2016 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 8 November 2016

Menene banbancin buhutani da allagwu ??

*MENENE BAMBANCIN BUHUTANI DA ALLAGWU??*

الحمد لله والصلاة على أشراف الأنبياء والمرسلين،

Amsa: Abun da ake cewa buhutani shine ka qagi e
wani mummunan abu, ka jinginawa dan,uwanka sawa'un maganace ko aiki, wanda bashi ya aikata ba kuma ba dabi'ar saba ce, kajingina masa danka batashi a idan wanda kake son batashi, ko karage masa wata daraja da yake da ita a tsakanin mutanen dasuke mutuntashi, shine Allah ya zargi masu aikatawa acikin alqur,ani, inda yace:
((ومن يكسب خطيئة او إثمًا ثم يرم به بريئا فقدا هتملوا وإثما مبيتا))،
duk Wanda yake kirkirar wani laifi ko kuskure sannan yajefi wanda yake kubutacce daka laifin, hakika yadaukarwa kansa laifin kirkirar karya da kuma zunubi mabaiyyani.

Shi kuwa lagwu shine wasa mara amfani wasa wanda bamai cema bari, yashashshe wanda bashi dawata fa'ida ko kadan aduniyarka da lahirarka, baida wani amfani akan kanka ma, kamar zance 'yan wasan kwaikwayo da musu akansu, da jayayya akan kwallo dan wasa kaza yafi na kaza, ba'abunda zancen  zai tsinanawa rayuwarka, shine ake cewa lagawu , kuma shine wanda Allah ya yabi bayinsa nagari cewa insun wuce ana yashashshen zance na lagawu basa zama ayi dasu, sai suwuce suna masu kubuta daka gareshi inda yace:

((والذين لا يشهدون الزورا وإذا مروا باللغو مروا كراما)).

Sune wadanda basa bada shaida kan karya abunda basu da masaniya akai, kuma insun wuce ana zance mara amfani sai suwuce suna masu mutunci.

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Aiki da hankali

AIKI DA HANKALI....

Kada ka tambayi maraya ina mahaifinka?

Kada kace wa bazawara me ya kashe aurenki?

Idan zaka taimaki talaka kada ka ce masa, ko kana da bukata?

Wadannan tambayoyi ba su dace da halin mutanen kirki ba...

Duniya makaranta ce. Mutane sune dalibanta...

Rayuwa ita ce dakin karatu, lokaci shi ne babban malami a cikin ta...

Muna haduwa a matsayin baki, sai
kuma mu watse da dai daya...

Kada kace mutane ba sa nema na sai idan suna da bukata. Fitila sai an shiga cikin duhu ake neman ta...

Duniya a tsakanin baka biyu take ( ). Baka ta farko ita ce haihuwa, ta biyu ita ce mutuwa. A tsakanin su kake rayuwa.

Idan ka wuce sai a nade aikinka a
aika maka da shi ya zama abokin jin dadinka ko shan wahalarka acikin rayuwar kabari data lahira...

Ruwan zafin da yake dafa kwai ya yi qwari shi yake dafa dankali ya yi laushi.

Ba ruwan zafin ba ne, dabi'ar
kowanensu. A'a haka mutane suke, wani yau da gobe ke sa ya yi laushi, wani kuma sai ta sa shi ya sandare...

Duk wanda ya ji tsoro zai samu damuwa a zuciyarsa. Amma ban da wanda ya ji tsoron Allah. Shi kam wanda ya ji tsoron Allah zai samu aminci da kwanciyar hankali a zuciyarsa...

Addu'a ba ta faduwa kasa. Ko a baka yau, ko a baka gobe, ko kuma a baka abin da ya fi wanda ka roka...

Idan ba a ba ka ba sam, to akwai wani sharri da za a tunkude maka...

Addu'a makamin mumini ce 'yan-uwa... Don haka muyi ruqo da Addu'a kuma mu dogara da Allah akoda yaushe...

Aikawa wasu da wannan sako domin ka/ki samu ladan tunatarwa daga Allah (SWT)Allah yasa mudace Amiin Amiin ������

Share:

Hukuncin ci ko sha da mantuwa alhali mutum yana azumin nafila

*HUKUNCIN CI KO SHA DA MANTUWA ALHALI MUTUM YANA AZUMIN NAFILA*

Mai azumin nafila ko da gangan yaci abinci ko ya sha abin sha ko yayi jima'i da matarsa to bai da laifi kuma ba zai rama azumin ba. Saboda Annabi (s.a.w.) yana cewa: "Mai azumin nafila sarkin kansa ne, in ya ga dama ya ci gaba da azumi, in ya ga dama kuma ya karya" Albani ya ingantarda shi a sahihul-jami'i hadisi mai lamba ta: 3854.

Haka kuma idan yaci ko ya sha ko yayi jima'i da matarsa da mantuwa alhali yana azumin nafila to yana da zabi guda biyu:

1. In yaga dama yaci gaba da azuminsa saboda duk wanda yaci abinci ko yasha abinsha cikin mantuwa, ko cikin kuskure, ko kuma aka tilasta masa, to babu kaffara ko ramuko akansa. Saboda Sahihin hadisin da Abu Huraira (r.a) ya ruwaito daga Manzon Allah (s.a.w) yana cewa:
"DUK WANDA YA MANTA CEWA YANA AZUMI, HAR YACI ABINCI KO YASHA WANI ABU, TO
YACI GABA DA AZUMINSA. HAKIKA ALLAH NE YA CIYAR DASHI KUMA YA SHAYAR DASHI"
(Jama'ar Maruwaitan hadisi ne suka ruwaito
shi).

Haka kuma Ibnu Maajah da Hakim daga Abdullahi bn Abbas (r.a) daga Manzon Allah (s.a.w) yana cewa:
"ALLAH YA DAUKE MA AL'UMMATA LAIFIN DA SUKAYI CIKIN KUSKURE, DA MANTUWA, DA KUMA ABINDA AKA TILASTA SU AKANSA".

Anan koda kuwa na farillah to zai ci gaba da azuminsa kawai Allah ne ya ciyar ko ya shayar dashi.

2. Ko kuma idan yaga dama sai yaci gaba da cin abincinsa wato ya karya azumin gaba daya saboda shine sarkin kansa kamar yadda hadisi yazo a sama. Anan ana nufin mai azumin nafila kenan, banda mai azumin farillah.

Wallahu a'alam

Share:

Falala da hukuncin kwanciya da tsarki (alwala)

*FALALA DA HUKUNCIN KWANCIYA DA TSARKI (ALWALA).*

A- *FALALAR KWANCIYA DA TSARKI*

@-Wanda ya kwana cikin tsarki,yana kwanane tare da Mala'ika a shinfidarsa, kuma mala'ika yana yimasa addua.

Manzon Allah s.a.w yana cewa:
"Ku tsarkake wannan jiki, sai Allah ya tsarkakeku, domin babu wani bawa da zai kwana cikin tsarki (alwala) face ya kwana tare da Mala'ika acikin mayafinsa,babu wani motsi da bawan zaiyi acikin wani lokaci na dare face yace:
Allah ka gafartawa wannan bawan naka,domin ya kwana cikin tsarki".
#Alban yace Hadisine mai kyau: Saheehut Targheeb

@-Allah yana amsa adduar wanda ya kwanta da tsarki (alwala).
Annabi s.a.w yana cewa:
"Babu wani musulmi da zai kwanta cikin tsarki(alwala) sannan ya tashi cikin dare ya roki Allah alkhairin duniya da na Lahira  cikin dare,face sai Allah ya biya masa buqatarsa".
#Abu Dauda, kuma albany ya ingantasa.
#Ahmad.

