A.W. hakan kuma ba ya nuna an tauye manzon tsira.

Annabi S.A.W. bawa ne daga cikin bayin Allah kamar yadda tarin ayoyin Al'qur'ani suka tabbatar da hakan, sannan shugaban 'ya'yan Annabi Adam kamar yadda ya tabbata a hadisai ingantattu a kundayan musulunci.
Ajjiye shi a matsayinsa da Allah ya ajjiye shi, shi ne daidai kamar yadda yake cewa "Kada ku wuce gona-da-iri wajan yabona kamar yadda nasara suka wuce a lamarin Isa dan Maryam"

Allah ne mafi sani

*_Dr, Jamilu Zarewa_*

02/12/2017
Share:

ZAKKAR GIDAN HAYA DA MOTAR HAYA - Dr.jamilu yusuf zarewa

*_ZAKKAR GIDAN HAYA DA MOTAR HAYA_*


*_Tambaya_*

Assalamu alaikum
Malam Shin ko akwai zakka akan Gona, Fili ,Gidan haya da Motar Haya?


*_Amsa_*
Waalaikumussalam

To dan'uwa duk gonar da aka rika don ayi amfani da ita, to babu zakka a cikinta, haka nan fili, amma idan kasuwanci ake yi da su, kamar a siya a sayar to za'a fitar musu da zakka, idan sun cika nisabi kuma shekara ta zagayo musu, ko kuma ya zama  sun cika sharudan zakka idan ya hada su da abin da ke hannunsa .
Haka nan babu zakka a cikin gidan haya saidai idan aka tara kudin kuma shekara ta zagayo akan su, sun cika nisabi, to anan ne za'a fitar musu da zakka, ko kuma ya zama sun cika sharudan zakka idan ya hada su da abin da ke hannunsa .

Allah ne ma fi sani .

*_Dr. Jamilu Zarewa_*

18/12/2014

Gà dukkan mai son shiga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH* sai ya yi saving wannan number +2348122248585 sannan ya tura da sunansa da adireshinsa ta whatsApp.Duk abun da mutum ya turo matukar ba suna ba ne ba za a kula shi ba.
Share:

Saturday, 9 December 2017

Goron Juma’a: Mutanen da Allah ba ya kauna a Duniya

- Mun kawo Mutane 4 da Allah ba ya kauna a Duniya

- Daga ciki akwai tsohon da ya tsufa ba ya gudun zina
- Akwai kuma Matalaucin mutum mai mugun girman kai
A Rana irin ta yau mun kawo maku wani Hadisi na Manzon Allah Annabi Muhammadu SAW inda ya bayyana wasu mutane 4 da Ubangiji Madaukaki ba ya kaunar su a Duniya saboda mugun halin su. Wadannan mutane dai su ne:-

1. Matalauci mai girman kai
Kamar yadda Marigayi Malam Ja’afar Mahmud Adam ya bayyana daga cikin wadannan mutane akwai wanda ke fama da mugun talauci amma kuma yake da dan-karen girman kai.

2. ‘Dan kasuwa mai yawan rantsuwa
Haka nan kuma akwai ‘dan kasuwar da yake yawan rantsuwa bini-bini a duk lokacin da zai saida kaya a kasuwa. Musamman kuma ace mutum karya yake yi wajen ratsuwar.

3. Dattijo mai yawan zina
Akwai kuma tsohon da ba ya gudun zina duk da shekarun sa sun yi nisa amma ba ya jin tsoron Allah. Ubangiji Madaukaki SWT ba ya son irin wannan mutumi.

4. Azzalumin mai mulki
Na karshen su dai a Hadisin shi ne kuma wanda ya samu mulki amma kuma yake kuma kuntatawa Jama’ar sa na Talakawa da damar da ya samu.

Share:

*'YAN SAMARI MINTI BIYU 03

*'YAN SAMARI MINTI BIYU 03*

Duk wanda ka gani da arziki tashi ya yi ya nema sai Allah Ta'ala Ya bashi domin sama ba ta ruwan zinariya.

Manzon Allah, sallallahu' alaihi wa sallama, Ya ce a cikin hadisin da Abi Hurairah ya riwaito: *"Ina rantsuwa da wanda Raina ke hannun Shi, dayan ku ya dauki igiya ya je ya yi itace ya dauko shi a bayansa, shi ya fi masa alheri fiye da ya je wurin wani mutum yana rokon shi koda kuwa wannan mutumin ya bashi abun da ya roka ko ya hana shi"*. Bukhari ya riwaito hadisi na 1412.

Don haka, Abokina ka tashi ka kama sana'a arziki a hannun Allah Yake kuma Zai iya baka fiye da tsammanin ka.

Mu hadu a fitowa ta 04 in sha Allahu Ta'ala.

