Zan Iya Rantsuwa Da Al-Qur'ani ? Dr Jamilu Yusuf Zarewa ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 25 November 2017

Zan Iya Rantsuwa Da Al-Qur'ani ? Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*TAMBAYA*
Salamun alaikum Dr. Don Allah mene ne hukuncin rantsuwa da Al-Qur'ani?, kamar ka ce: Alquran.

Allah Ya kara ma Dr. Lfy Amin.

*AMSA*
Wa alaukum assalam, Ya halatta mana tun da qur'ani sifa ne daga cikin sifofin Allah .

Annabi S.A.W. Yana cewa: "Duk wanda zai yi rantsuwa, to ya rantse da Allah ko kuma ya yi shiru" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta: (6270).

Rantsuwa da Allah ya kunshi rantsewa da daya daga cikin sunayanSa ko daya daga cikin sifofinSa, kamar yadda malamai suka yi bayani.

 kasancewar daga cikin sifofin Allah akwai zance,  kuma Al-Qur'ani maganar Allah ce ba halittarsa ba, kamar yadda aya ta: (6) a suratu Attaubah ta yi bayani, hakan sai ya halatta rantsuwa da shi.

Allah mafi sani.

✍🏼Amsawa:
*_Dr Jamilu Yusuf Zarewa_*
09/11/2017.
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support