@Wanda ya kwanta da tsarki(alwala) kamar mai azumine mai tsayuwar dare.
Amru BN As R.A yana cewa
"Wanda ya kwanta yana mai tsarki kamar mai azumine kuma mai raya dare da ibada".
#Tirmizy da Hakim

B- *HUKUNCIN KWANCIYA DA TSARKI(alwala).*

Malamai suna cewa kwanciya da tsarki ba wajibi bane, Sunnace ta Annabi s.a.w mai hukuncin mustahabbi.
Annabi s.a.w ya kasance idan zai kwanta barci yana yin alwala sannan ya umarci wani daga cikin sahabbansa akan haka.
#Bukhari.

Abinda ake nufin tsarki lokacin kwanciya barci shine alwala saukakkiya wato wadda ba'a wanki uku ba,kuma alwala ba karyewa saboda wani hadasi kamar fitar da iska ko wasa da iyali,saboda alwalace ta barci bata sallaba.
#Duba Umdatul qary.

NB:
Kuma mutum zai yi wannan alwala ko yana da janaba.
Domin an tambayi nana Aisha R.A ya Annabi s.a.w kwanci idan yana da janaba sai tace yakanyi dayan abubuwa ukku:
-ko yayi wankan janaba sai yakwanta ko
-Yayi alwala ko kuma
-yayi Taimama.
#Saheehul Jami'I.

Allah ne mafi sani.

Allah ka bamu ikon kiyaye, amin

Share:

Shin ana ramawa wanda ya mutu azumi na ramadan ??

*SHIN ANA RAMAWA WANDA YA MUTU AZUMI NA RAMADAN??*

الحمد الله وكفى وصلى الله على محمد وآله وصحبه وسلم،

Amsa:An yiwa shaeik uthaimeen {Rahimahullah} irin wannan tambaya sai ya amsa dacewa,
Mara lafiya matukar yana cikin rashin lafiya a zumi bai wajaba akan saba, idan ya mutu kafin ya warke, ya mutu kafin yazama wajibi akansa, baza'a ciyar a madadin saba domin ciyarwa a matsayin azumi take, idan azumi bai zama wajibi ba, to mamadin sama bai zama wajibiba,Allah madaukakin sarki yace:
(ومن كان مريضا أو على سفر فعدة من أيام أخر، يريد الله بكم اليسر ولايريد بكم العسر ولتكملو العدة ولتكبر الله على ما هداكم ولعلكم تشكرون،)
Duk wanda yakasance mara lafiya acikinku ko yana halin tafiya, to ya rama awasu kwanakin daban bana ramazan ba, Allah yana nufin saukine a gareku, ba yana nufin quntatawa agareku bane, danku cika kwanakin dan kuma ku godewa Allah abisa abun da ya shiryar daku, ko zaku zamto masu yawan godewa,

Tabbatar  dalili da wananana aya shine idan bai samu dama ba babu komai akansa, saboda Allah ya sanya wajabcin ramuwar azumi a kwanaki nagaba, shikuwa bai kaiba sai yarasu, idan ya mutu kafin yakai zuwa garesu hakika ya mutu kafin lokacin wajabci yazo, sai yakasance kamar wanda ya mutu kafin shi gowar watan ramazan, bai wajaba aciyar masaba sobada watan ramazana da zaizo agaba, koda ya mutu ramazan yana gobe kamawa.

Amma a hadisi manzan Allah salallahu Alaihi wasallam yace, (Duk wanda ya mutu da azumi akansa to waliyyinsa sai yayi masa, bukhari da muslim,
Abunda hadisin ke magan akai shine wanda ya mutu yana da ramuwar azumi akansa, to waliyyinsa sai ya rama masa, ba wanda ya mutu acikin watan azumin ba, idan bazai masa azumi ba to ya ciyar kowacce rana miskini daya, iya adadin azumin dake kansa bai rama ba,

Abun nufi wanda ya mutu babu azumi a kansa baza ai masa azumi ba, mun sani cewa idan mara lafiya cuta taci gaba ajikin sa, azumi bai wajaba akansa ba, ko ramuwa a halin rashin lafiyarsa,

Amma wanda ya mutu ana cikin azumi, to waliyyinsa bazai karasa masa zumiba kuma bazai ciyar ba, domin mara lafiya idan ya mutu aiyukansa sun yanke, kamar yanda Annabi sallahu alaihi wasallam, yafada ( Idan mutum ya mutum ayyukansa sun yanke sai abubuwa uku sadaka mai gudana, ko ilmin daya bari ake amfana dashi, ko da nagari dazai dungai masa addu'a, abisa wannan baza,a rama masaba hatta na ranar daya mutu

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Shin meke sa mace tanayin al'adarta wata-wata amma wani lokaci sai bayan wata biyu ko uku kuma ba matar aure ba ??

*SHIN MEKE SA MACE TANAYIN AL'ADARTA WATA-WATA AMMA WANI LOKACI SAI BAYAN WATA BIYU KO UKU KUMA BA MATAR AURE BA*

الحمد لله الذي أنزل على عبده الكتابة ولم يجعله عواجا، والصلاة والسلام على أشراف الأنبياء والمرسلين، سيدنا محمد وعلى آله وصحبه ومن ولاه،

Allah madaukain sarki mai ikone akan komai, kuma yakanyi halitta yanda yaso kuma yakan saukarwa da bawansa jarrabawa akowane lokaci dayaso, wani lokacin dan yajarraba bawansa, wani lokacin danya kankarewa bawansa wani laifi da ya aikata asanadin wannan cutar, yakanyi hakanne tahanyoyi daban daban,

Alal hakika abunda yakesa mace canjawar lokacin ala'ada akwai ababe dasuke faruwa wanda suke sabbaba hakan musamman ga wacce ba matar aure ba, sune abubuwa guda biyu cikin su ake samun daya,

▪Shine akwai matan da haka Allah yayisu sukan yi wata uku ko biyu batare da sunyi al,ada ba kuma basu da aure, haka halittar su da Allah ya yisu da ita take, wannan kuma ba'abun damuwaneba.

▪Abu nabiyu dake kawo wannan shine rashin lafiya, ke sa mace tana al'ada wata sai ta koma wata uku wasu ma har shida, lallai yakamata ki tsananta bincike kiga likitoci, ko kuma masana akan abun da yashafi shafar shaidanu, ko masu aurar mace surike mata jini, lallai bazaki gane awane aji kikeba sai anyi bincike in rashin afiyace sai anemi magani dan samun lafiya Allah madaukakin sarki ya taimakemu.

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Monday 7 November 2016

Yaya hukuncin sallar wanda yasha rake bai kuskure bakin saba ??

*YAYA HUKUNCIN SALLAR WANDA YASHA RAKE BAI KUSKURE BAKIN SABA*

الحمد لله الذي شرفنا بالإسلام وجعلنا خير أمة أخرجت للناس، صلى الله على محمد وآله وصحبه وسلم،

Amsa: cin wani abu ko sha, ko taba wani abu, ko sun batar mace, ko tabata dan sha'awa, baya karya alwala, balle yai tasiri a sallar mutum dan haka babu komai ga wanda yaci ko yasha yai sallah batare da ya kuskure bakin saba, saifa idan abunda yaci naman rakumine to wannan dole sai ka kuskure bakinka da nassin  hadisin Manzan Allah salallahu Alaihi wasallam wannan ya tabbata.

Amma kuma kuskure baki  bayan kaci ko kasha sunnah ne kuma abun sone, saboda dalilai da suka tabbatar da hakan,.

Daka Abdullahi dan Abbas Allah yakara musu yarda, Manzan Allah sallahu Alaihi wasallam ( ya sha nono sai yabukaci akawo masa ruwa ya kuskure bakinsa bayan yayi alwala, sai yace yana da naso, ma'ana ragowar dandanon nazama abaki,

Imamul nawawi yace: acikin wannan hadisin akwai mustahabbanci kuskure baki bayan anci ko an sha, bayan alwala, saboda abunda yaci ko yasha rogowarsa zai iya rage masa abaki,

Da kuma hadisin nu'uman wanda manzan Allah a yakin khaibar bayan sunje wani gari "suhaba'i" can wani garine dake gangaren khaibar, yai umarni akawo musu wani abunci ba,a samu ba sai assaweeq sai sukaci bayan la,asar sai sukazo yin sallar magriba, sai Annabi ya kuskure bakinsa sai sahabbai ma suka kuskure bakinsu,

acikin wannan hadisi akwai mustahabbanci kuskure baki idan akaci ko aka asha bayan alwala, duk cewa abuncin saweeq bashi da naso, amma dan ragowarsa dake tsakanin hakora da sauran guraren nabaki su zauna abakinsa.

