Ya hukuncin wanda yai magana ko danna waya a lokacin da liman ke huduba ranar jumu'a?? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 21 October 2016

Ya hukuncin wanda yai magana ko danna waya a lokacin da liman ke huduba ranar jumu'a??

*YA HUKUNCIN WANDA YAI MAGANA KO DANNA WAYA A LOKACIN DA LIMAN KE HUDUBA RANAR JUMA'A.??*

AMSA:Wanda yai magana ranar juma,a ko wasa, ko danna waya, ahalin liman yana huduba, babu shakka yayi laifi wato yayi lagawu wato yashasshen zance na wargi.

Domin shi sauraren huduba ranar juma,a ibada ne yana cikin hukunce hukuncen da juma,a ta kebanta dasu da sauran ranaku,

kuma hadisi ingantacce ya razanar dangane da masu zance ko wasa da wani abu wanda zai dauke hankalinsu daka sauraren huduba lokacin da liman ke huduba, kuma basu da ladan juma,a kawai dai sunyi azahar ne.

Maganar nan kuwa koda ta nusar wace koda wani dan,uwanka ne yake wani abu da bai daceba kace yabari ko yai shiru to kayi lagawu, kuma baka da ladan sallar juma,a.

Allah kayi salati da sallama abisa Annabi muhammad da alayensa da sahabbansa.
Wallahu a'alam

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك.

*TAMBAYOYIN MUSULUNCI*

Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support