✍🏼Dan uwanku a Musulunci:
*_Umar Shehu Zaria_*
05/12/2017.
Share:

*'YAN SAMARI MINTI BIYU 02*

*'YAN SAMARI MINTI BIYU 02*

Abokina, kar ka yaudari kanka ka kashe kuruciyarka ta hanyan zama a dakali ko wani wurin zama inda zallan labarin duniya ake yi ko cin naman mutane a irin wannan wuri.

Ibn al-Qayyim, Rahimahullah, ya ce: *"Wuraren zama inda  ake ambaton Allah, su ne wuraren da Mala'iku suke zama, amma wuraren da ake zama ana wasanni da shagala, wadannan wuraren zama ne na shaidanu. Don haka, bawa ya zaba ma kansa wanda ya fi burge shi daga cikin wadannan biyu, amma ya sani yana tare da duk wanda ya zaba a nan duniya da lahira"*. A duba littafin al-Waabilu al-Sayyib 65.

Don haka Abokina, yi kokari ka zauna da mutanen kirki kafin lokaci ya kure maka.

Mu hadu a fitowa ta 03, in sha Allahu Ta'ala.

✍🏼Dan uwanku a Musulunci:
*_Umar Shehu Zaria_*
04/12/2017.
Share:

Thursday, 30 November 2017

MAFI DADIN ABINDA NA KARANTA A YAU

*MAFI DADIN ABINDA NA KARANTA A YAU*


تمنى إبراهيم الخليل أن يكون أبوه مسلماً ولم يشأ الله له رغم أنه أبو خليله ... !!!

Annabi Ibrahim yayi fatan mahaifinshi ya musulunta, amma Allah bai ga damar hakan ta kasance ba, duk da cewa baban babbanmasoyinshi (bada'dayin) ne....

وتمنى نوح العبد الشكور أن يكون ابنه مسلما  ويأبى الله رغم دعاء نوح ...!!!

Haka nan Annabi Nuhu bawa mai yawan godiya ga Allah, yayi fatan danshi ya musulunta, amma Allah ya'ki hakan ta kasance, duk da addu'ar da Annabi Nuhu yayi...

وتمنى محمد  صل الله عليه وسلم أن يسلم عمه ولم يكتب الله له هداية رغم أنه نصر الرسول في دعوته ...!!!

Haka nan Annabi Muhammad S.A.W yayi fatan Baffan shi (Abu 'dalib) ya musulunta, amma Allah bai rubuta mishi shiriya ba, duk da irin taimakon da ya bawa Annabi wajen ya' da da'awar shi....

وجعلني وجعلك مسلماً دون سؤال وأعطانا ما لم يعط إبراهيم في أبيه ونوحًا في ابنه ومحمدًا صل الله عليه وسلم في عمه ..

Amma Allah ya sanya ka ya sanya ni muka zamto musulmai ba tare da mun ro'ka ba, ya bamu abinda bai bawa Annabi Ibrahim ba dangane da mahaifinshi, bai bawa Annabi Nuhu ba dangane da 'danshi, bai bawa Annabi Muhammad S.A.W ba dangane da Baffan shi..!!!

أي فضل هذا ... !!!!! ؟
( إِنَّ اللَّهَ لَذو فَضلٍ عَلَى النّاسِ وَلكِنَّ أَكثَرَ النّاسِ لا يَشكُرونَ )
Wannan Wace irin falala ce....!!!!
"hakika Allah ma'abocin falala ne ga mutane, sai dai mafi yawan mutane basu da godiya "

نعمة اﻹسلام ترجح لو وزنتها بكل النعم ..
الحمد لله الذي هدانا لهذا وما كنا لنهتدي لولا ان هدانا الله ..


Ni'imar musulunci ta rinjayi dukkan wata ni'ima da za'a auna.....
Godiya ta tabbata ga Allah da ya shiryar damu da hakan, kuma bamu kasance masu shiryuwa ba, ba don Allah ya shiryar damu ba.

الحمد لله حتى يبلغ الحمد منتهاه
Godiya Ta tabbata ga Allah, iya matu'kar kurewar godiya.

*Fassara* :
*Malam Anas Assalafy Fagge*

Daga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*


Share:

Saturday, 25 November 2017

Audio :- Muhimmancin Amana A Wajen Musulmi - Dr. Muhammad Sani Umar R/Lemo

Muhadara

Mai taken: Muhimmancin Amana A Wajen Musulmi

Tare da: Dr. Muhammad Sani Umar R/Lemo

30/2/1439
19/10/2017​



Download Audio Now

Share:

Naga Wandona A Jike Da Maniyyi Bayan Na Kammala Sallar La'asar? Dr Jamilu Yusuf Zarewa


Tambaya

 Aslamualaikum MALAM na tashi da janaba nayi salar asuba da azahar da kuma laasar, duk nayi sallah sai bayen naje wanka da yemma naga wando na da alamun manniyi shin ya ingancin sallolina na baya ? nagode

Amsa

Wa alaikum assalam, mutukar ka tabbatar a baccin asuba maniyyin ya fito, to ya wajaba ka sake asuba da azahar da la'asar din.