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Menene hukuncin namiji mai biye biyen mata bayan yana da aure iyalinsa tana iya kokarinta wajan bashi hakkinsa ??

*MENENE HUKUNCIN NAMIJI MAI BIYE BIYEN MATA BAYAN YANA DA AURE IYALINSA TANA IYA KOKARINTA WAJAN BASHI HAKKINSA.?*

الحمد لله والصلاة والسلام على محمد وآله وصحبه وسلم،

Amsa: Lallai wannan mijin bai kyauta ba kuma abun da yake aikatawa hadarine mai girma agareshi anan duniya da kuma lahira, kuma abun bakin cikine yakamata yagane bashi kadai keda hakki akanki ba, kema kina da hakki akansa ya nuna kulawa da kishi dakuma barin abunda duk zaibata miki rai, kozai saki damuwa matukar wannan abun basabon Allah bane.

Shine wanda shari'ar musulunci take kira da dayyus, wato sakarai shasaha wanda baya kishin matarsa ko kannensa mata ya kyalesu sakaka suna abunda sukaga dama, ko kuma baya kishin matarsa kwata kwata, kawai yadauki matarsa amatsayin mai dafa masa abunci ba ruwansa, zaije yaita mu'amala da wasu matayen, wannan sharrine mai girma, domin irin wadannan matayen ne in ba,a samu mai tsoran Allah ba, itama sai tafada wasu dabi'u da ababe marasa kyau, akwai wadanda tsabar lalacewa sune suke baiwa matayan nasu dama cewa suma suna iya yin mu'amala da kowa, hakika matarka tanada daraja da mutunci domin itace suturarka kamar yanda kur'ani yanuna, ba daidai bane kabarta gida kaje kana biyewa wasu akwararo, kuma ya kamata kasani wadannan  wadanda kake biyewa bawani abu sukafi taka matarba, kai takama tafisu kawai saboda su sun tube rigar mutunci suna fito na fito da Allah ne har kake ganin wani abu atare dasu, domin sudin kamar shaddar kasuwa suke kowa zai hausu yaikashi, lallai wanna miji naki yakamata yaji tsoran Allah yatuba yadena, kuma kici gaba da rokon Allah Allah ya shiryar miki dashi, sannan kibi duk wasu hanyoyi na hikima da fasaha kinunar masa abunda yake yana matukar kona miki rai, kuma kitunatar dashi lallai wannan mugun aikine yake, inda hali kihada da abokansa iyayensa da duk wanda kikasan yanajin nauyinsa danya dena wannan dabi,a yadawo gareki, inkinbi duk wadannan hanyoyin bai daina ba, kinemi taimakon Allah kawai araba aurenku Allah ya musanya miki da mai kishinki mai kiyaye addinin Allah madaukakin sarki,

Hadisi yazo daka manzan Allah sallahu Alaihi wasallam, daka abdullahi dan umar Allah  yakara masa yarda yace manzan Allah yace, ( mutane uku Allah yaharamta musu aljannah, wanda ya dawwama yana shan giya har yamutu, dakuma maiyawan sabawa iyayensa, dakuma dayyus sakaran dayake tabbatar da barna acikin iyalinsa baya kishinsu, ) Imamu Ahmad.

Malam haisami yace: acikin mu'ujamul zawa'id acikin hadisin akwai rawin da ba,a ambataba, amma sauran mutanen dasuka ruwaito shi dukansu amintattu ne, Dabarani ya ruwaito daka Ammar bin yasir manzan Allah salallahu Alaihi wasallam yace:

(Mutane uku, bazasu shiga aljannaba har abada, Mace mai kamanceceniya da maza, dakuma wanda yake shan giya har yamutu, da dayyus sokwan da baya damuwa da wanda yake shiga wajan ahlinsa, baya kishinsu.

A bisa wannan duk wanda yai duba da hadisn farko duk da hadisi nabiyu akwai  rauni acikin ruwayarsa, zai fahimci dayyus shine wanda yake kyale barna acikin iyalinsa tana wakana kuma baidamu ba, ko yake bada kofar da kowacce irin barna zata iya faruwa akan iyalinsa, domin duk wanda bai damu da matarsa ba baya kishinta yana bin wasu awaje, hakika yakyale babbar kofa ta faruwar fitina acikin iyalinsa. Sa'annan kuma wadda keda miji irin wannan kuma ta tabbatarda yana wannan biye-biyen matan, ba zargi bane to sai ta fara masa nasiha cikin hikima da kuma rokon Allah ya shiryar mata da mijinta da ci gaba da gyara jikinta sosai ta hanyoyin da suka halatta ( maganar gaskiya da yawan matanmu na arewacin qasarnan suna wasa da gyaran jikinsu ) da yawan mazaje shi yasa shaidan ke samun galaba akansu sai na wajen suke basu sha'awa kuma alhali ba komai suka fi na auren ba kawai su na auren basa gyara jikinsu ne, to idan tabi duk wadannan matakan tayi-tayi yaqi dainawa to sai ta janyo magabata a cikin lamarin, idan yaqi bari to zata iya neman rabuwa dashi Allah ya musanya mata da wani nagari saboda yana iya dauko musu wani ciwo can wajen fasikancin nasa. Allah ya kiyaye!

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Ya halatta mutum ya auri matar da kanen babansa ya taba aura??

Assalamu alaikum
Malam Tambaya na shine ya halatta mutum ya auri matar da kanen babansa ya taba aura?
Kuma miye hukuncin sa.

_*AMSA:*_
*******

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،

Matar da kanen babanka ya taba Aure, bã ta cikin jerin mata 7 da Allah ya haramta aurensu ga namiji mai alãqa dasu.
Acikin suratun Nisaa'i, ayah ta 23, Allah yana cewa;

ﺣُﺮِّﻣَﺖْ ﻋَﻠَﻴْﻜُﻢْ ﺃُﻣَّﻬَﺎﺗُﻜُﻢْ ﻭَﺑَﻨَﺎﺗُﻜُﻢْ ﻭَﺃَﺧَﻮَﺍﺗُﻜُﻢْ ﻭَﻋَﻤَّﺎﺗُﻜُﻢْ ﻭَﺧَﺎﻻَﺗُﻜُﻢْ ﻭَﺑَﻨَﺎﺕُ ﺍﻷَﺥِ ﻭَﺑَﻨَﺎﺕُ ﺍﻷُﺧْﺖِ ﻭَﺃُﻣَّﻬَﺎﺗُﻜُﻢُ ﺍﻟﻼَّﺗِﻲ ﺃَﺭْﺿَﻌْﻨَﻜُﻢْ ﻭَﺃَﺧَﻮَﺍﺗُﻜُﻢ ﻣِّﻦَ ﺍﻟﺮَّﺿَﺎﻋَﺔِ ﻭَﺃُﻣَّﻬَﺎﺕُ ﻧِﺴَﺂﺋِﻜُﻢْ ﻭَﺭَﺑَﺎﺋِﺒُﻜُﻢُ ﺍﻟﻼَّﺗِﻲ ﻓِﻲ ﺣُﺠُﻮﺭِﻛُﻢ ﻣِّﻦ ﻧِّﺴَﺂﺋِﻜُﻢُ ﺍﻟﻼَّﺗِﻲ ﺩَﺧَﻠْﺘُﻢ ﺑِﻬِﻦَّ ﻓَﺈِﻥ ﻟَّﻢْ ﺗَﻜُﻮﻧُﻮﺍْ ﺩَﺧَﻠْﺘُﻢ ﺑِﻬِﻦَّ ﻓَﻼَ ﺟُﻨَﺎﺡَ ﻋَﻠَﻴْﻜُﻢْ ﻭَﺣَﻼَﺋِﻞُ ﺃَﺑْﻨَﺎﺋِﻜُﻢُ ﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﻣِﻦْ ﺃَﺻْﻼَﺑِﻜُﻢْ ﻭَﺃَﻥ ﺗَﺠْﻤَﻌُﻮﺍْ ﺑَﻴْﻦَ ﺍﻷُﺧْﺘَﻴْﻦِ ﺇَﻻَّ ﻣَﺎ ﻗَﺪْ ﺳَﻠَﻒَ ﺇِﻥَّ ﺍﻟﻠّﻪَ ﻛَﺎﻥَ ﻏَﻔُﻮﺭﺍً ﺭَّﺣِﻴﻤﺎ.

