Wanda Ya Zage Ka, Yafi Wanda Ya Yabe Ka !!!Dr Jamilu Yusuf Zarewa ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 25 November 2017

Wanda Ya Zage Ka, Yafi Wanda Ya Yabe Ka !!!Dr Jamilu Yusuf Zarewa



salamu alaikum Malam wani yana ta zagina ba abin da na yi masa, ina neman shawara ?

*Amsa:*

Wa alaikum assalam To dan'uwa Ibnuhazm Azzahiry (456) yana cewa a cikin littafinsa Assiyar Wal-aklaak : "Wanda ya zage ka yafi wanda ya yabe ka, saboda wanda ya yabe ka ko dai ya fadi abin da kake da shi, ko kuma ya fadi abin da ba ka da shi.
idan ya fadi abin da kake da shi bai kare ka da komai ba, idan kuma ya fadi abin da baka da shi to ya cutar da kai.

Wanda ya zage ka kuwa : ko dai ya aibantaka da wani hali da kake da shi ka ga hakan sai ya sa ka gyara, ko kuma ya aibanta ka da halin da baka da shi , sai ya zama ya maka tanaji a lahira."

Daya daga cikin magabata ya hadu da wani sai ya ci mutuncinsa, sai ya ce masa dan jira kadan, ya shiga gida ya tuba ga Allah kankan da kai zuwa gare shi.
Bayan ya fito mutumin ya kasa zaginsa sai ya ce me ya faru da kai ? sai ya ce: Na tuba ga Allan da ya dora ka a kaina.
Da yawa zagin da mutane suke maka wani zunubi da ka aikata ya jawo maka.
Allah ne mafi sani

 *Amsawa* ✍🏻 

                                                                               *DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
11/11/2017
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support