In har ka yi wani baccin bayan azahar to za ka danganta janabar ne zuwa ga baccin karshe da ka yi, ta yadda sallar da ka yi bayan baccin karshe ita za ka sake, kamar yadda Imamu Malik ya rawaito a Muwadda daga Sayyady Umar.
Allah ne mafi sani 

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
13/11/2017
Share:

Siffofin Aboki Nagari !!! Dr Jamilu Yusuf Zarewa

*Tambaya:*

Assslamu alaikum Malam ina da abokai da yawa, amma ina so ka ba ni shawara?

*Amsa:*

Wa alaikum assalam, To dan'uwa Aboki yana da mutukar mahimmanci a rayuwar mutum, idan ya zama abokinka mutum ne mai himma, sai kai ma ka samu himma kamar yadda ake cewa zama da madaukin kanwa yana kawo farin kai, haka nan idan ya zama mutumin banza sai ya yi maka tasiri, Abu Musa Al’ash’ari ya rawaito hadisi daga Annabi ((s.aw.)) yana cewa (misalin aboki na gari da abokin banza, kamar misalin mai daukar turare ne da mai hura zuga-zugi, mai daukar turare ko dai ya shafa maka ko ka sayi turare a wurinsa ko kuma ka ji kamshi mai dadi a wurinsa, mai hura zuga- zugi kuma ko ya kona maka kaya ko ka ji wari a wurinsa) Bukhari ne ya rawaito
Kuma wani malami yana cewa:
• idan ka kasance a cikin mutane, to ka yi abota da zababbensu, kada ka yi abota da halakakke saiku halaka tare.
• Idan kana so ka san waye mutum, to ka tambayi abokinsa, saboda kowanne aboki da abokinsa yake koyi .
Wani kuma yana cewa:
• Kar ka aboci malalaci a kowanne hali, da yawa mutumin kirki yana lalacewa ne idan ya hadu da mara kirki.
• Dakiki yana saurin tasiri akan mai kokari, ba ka ganin garwashe idan aka saka shi a toka shi ma sai ya zama toka.
Da fatan za ka kula da abin da ya gabata.
Allah na mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
11/11/2017
Share:

Wanda Ya Zage Ka, Yafi Wanda Ya Yabe Ka !!!Dr Jamilu Yusuf Zarewa



salamu alaikum Malam wani yana ta zagina ba abin da na yi masa, ina neman shawara ?

*Amsa:*

Wa alaikum assalam To dan'uwa Ibnuhazm Azzahiry (456) yana cewa a cikin littafinsa Assiyar Wal-aklaak : "Wanda ya zage ka yafi wanda ya yabe ka, saboda wanda ya yabe ka ko dai ya fadi abin da kake da shi, ko kuma ya fadi abin da ba ka da shi.
idan ya fadi abin da kake da shi bai kare ka da komai ba, idan kuma ya fadi abin da baka da shi to ya cutar da kai.

Wanda ya zage ka kuwa : ko dai ya aibantaka da wani hali da kake da shi ka ga hakan sai ya sa ka gyara, ko kuma ya aibanta ka da halin da baka da shi , sai ya zama ya maka tanaji a lahira."

Daya daga cikin magabata ya hadu da wani sai ya ci mutuncinsa, sai ya ce masa dan jira kadan, ya shiga gida ya tuba ga Allah kankan da kai zuwa gare shi.
Bayan ya fito mutumin ya kasa zaginsa sai ya ce me ya faru da kai ? sai ya ce: Na tuba ga Allan da ya dora ka a kaina.
Da yawa zagin da mutane suke maka wani zunubi da ka aikata ya jawo maka.
Allah ne mafi sani

 *Amsawa* ✍🏻 

                                                                               *DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
11/11/2017
Share:

Zan Iya Rantsuwa Da Al-Qur'ani ? Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*TAMBAYA*
Salamun alaikum Dr. Don Allah mene ne hukuncin rantsuwa da Al-Qur'ani?, kamar ka ce: Alquran.

Allah Ya kara ma Dr. Lfy Amin.

*AMSA*
Wa alaukum assalam, Ya halatta mana tun da qur'ani sifa ne daga cikin sifofin Allah .

Annabi S.A.W. Yana cewa: "Duk wanda zai yi rantsuwa, to ya rantse da Allah ko kuma ya yi shiru" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta: (6270).

Rantsuwa da Allah ya kunshi rantsewa da daya daga cikin sunayanSa ko daya daga cikin sifofinSa, kamar yadda malamai suka yi bayani.

 kasancewar daga cikin sifofin Allah akwai zance,  kuma Al-Qur'ani maganar Allah ce ba halittarsa ba, kamar yadda aya ta: (6) a suratu Attaubah ta yi bayani, hakan sai ya halatta rantsuwa da shi.

Allah mafi sani.

✍🏼Amsawa:
*_Dr Jamilu Yusuf Zarewa_*
09/11/2017.
Share:

Archive

Unordered List

Support