*Fassarar Hausa.*
_An haramta muku uwãyenku da ´yã´yanku da ´yan uwanku mãtã da goggonninku da innoninku da ´yã´yan ɗan uwa da ´yã´yan ´yar uwa da uwãyenku waɗanan da suka shãyar da ku mãma da ´yan uwanku mãtã na shan mãma da uwãyen mãtanku da agõlolinku waɗanda suke cikin ɗãkunanku daga mãtanku waɗanda kuka yi duhũli (Jimã'i) da su, kuma idan ba ku yi duhũli da sũ ba, to, bãbu laifi a kanku, da mãtan ´yã´yanku waɗanda suke daga tsatsonku, kuma kada ku haɗa tsakanin ´yan´uwa biyu mãtã, fãce abin da ya shige. Lalle ne, Allah Yã kasance Mai gãfara ne Mai jinqai._

Anan, haramcin Aure ya shafi har da kishiyoyin mamarka da matar da ta shayar dakai mama, da wacce aka shayar daku tare, da kuma duk wata yarinyar da wannan matar ta shayar mama.

_*HUKUNCI*_
Amma ita waccan matar da kanen babanka ya saka, ya halatta agareka ka aureta idan kana so, babu haramci a hakan.

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_

Share:

Menene banbanci tsakanin girman kai da kuma jiji dakai meye matsayin maiyinsu a musulunci

*MENENE BANBANCI TSAKANIN GIRMAN KAI DA KUMA JIJI DAKAI MEYE MATSAYIN MAIYINSU A MUSULUNCI.*

الحمد الله الذي هدان للإسلام وما كنا لنهتدي لولا أن هدان الله، والصلاة والسلام على محمد وآله وصحبه وسلم.

Girman kai da kuma jiji dakai, dukansu dabi'une munana wanda musuluci ya yakesu, kuma dabi'u ne ababen zargi masu kai mutum ga halaka, cikin kankanin lokaci, banbaci dake tsakanin su kadanne shine:
Shi girman kai shine kadunga ganin fifiko akan wani, kadunga jin kafi wane kai abu kaza kafi karfin ko kawuce matsayin wane kafi karfin saurarensa dadai makamantan haka.

Shima jiji dakai shine kadunga  jin kana da wani abu da waninka bashi dashi.

Dukansu munane wadanda suke dauke bawa daka godewa Allah, zuwa godewa kai dajin wayanka ko iyawarka sukema abu, suna hanaka yaban Allah dagode masa ka koma yaban kanka, dakuma qin kankantar da kanka ga mahalicci, da ruduwa dakai dakin  girmama mutane da sanin matsayinsu izuwa hantarar su, da danne hakko qinsu.

yana daka illolin jiji dakai suke haifarwa akwai rusa ayyuka kyawawa da kuma boye masu kyau, dakuma janyo zarge zarge.

Hukuncin jiji dakai haramunne domin nau'ine na shirka,shaikul islam ibnu taimiyya yace : ( Sauda yawa riya tana kusanci da jiji dakai, ita riya tana babin shirka da halittu, shikuma jiji dakai yana babin shirka dakai, wannan shine halin mai girman kai, Mai riya bai tabbatar dafadin Allah madaukakin sarki ba
إياك نعبد،
Mai jiji dakai kuma bai tattabatar, da fadin Allah madaukin sarki,
وإياك نستعين،
duk wanda yatabbatar da fadin Allah إياك نعبد zaifita daka riya
wanda yatabbatar da fadin Allah
وإياك نستعين،
zai futa daka jiji dakai.

Jiji dakai abun zargine acikin alqur,ani da sunnah Allah madaukakin sarki yace: ( ويوم حنين إذ أعجبتم كثرتكم فلم تغن عنكم شيئا )
Daranar yakin hunaini lokacin dayawanku ya burgeku kuma bai tsinana muki komai ba yawan naku.

Abdullahi dan masu' ud yace halaka tana cikin ababe biyu, debe tsammani daka Allah dakuma jiji dakai.

jiji dakai yakan kai maiyinsa zuwa ga kafirci da futa daka musulunci kamar yanda shaidan yai alfahari da asalinsa da ibadar sa, yaiwa Allah girman kai.

Ibnu qudama yace: kasani jiji dakai yakan kawo girman kai domin yana cikin dalilan dake kawo girman kai, acikin girman kai kuma akwai masifu dayawa akwai tsakanin haittu da kuma tsakaninka da mahaliccinka

Ababen dazaka gane maijiji dakai sune

•Kin gaskiya mayar da ita da hantarar mutane
•Raina kowa
•Rashin shawartar masu hankali da manya acikin al'amura
•Rangwada atafiya ji da isa
•Ganin girman biyayyar da kakewa Allah dakuma ganin yawanta
•Alfahari da ilimi da gori dashi
•Alfahari da dukiya da dangi da kyawun halitta
•Raina kokarin maluma masu tsoran Allah
•Dawwama akan kuskure
•Karancin sauraron ilmi ko mika wuya ga masu shi dalazimtarsu
•Hantarar masu sabo
•Manta zunubai da rainasu ganin karancin su
•Sabawa mutane dagangan danjin isa

Abubuwan da suke janyo jiji dakai

√Jahilci
√karancin tsantseni da tsoran Allah
√Raunin jin cewa Allah yana tare dakai yana kallanka
√Karancin wadanda zasuyiwa mutum nasiha
√Mummunar niyya
√Yawan jindadin yabon mutane koyin abun dan samun yabonsu dakuma taimakon shaidan Akan haka
√Fitunwa dasan duniya dabin san zuciya
√Karancin tunani
√Karancin godewa Allah
√Karancin Ambaton Allah
√ Rashin tadabburin Alqur'ani da kuma hadisai
√Amintuwa da azabar Allah da dogara da Afuwarsa da gafarar sa kadai.

Maganin sa shine tuna ni'imomin Allah dakuma tuna yanda mutum yake abaya kafin yakai matsayin dayake na yanzu, dakuma tuna tarihin Al'ummatan da suka shude da karanta rayuwar manzan Allah salallahu Alaihi wasallam da sahanbansa.

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Me yakamata wanda yake tunanin ace yazama kirista??

*ME YAKAMATA WANDA YAKE TUNANIN ACE YAZAMA KIRISTA*

الحمد لله والصلاة والسلام على من لا نبي بعده.
Alal hakika raunin imani shine ke kawo wannna tunani dakuma shedan, abunda yakamata ka dunga yi shine neman tsarin Allah daka shaidan kamar yanda Allah madaukakin sarki yace:

(وإما ينزغنك من الشيطان نزغ فاستعذ بالله إن هو السميع العليم)
Duk lokacin da shaidan yakawo maka wata fizga hari na mummunan aiki ko tunani kanemi tsari da Allah

Yazo acikin hadisi ingantacce manzan Allah salallahu Alaihi wasallam yace: shaidan zai zowa da yanku yadunga rayamar azuciya cewa wanene yahalicci kassai yace Allah wanenene ya halicci sammai yace Allah wanene yahalicci kaza yace Allah karshe sai ya dunga kawo cewa shi Allah kuma waya halicce shi, Annabi yace da kaji haka kacanjawa zuciyarka wani abun daban kanemi tsari daka Allah.

