Abinda ake so wanda yaji kiran sallah yayi daga lokacinda yaji kiran sallah har izuwa iqamah ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Wednesday 26 October 2016

Abinda ake so wanda yaji kiran sallah yayi daga lokacinda yaji kiran sallah har izuwa iqamah

*ABINDA AKE SO WANDA YAJI KIRAN SALLAH YAYI DAGA LOKACINDA YAJI KIRAN SALLAH HAR I ZUWA IQAMAH*

Assalamu alaikum
Malam dan Allah ina so amin bayani akan yanda ake amsa kiran Sallah
Nagode

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ

_*AMSA:*_
*******
Da farko dai abinda ake son wanda yaji kiran sallah yayi shine: Maimata wato fadin irin abinda duk ladan ya fada. Amma wajenda ladan ke cewa:

*ﺣﻲ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺼﻼﺓ*
*"Hayya alal Salah"*

da

*ﺣﻲ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻔﻼﺡ*
*"Hayya alal falah"*

Anan sai ace

*ﻻ ﺣﻮﻝ ﻭﻻ ﻗﻮﺓ ﺇﻻ ﺑﺎﻟﻠﻪ*
*"La haula wala quwwata illa billah"*

[Bukhari da Muslim 385]

Idan kuma mai kiran sallah ya kammala kiran sallah sai kace:

*"Ashhadu an la'ilaha illallah wahdahu la sharika lahu, wa anna Muhammadan abduhu wa rasuluhu, raditu billahi rabban, wa bi Muhammadin rasulah, wa bil islami dinan"* [Muslim]

Bayan wannan sai mutum yayi wa Annabi sallallahu alaihi wasallam salati:

Daga Jabir (Allah ya yarda dashi) yace: Annabi (sallallahu alaihi wasallam) yace: "Dukkan wanda yace a lokacinda yaji kiran sallah:

*ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺭﺏ ﻫﺬﻩ ﺍﻟﺪﻋﻮﺓ ﺍﻟﺘﺎﻣﺔ ﻭﺍﻟﺼﻼﺓ ﺍﻟﻘﺎﺋﻤﺔ ﺁﺕ ﻣﺤﻤﺪﺍ ﺍﻟﻮﺳﻴﻠﺔ ﻭﺍﻟﻔﻀﻴﻠﺔ ﻭﺍﺑﻌﺜﻪ ﻣﻘﺎﻣﺎ ﻣﺤﻤﻮﺩﺍ ﺍﻟﺬﻱ ﻭﻋﺪﺗﻪ*

*"Allahumma Rabba hazihid da'watit tammat wassalatil qaimati, ati Muhammadan waseelata wal fadeelata, wab'athhu maqaman mahmoodal lazi wa'adtahu"*

Cetona ya halatta akansa ranar alqiyamah". [Bukhari, 589]

Wato duk wanda aka gama kiran sallah yayi wannan addu'ar zuwa ga Annabi (sallallahu alaihi wasallam) dake a sama to cetonsa ya halatta a gare shi ranar qiyamah. Allah yasa muna daga cikin wadanda zai ceta.

Sai kuma tsakanin kiran sallah zuwa tada iqamah ana son mutum yayi addu'a saboda ana amsar addu'a a wannan tsakanin. Daga Anas (Allah ya yarda dashi) yace: Annabi (sallallahu alaihi wasallam) yace:

*Haqiqa ba'a mayarda addu'a tsakanin kiran sallah da iqamah, saboda haka kuyi addu'a*. [Tirmizi 212, Abu Dawud 437, Ahmad 12174]

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support