Menene hukuncin magana a cikin bandaki ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Thursday 20 October 2016

Menene hukuncin magana a cikin bandaki

MENENE HUKUNCIN MAGANA ACIKIN BANDAKI

الحمد لله والصلاة والسلام على محمد وعلى آله وصحبه وسلم.

AMSA:Makaruhine ambaton Allah awajan biyan bukata, dan girmama sunan Allah madaukakin sarki bai kamata ka ambaceshi agurin najasaba, wanda kuma makwancin shaidanu ne.

Imamun nawawy rahimahullah yace: acikin littafin al'azkaar, [ makaruhine ambaton Allah alokacin da mutum yake biyan bukata, a sahara yake jeji kenan dajin Allah ko agurin da angina shi dan biyan bukata kawai, bawai Ambaton Allah kawai ba, dukkanin zikirai da zance na duniya inba da lalura ba, idan mutum yai attishawa abandaki bazai tahmidi ba kuma baza'a amsa masa ba, haka idan mutum yana biyan bukata bazai amsa sallama koya mayar ba, haka kuma bazai amsawa mai kiran sallah ba, zance a wadannan gurare makruhine, dan tsarkake sunan Allah madaukakin sarki amma ba haramun bane, idan mutum yai attishawa sai ya godewa Allah azuciyarsa, harshensa bai motsaba babu laifi, haka zai aikata ahalin dayake jima'i da matarsa.

Dalili shine hadisi daka Abdullahi dan umar Allah yakara yarda dasu yace: Wani mutum ya wuce manzan Allah yana fitsari sai yaiwa manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam sallama bai amsa masaba,) Muslim (370).

Sabida haka idan wajen alwala yakasance acikin bandaki ban dakin kuma bawajen wankane kawai ba, hukuncin karhancin ambaton Allah maganganun malamai sunci karo da juna awannan wajen tare da halaccin yin bismillah, wasu malaman suntafi akan zaiyi bismillar azuciyarsa batare daya furta da harshen saba.

Wasu malaman kuma sukace: zai yi bismillah da harshen sa ayayin alwala abandaki awannan lokacin babu karhancin.

Yazo afatawar lajnatul da'ima cewa:"makaruhine ambaton Allah agurin da ake biyan bukata dan tsarkake sunan Allah da girmama shi, amma ya halatta yayi bismillah yayin fara alwala domin wajibice awajen dayawa daka cikin malamai.

Idan wajen alwala yakasance wajen bandaki koda ajikin bandakin yake kamar katanga daya gurin yake data bandaki, yahalatta ga mai alwala yafurta bismillah awannan hali domin awajen bandaki ne.

Saboda haka zance abandaki makruhine koda ba ambaton Allah bane, amma idan bukata ta kama yahalatta kamar kana wanka ruwa yakare ma, zakai magana dakarfi akawo ma ruwa ka karasa, ko kana gidan wanka nakudi shaya tadauke ruwa zakai magana babu ruwa da makamantan uzuruka dazaka bukata aima kanada daka cikin bandaki, wallahu A'alam

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك.

Tambayoyin musulunci
Watsapp

Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support