Hakika ni'imar musulunci ni'imace mai girman gaske, dan haka bazai taba yiyuwa shaidan ya kyaleka haka kawai kazauna lafiya ba, sai ya dunga kawo maka hari dare darana

Amma kakiyaye karka sake ka furta hakan inka furta malamai sukace kazama kafirin.

Sannan ka yawaita tuba zuwa ga Allah idan kasan kana tare da mutanen banza ka gaggauta canzasu da mutane nagari, idan kuma gurine kake tasirantuwa dashi ka kaurace masa, ka yawaita karatun alqur'ani da sauraron sa dajin  wa'azuzzuka da halartar guraren da duk ake karantar da musulunci.

Sannan ka yawaita addu'ar manzan Allah salallahu Alaihi wasallam.

اللهم يا مقلب القلوب ثبت قلوبي على دينك،

Ya Allah mai jujjuya zukata ka tabbatar da zuciyata akan addininka

In sha'allahu zaka kubuta daka abunda kake ji na sha'war wani addini koma bayan musulunci.

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*Tambayoyin*_ _*Musulunci*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Nasha nonon matata, yaya auren mu??

*NA SHA NONON MATATA, YA YA AURENMU?*

*_Tambaya?_*

Don Allah Malam ya matsayin mutumin da ya sha nonon matarsa,  ya aurensu  yake?

*_Amsa:_*
Wa'alaykumussalam,

To dan uwa, Allah Madaukakin Sarki ya halatta maka jin dadi da dukkan bangarorin jikin matarka, in ban da dubura ko kuma saduwa da ita lokacin da take haila,  don haka  ya halatta ka tsotsi nononta mutukar babu ruwa a ciki, amma idan akwai ruwa a ciki, to Malamai sun yi sabani akan halaccin hakan zuwa  maganganu guda biyu :

1. Ya halatta, saboda kasancewar nonon da yake haramta aure shi ne wanda aka sha kafin yaro ya cika shakaru biyu,  saboda fadin Annabi s.a.w. "Shayarwar da take haramtawa, ita ce wacce yaro ya sha saboda yunwa" , Bukhari lamba ta : 5102.

Ma'ana lokacin da ba zai iya wadatuwa ba daga nono, saboda shi ne abincinsa, shi kuma wannan ya faru ne bayan mutum ya girma don haka ba zai yi tasiri ba wurin haramta aure,  wannan ita ce maganar mafi yawan Malamai.

2. Bai halatta ya sha ba, saboda ko da yaushe mutum ya sha nonon mace to ta haramta a gare shi, domin Annabi s.a.w. ya  umarci matar Abu-huzaifa da ta shayar da Salim,  don ta haramta a gare shi, kamar yadda Muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 2636, tare da cewa a lokacin Salim ya riga ya girma,  wannan sai yake nuna cewa idan babba ya sha nono to zai yi tasiri wajan haramcin aure .

Zancen da ya fi karfi shi ne ya halatta miji ya sha nonon matarsa, sai dai rashin shan shi ne ya fi, saboda fita daga sabanin malamai yana da kyau, don neman Karin bayani duba : Bidayatul-mujtahid 2\67

Allah ne mafi sani.

31/10/2014

*_Dr Jamilu Yusuf Zarewa_*

Daga: *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*

Share:

Monday 31 October 2016

Kalaman hikima ba kowane zai fahimcesu ba sai mai hikima

KALAMAN HIKIMA BA KOWANE ZAI FAHIMCESU BA SAI MAI HIKIMA.:_
.
Tunda Ake Mutuwa a Duniya Mutum Biyu(2) Ne Kawai Suka Mutu. Daga Wanda Ya Mutu Ya HUTA Sai Wanda Ya Mutu aka HUTA!
.
Duk Haihuwar da Ake a Duniya MutumBiyu (2) Ne Kawai Ake Haihuwa.
DagaWanda Aka Haifa Ya Zama Alkhairi Sai Wanda Aka Haifa Ya Zama Sharri!
.
Duk Yawan Mutanen Duniyar Nan Abinci Kala Biyu (2) Muke Ci. Ko Dai Kaci Abinci ta Hanyar Halal Ko Kuma Kaci Shi Ta Hanyar Haram!
.
Idan Ka Tuna Mutum A Zuciyarka Dole ACikin Abu Biyu (2) Kayi Guda (1). Ko Dai Ka Tuna Alkhairinsa Ko kuma Ka Tuna Sharrinsa!
.
Duk Mutanen Duniya Kowannen Mu Yana Gina daya Daga Cikin Wadannan Gidaje Guda Biyu (2). Daga Wanda Zaiyi Gini a Aljanna Sai Wanda Zaiyi Gini a Cikin wuta!
.
Ya Allah Kasa mu gina namu Gida a cikin Aljanna Firdaus, Ameen.

Share:

Aqidar shi'a dangane da makka da madina

*AQIDAR SHI'A DANGANE DA MAKKA DA MADINA*

الحمد لله والصلاة والسلام على محمد وعلى آله وصحبه وسلم،

Aqidar shi'a dangane da makka da madina aqidace wacce kafirai ma sunfisu saukakawa akai, dan duk kafircin kafiri yasan wadannan gurare suna da falala da daraja,ruwaya daka littafinsu wanda babban malaminsu kuma hujja a'adinin nasu yaruwaito acikin littafinsa

Daka abu baseer daka daya daga cikinsu, yace ((Mutanan makkah sun kafircewa Allah afili, Mutanan madina sunfi mutanen makkah kafirci da lalacewa, sau saba'in wannan magana tana cikin usul kafiy 2/410

Yace dangane da "sham" siriya kenen (( kar kuce ma'abota "sham" sai dai kuce ma'abota zalunci, ma'ana bazaka ce mutanan "sham" ba saidai kace mutanan "zalunci da danniyi, saboda tsabar kiyayyyarsu da sahabbai, sukace Wai Allah yatsine musu tahanyar Annabinsa Dauda, ya maida su birai da aladu,  Biharul Anwar 60/208

Sukace tahanyar Ja'afaru ssadeq, Allah yakara masa yarda, karyane yafadi wannan magana, kawai sun jinginata gareshine, (( Mutanan "shaam" sunfi rumawa arna sharri, mutanen  madina sunfi mutanen makka sharri, mutanan makka sun kafircewa Allah afili, Usul kahfy 2/409.

Wannan shine dalilin da yasa Iran ta hada kai amunafunce da America da sauran kafurai suke yakar musulunci musamman akasashen Iraqi da Afganistan.

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Matsalar saurin kawowa (wato rashin dadewa lokacin jima'i)

*MATSALAR SAURIN KAWOWA ( WATO RASHIN DADEWA LOKACIN JIMA'I)*

Rashin sanin hakikanin gaskiyar magana dangane da lokacinda namiji yake iya dauka kafin yayi inzali (wato irin tsawon lokacin) ya kasance abu mai matukar damuwar da yawa daga cikin ma'aurata a wannan zamani. Ya kasance yana saka mazaje da yawa cikin damuwa da rashin walwala sosai gun iyalansu wanda hakan yasa suke ta neman magunguna haukace daga masu bayarda irin wadannan magungunan na gargajiya; ba kadan yake laqumewa mazaje kudi ba. Wannan matsalar tana kasancewa silar son kashe aure ga wasu matan da sunan suje su auri masu daukar tsawon lokaci domin biya musu bukatarsu, wasu matan kuma har yakan zamo silar sabon Allah garesu ta hanyar neman maza a waje wai duk da sunan mazansu basa biya musu bukata. Kuma duk wannan damuwar da wahalolin suna faruwa ne saboda irin  yadda mutane suke karantawa a mujallu, social media, littafai e.t.c cewa maza suna daukar tsawon mintuna talatin (30) zuwa sama suna jima'i kafin suyi inzali( kafin maniyyi ya fito musu) wasu kuma suna jin labarai ko gani ne a irin bidiyoyin batsa da Yahudawa maqiya Allah suke shiryawa.

