Goron Juma’a: Mutanen da Allah ba ya kauna a Duniya ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 9 December 2017

Goron Juma’a: Mutanen da Allah ba ya kauna a Duniya

- Mun kawo Mutane 4 da Allah ba ya kauna a Duniya

- Daga ciki akwai tsohon da ya tsufa ba ya gudun zina
- Akwai kuma Matalaucin mutum mai mugun girman kai
A Rana irin ta yau mun kawo maku wani Hadisi na Manzon Allah Annabi Muhammadu SAW inda ya bayyana wasu mutane 4 da Ubangiji Madaukaki ba ya kaunar su a Duniya saboda mugun halin su. Wadannan mutane dai su ne:-

1. Matalauci mai girman kai
Kamar yadda Marigayi Malam Ja’afar Mahmud Adam ya bayyana daga cikin wadannan mutane akwai wanda ke fama da mugun talauci amma kuma yake da dan-karen girman kai.

2. ‘Dan kasuwa mai yawan rantsuwa
Haka nan kuma akwai ‘dan kasuwar da yake yawan rantsuwa bini-bini a duk lokacin da zai saida kaya a kasuwa. Musamman kuma ace mutum karya yake yi wajen ratsuwar.

3. Dattijo mai yawan zina
Akwai kuma tsohon da ba ya gudun zina duk da shekarun sa sun yi nisa amma ba ya jin tsoron Allah. Ubangiji Madaukaki SWT ba ya son irin wannan mutumi.

4. Azzalumin mai mulki
Na karshen su dai a Hadisin shi ne kuma wanda ya samu mulki amma kuma yake kuma kuntatawa Jama’ar sa na Talakawa da damar da ya samu.

Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support