To dan uwa mai cike da damuwa ganin cewa baka daukar tsawon lokaci yayin saduwa da matarka ko kuma malama mai ganin cewa mijinki baya da lafiya kike damuwa duk ku kwantarda hankulanku wancan bayanin dake a sama na mintuna talatin zuwa sama ba gaskiya bane, bayani zaizo daga baya. Abinda bincike daga masana kwararru a wannan fannin ya tabbatar shine:

1. *Mafi yawan maza suna daukar tsawon mintuna 4 zuwa 5 ne ko kuma 5 zuwa 7*.  Kuma wadannan mazajen lafiyayyu ne daram.

2. Qalilan sosai ne daga cikin maza *suke iya daukar mintuna 12 zuwa sama suna saduwa da matansu bayan shigarsu*.

3. Su kuma wadanda wannan cutar ta saurin kawowa ke damu to *suna kawowa ne irin seconds 15 zuwa  seconds 30 wato dai kasa ga minti 1 kacal bayan sun shigi mace. Wasu ma suna inzali ne tun kafin su shigi matan nasu*. Kuma da zaran sunyi inzali kafin su sake mayarda karfinsu (kafin gabansu ya qara mikewa) wani aiki ne babba.

Sai kuma maganar cewa mazaje suna daukar mintuna 30 zuwa sama ba za'a ce ba'a rasawa ba amma dai mafi yawancin hakan ciwo ne. Sai kuma wadanda suke ji daga masu tallar magunguna, su kuma wadannan suna yi ne dan tallar maganinsu. Wadanda kuma suke kalla a bidiyoyin batsa irin wadanda yahudawa maqiya Allah suke yadawa shi kuma wannan abinda wani fasiqi wanda shi Mai shirya irin wannan batsar ne ya gayawa masu wannan binciken shine *Yadda mutane suke ganin bidiyoyin ba haka abin yake ba. Suna iya daukar watanni suna hada bidiyon. Yace ya kan yiwu shi fasikin wanda ake nunowa yana fasikanci da macen yayi inzali kusan sau biyar ko goma duk a cikin bidiyo guda amma sai su dinga katse wuraren sai subar na karshen kawai. Misali suna iya suzo idan suka fara fasikancin nasu idan yayi inzali sai su tsaya sai kuma wani lokaci idan zasu ci gaba sai su sake dorawa daidai wurinda suka tsaya; kalar kwanciya (position), wurinda suke fasikancin, kalar kaya da komai dai duk iri daya kamar yadda ake hada fim, haka kuma idan ya qara inzali sai su dakatarda daukar sai kuma lokacinda zasu ci gaba hardai sukai tsawon lokacinda suke bukatar kaiwa, sa'annan kuma muna ba jarumman namu kwayoyin kara kuzari*. Kunga kenan indai hakane to suna iya nuna bidiyo mai tsawon awoyi amma shi mai kallon fasikancin sai yaga kamar duk tun lokacinda suka fara fasikancin yine suke bai kawo ba. *Ku kura da kyau wannan fa bincike ne kuma ni na kawo wannan bayanin ne domin wayarda kai tare da kwantarwa da yawa daga cikin yan uwa maza masu ganin cewa kamar basu da lafiya da mata masu ganin cewa mazansu basu da lafiya hankulansu saboda irin yadda suke karantawa ko gani a irin wadannan hanyoyin dake a sama. To kunji yadda suke shirya wannan fasikancin.*

To wasu daga cikin masu rubuce-rubuce akan wannan matsalar wadanda mafi yawancinsu masu tallar magunguna ne suna amfani da irin wannan bayanin ne ba tare da sanin hakikanin gaskiyar lamarin ba domin tallar hajojinsu. Wasu ma sun sani kawai dai dan su tallata kayansu ne ta yadda mutum zai ga lallai baida lafiya bari ya siya maganinsu.

Saboda haka dan uwa mai ganin tamkar baka da lafiya ko wadda take ganin mijinta baya da lafiya har take kokarin rabuwa dashi ko neman wani a waje saboda irin wancan bayanin na karya to ku kwantarda hankalinku karya ne. Haka kuma wanda ma yake fama da wannan rashin lafiyar wato saurin inzali din (rashin dadewa ana saduwa) wato baya iya daukar ko minti daya kacal yana saduwa da iyalinsa to sai ya garzaya asibiti ko wajen masu islamic medicine akwai magunguna kuma suna dan tasiri sa'annan kuma ga wasu 'yan hanyoyi masu taimakawa sosai ga masu wannan rashin lafiyar, harda ma wadanda ke irin mintuna 2 ko 3 haka to duk wannan bincike ya nuna zasu samu ci gaba su haura hakan idan suna bin wadannan hanyoyin. Ga hanyoyin kamar haka:

1. Mutum ya yawaita motsa jiki (exercise)

2. Cin lafiyayyen abinci mai gina jiki da qara lafiyar jiki da kuma yawan cin 'ya'yan itatuwa (Kawai dai aje asibiti domin samun gamsasshen bayani)

3. Yin wasa da gaba a fitarda maniyyi aqallah awa daya kafin fara jima'i da matarka ( *A lura wannan bincike ne a kimiyyance to kuma munsan cewa a musulunce yin wasa da gaba har a fitarda maniyyi haramunne. To amma mafita itace sai ka saka matarka tai maka wannan aikin aqallah awa daya kafin ku fara kaga zaka iya sanyata tai maka bayan kayi inzalin sai ku shiga wanka tare ta yadda dai zaku iya bata lokaci har ayi awar kuna tare kafin fara jima'in, kaga wannan ma duk karin soyayya ne*)

4. Matarka ta dinga yi maka wasa da azzakarinka har sai kaji ka kusan kawowa sai ta dakata, sai gabanka ya tafi kwantawa sai kuma taci gaba ku yawaita yin haka, shima masana sunce yana taimakawa sosai wajen qara tsawon lokaci yayin saduwa.

5 Ku dinga yin wasa sosai da matarka gabanin ka shigeta ta yadda koda kayi  saurin inzalin to ita matar zata iya samun biyan bukatarta daga wadannan wasannin.

6. Haka kuma akwai irin taimakawar da ita macen zata dinga yi yayin saduwar. Kamar lokacinda kuke jima'i idan kaji ka kusa kawowa sai ka cire ita matar tayi sauri ta dan matse kan azzakarinka ta yadda sha'awarka zata dan gushe. Haka kuma kasancewar matarka a samanka shima wannan yana taimakawa sosai. (Wannan dai idan mai fama da rashin lafiyar yaje asibiti duk zai samu cikakken bayani)

To da yardar Allah masana wannan fannin sunce idan mai fama da wannan rashin lafiyar yana yin haka zai samu canji sosai. Haka kuma wadanda suke yin irin mintuna 2 ko 3 haka suma idan suna bin wadannan matakan to lokacinsu zai karu sosai kamar zuwa 4 zuwa 5 haka. Allah ya kara mana lafiya da abinda lafiya ke bukata.

+2348164884055.
+2347068043652.

*��Tambayoyin Musulunci��*
           *WhatsApp Group*

Share:

Sunday 30 October 2016

Ya hukuncin wanda yake sallah wasu raka'o'i yayi qabdu wasu kuma yayi sadalu??

YA HUKUNCIN WANDA YAKE SALLAH WASU RAKA'O'I YAYI QABDU WASU KUMA YAYI SADALU

الحمد لله على المبعوث رحمة للعالمين صلى الله عليه وعلى آله وصحبه ومن سار على نهجهم إلى يوم الدين

Alal hakika yasabawa koyarwar manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam, domin Allah ya umarcemu dakoyi da Annabin tsira muhammad salallahu Alaihi wasallam, cikin dukkan al'amuranmu narayuwa da addini da zamantakewa inda yace:

(لقد كان لكم في رسول الله أسوة حسنة لمن كان يرجوالله واليوم الآخر) الأية
Hakika abun koyi kyakkyawa yakasance agareku cikin al'amuran manzan Allah, ga wanda yake fatan samun yardar Allah da kuma tsira ranar alkiyama.

Shi kuma manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam ya umarcemu da muyi sallah kamar yanda aka ruwaito mana yana yi  inda yace:

(صلوا كما رأيتموني أصلي).
Kuyi sallah kamar yanda ku kaga inayi.

Acikin bayanin yanda manzan Allah yake sallah babu inda yake qablu awasu raka'o'in wasu kuma yayi sadalu.

Dan haka wannan kuskurene wanda baidace musulmi yake aikatawa ba Annabi sallallahu Alaihi wasallam yace:

(إنا معشر الأنبياء أمرنا بتأجيل فطرنا وتأخير سحورنا وأن نضع أيمننا على شمائلنا في الصلاة.

Mu taran Annabawa Allah ya umarcemu da gaggauta buda baki in munyi azumi dazarar rana tafadi, mukuma jinkirta sahur dinmu daf da fitowar alfijir, mu kuma dunga sanya hannayenmu nadama akan hagu dinmu acikin sallah.

Danhaka Qabdu a sallah gaba dayanta farillah, dana fila ta idi da ta jana'iza, data rokon ruwa dama duk wata sallah shine dora dama akan hagu bawai chakudawa ba.

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Saturday 29 October 2016

Menene hukuncin daura laya shin ta dace

MENENE HUKUNCIN DAURA LAYA SHIN TA DACE.

الحمد لله وحده والعاقبة للمتقين ولا عدوان إلا على الظالمين.

AMSA: Daka Abdullahi dan mas'ud Allah kara yarda dashi yace: Annabi sallallahu Alaihi wasallam ya kasance yana kin abubuwa guda goma, wani turare mai launin fatsi fasti, da chanza furfura, da zantufafi akasa, da sanya zoben zinare, da dukan kunci, mari, da bayyana ado ga mata a inda ba wajan bayyana shiba, dayin ruqya inba da falaqi da nasi ba, da sanya maniyyi a inda bai kamata ba, zina kenan, da saduwa da mai shayarwa,.
Wannan hadisi shaik albany ya raunana shi acikin za'ifan hadisin sunan nisa'i (3075).

Daka zainab matar Abdullahi dan mas'ud daka Abdullahi yace: Naji manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam yana cewa Lallai ruqya irin ta jahiliyya da kuma layu da tiwala "shine buda kaulasan ko takuri kowani harafi na kalmar alqur,ani asanya sunayen wadan za'a mallake, shirkane, sai tace : sai nace: saboda me kafadi haka,? wallahi idona yakasance ya naimin ciwo ina zuwa wajan wani mutum bayahude yaimun ruqya idan yamin ruqya sai yadena ciwo, sai Abdullahi yace: Wannan aikin shaidan ne shine yake tsone miki idan da hannunsa idan bayahuden yai miki ruqya sai yadena tsone miki, ya isheki kifadi irin abunda Annabi sallallahu Alaihi wasallam yakasance yana fada, " Allah katafiyar da cuta ya ubangijin mutane kawarkar dani, kaine mai warkarwa, warkarwar da babu sauran cuta.
Abu dauda (3883) da ibnu majah (3530).

Albany ya ingantashi acikin silsila sahiha (331) da (2972).

Daka uqubata dan Amir yace: Naji manzan Allah sallallahu alaihi wasallam yace: " Duk wanda ya rataya laya kada Allah yacika masa burinsa, duk wanda ya rataya daga kada Allah  yacika masa burinsa " imamu Ahmad ya ruwaito (16951).

Shaik Albani rahimahullah ya raunana hadisin acikin Za'iful jami'i (50703).

Daka uqubata bin amir aljuhany yace manzan Allah sallallahu alaihi wasallam wasu mutane goma sunzo wajansa sai yai muba'aya da mutane tara yaki mubaya'a da dayan, sai sukace: ya manzan Allah kaiwa mutum tara mubaya'a ka kyale daya sai yace: akwai laya atare dashi, sai yasa hannunsa ya cirota ya tsinkata, sai yayi masa mubaya'a sai yace: Duk wanda ya rataya laya hakika yayi shirka. Imamu Ahmad  (16969).

Shaik Albany rahimahullah ya inganta shi, acikin littafinsa silsila sahiha (492).

Laya itace abunda ake ratayawa yara ko manya su sanya ajikinsu ko asanya agida ko mota ko rumfar sana'a wata ta itatuwa da wasu ababe wata kuma dakashi ake hadasu dan kare sharri ko janyo amfani.

Malamai daka sahabbai databi'ai sunyi sabani wajan rataya layar da aka rubuta ayar alqu'ani kawai, wasu sukace indai ta qur'ani ce kawai ta halatta, wasu kuma sukace koda ta qur'ani ce bata halattaba saboda hadisin daya ce " duk wanda ya rataya laya yayi shirka" baice banda ta qur'ani ba.

Wannan magana kuma itace tafi karfi tafi fitowa fili saboda toshe hanyar barna, itace kuma mafiya yawan sahabbai suke akanta kamar Abdullahi dan Abbas da Abdullahi dan mas'ud da sauran malaman tabi'ai dama na wannan zamanin.

Malaman majaslisar ilmi da fatawa na kasar saudiyya sukace:" Malamai sunyi ittifaqi akan haramcin sanya laya da guru idan dai bata ayar qur'ani bace, sunyi sabani akan wacce akai da ayar alqur'ani kawai, daka cikinsu akwai wadanda suka halatta ta qur'ani zallah, daka cikinsu kuma akwai wadanda suka haramta harta alqur'anin, Amma fatawar haramcin harta alqur'ani itace mai rinjayen dalilai saboda gamewar da hadisai sukazo da ita na fadin kowacce laya basu kebe wacce take ta alqur'ani ba, da kuma to she hanyar barna.
Fatawa lajnatul da'imah (1/212).

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Shin ya matsayin sadaka da akeyi wajen mutuwa misali uku bakwai arba'in

SHIN YA MATSAYIN SADAQA DA AKEYI WAJEN MUTUWA MISALI UKU BAKWAI ARBA'IN

الحمد لله والصلاة والسلام على محمد وعلى  آله وصحبه وسلم

AMSA: Malamai sunyi ittifaqi akan cewa sadaqa da nemawa mamaci gafara da hajji duk suna isa zuwa ga mamaci.

Dalili akan addu'a da istigfari shine fadin Allah madaukakin sarki
(والذين جاؤوا من بعدهم يقولون ربنااغفرلنا ولإخواننا الذين سبقون بالإيمان)

Wadanda sukazo abayansu zasu dunga cewa ya ubangijinmu kagafarta mana damu da 'yan'uwanmu dasuka rigayemu da imani.
Manzan Allah sallahu Alaihi wasallam yace: ( kunemawa dan'uwanku gafara, ku roka masa tabbatuwa  domin yanzu za'a tambayeshi)
yasake cewa : ( Idan zakuyiwa mamaci sallah ku kyautata addu'a gareshi)

Amma sadaka ya tabbata acikin bukhari daka ubadah bin sabit yardar Allah takara tabbata agareshi, mahaifiyarsa ta rasu baya gari yace: ya manzan Allah mahaifiyata ta rasu bana nan shin innai mata sadaka zata amfaneta, sai manzan Allah yace: eh, sai ubada bin sabit yace: ina shaida maka gonata mai 'ya'yan kayan marmari na badashi sadaka agareta. bukhary (2756).

Amma aikin hajji kuwa Manzan Allah sallalllahu Alaihi wasallam yace: da matar data tambayeshi shin zan iya yiwa mahaifiyata aikin hajji bayan ta mutu? sai yace; shin inda bashine akanta zaki biya mata, sai tace : eh sai Annabi yace bashin Allah shine yafi cancanta abiya.) Bukhary 6699 muslim 1148.

Wadannan dalilai sun nuna sadaqa tana amfanar wanda ya mutu kuma ladanta zai isa gareshi.

Ansamu hadisi mai rauni wanda yake nuna ya halatta cewa idan kaiwa mamaci sallah ladan zaije gareshi, sai dai imamu muslim yace hadisine mai rauni acikin mukaddimar littafinsa ingantacce daka Abdullahi bin mubarak, sannan imamu muslima yace babu sabani akan sadaka.

Amma azumi da sallah amazhabar shafi'iyyah da jamhur din malamai ladansu baya kaiwa ga wanda ya mutu, sai dai idan azumin nawajibine mamaci ya mutu ana binsa to waliyyinsa zai rama masa ko kuma wanda mamacin yaiwa izinin ya rama masa kafin rasuwarasa.

Imamun nawawy acikin tuhfatul muhtaaj yace: " mamaci zai amfana da sadakar da akai masa daka ciki akwai kana iya sayen alqur'ani kakai masallacin daza'a dunga karantasu ko makaranta amtsayin wakafi ga mamacin, ko ka haka rijiya inda ake bukatar ta amatsayin wakafi ga mamaci, koya dasa bishiya zaidunga samun ladanta matukar ana amfana da ita, ko kuma wani yadasa bishiyar amatsayin wakafi ga mamacin.

Amma mafificiyar hanyar da mamaci zai amfana da wani abu dazakai mar shine kayawaita masa addu'ar Allah yagafarta masa, ko ka gina masallatai a inda ake bukatarsu da rayasu da ilmi, ko taimakawa dalibai tahanyar biya musu kudin makaranta ko buga littattafai dansu amfani dasu.

Amma taruwa da'ake bayan kwana uku da mutuwar mamaci a karanta alqur'ani ko adauki dukiyar marayu ayi abunci da sunan sadaka ga mamaci, wannan bidi'ane kuma cin dukiyar marayuce batare da hakki ba, Allah kuma yaharamta cin dukiyar marayu, haka ta arba'in haka ta shekara wadannan duk bidi'o'ine Allah bai saukar dawata hujja akai ba.

Kawai kai kadai kaiwa mamaci addu'a kadauki dukiyarka ta kanka halaliyarka kayi sadaqa da ita da nufin Allah yakai ladan ga mamaci wannan shine zai isa ga mamaci kamar yanda dalilai suka gabata, shima kuma batara  mutane akace kaiba, zakayi batare ma dakowa ya sani ba wannan shine sunnah.

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Friday 28 October 2016

Hukuncin yan kasuwa masu qarin farashi

HUKUNCIN 'YAN KASUWA MASU QARIN FARASHI

TAMBAYA TA 2011
********************
As-salamu Alaikum malam mai zauren fiqhu godiya da Fatan Alkhairi A gareka Allah yakara daukaka ga wannan zauren Naka,    

Malam ina son nayi tambaya ce Akan yanayi ta kasuwanci domin ‎ ni ina kasuwanci ne ina saye da sayarwa sai Naji ance abinda Nike sayarwa ya samu karin kudi Daga kasuwa ko Daga kamfani shin ya halitta nima nayiwa nawa ababan da Nike sayarwar karin kudi domin in zanje kasuwa sai nayi cikon kudi  ba zan tsameshi kamar yadda Nike sayarwa in banyi karin kudin ba, Allah yabada ikon amsa

AMSA
*******
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Irin wannan abinda kake tambaya akansa, bai halatta ba. Abinda ake so ga dan kasuwa shine ya zamanto Mai gaskiya mai son gaskiya, kuma mai aiki da gaskiya acikin dukkan harkokinsa.

Abu Sa'eed Alkhudriy (rta) yace Manzon Allah (saww) yace : "DAN KASUWA MAI GASKIYA, MAI AMANA, YANA TARE DA ANNABAWA DA SIDDIQAI DA SHAHIDAI (ARANAR ALQIYAMAH KENAN).

(Imam Tirmidhiy ne ya ruwaitoshi acikin kitabul buyu'i kuma ya ingantashi).

Wani hadisin kuma daga Isma'il bn Ubaid bn Rifa'ah, daga babansa daga Kakansa (rta) yace Ya fita zuwa wajen Sallah tare da Manzon Allah (saww) sai Manzon Allah (saww) yaga mutane suna ta cinikayya atsakaninsu.

Sai yace "YA KU TARON ATTAJIRAI!!". Sai suka amsa kiransa, suka 'daga kayuwansu da idanuwansu gareshi. Sai yace :

"HAKIKA SU 'YAN KASUWA ZA'A TASHESU NE ARANAR ALQIYAMAH AMATSAYIN FAJIRAI. SAI DAI WANDA YAJI TSORON ALLAH, YAYI BIYAYYA, KUMA YAYI GASKIYA".

(Tirmidhiy ne ya ruwaitoshi).

Don haka abinda yafi gareka shine ka saukaka ka bayyanar da gaskiya. Duk lokacin da ka koma domin sayowa, idan ka samu anyi Qarin kudi kaima sai ka Qara. Amma idan ka tarar anyi ragi kaima sai ka rage.

Annabi (saww) yayi addu'a yace : "ALLAH YAJI QAN MUTUM MAI SAUKAKAWA IDAN ZAI SAYI ABU, MAI SAUKAKAWA IDAN ZAI SAYAR.... ".

Idan kayi haka in sha Allah zaka shiga cikin addu'ar Manzon Allah (saww). Kuma zaka samu albarka mai yawa acikin kasuwancinka.

WALLAHU A'ALAM.

ZAUREN FIQHU

Share:

Ka/ki kiyaye raka'o'i 12 domin samun gida a aljannah

KA/KI KIYAYE RAKA'O'I 12 DOMIN SAMUN GIDA A ALJANNAH..

Assalamu alaikum malam dan allah ina son ayimin bayanin yadda nafilolin da ake yi kafin sallah da kuma bayan sallah suke da kuma falalarsu wslm?

Amsa:

الحمد لله

Malaman fiqhu sunyi bayanin cewa sallolin nafila na rana a asirce ake yinsu, su kuma sallolin nafila na dare a bayyane ake yinsu. Amma sallar bayan maghrib (ba'ad maghrib) da kuma raka'atanil fajr kana iyayi a bayyane ko a asirce. Hujja kuwa itace; Hadisin da Ibn Majah da Tirmizi suka ruwaito daga Abdullahi Dan Mas'ud (Allah ya yarda dashi) yace yaji abinda Manzon Allah sallallahu alaihi wasallam yake karantawa a sallar bayan Maghrib da kuma nafilar sallar al-fijr. Kenan wannan ya nuna manzon Allah sallallahu alaihi wasallam yana yi a bayyane shi yasa har Dan Mas'ud yaji abinda yake karantawa.

Haka kuma akwai hadisi wanda Uwar muminai A'isha (Radiyallahu anha) ta ruwaito cewa Annabi (sallallahu alaihi wasallam) ya kasance yana karanta Fatiha ne kadai acikin raka'atanil fajr, kuma yana yinta ne a asirce.

Saboda haka dai su sallolin Ba'ad maghrib wato sallar bayan maghrib da kuma raka'atanil fajr kana iya yinsu a bayyane ko asirce, kuma yana da kyau ma ka rinka yi kana canzawa; yau kayi asirce gobe kayi a bayyane.

Sai kuma dangane da fafalarsu; to kowace daga cikin sallolin nafilolin tana da nata falala wadda ita kadai take da ita kuma. Amma kuma akwai hadisi wanda ya nuna mana falalarsu a jimlace. Imam Muslim ya ruwaito hadisi daga Ummu Habeebah (Allah ya yarda da ita), matar Annabi (sallallahu alaihi wasallam) tace:  Naji manzon Allah (sallallahu alaihi wasallam), yace: " Ba wani Musulmi wanda zai kiyaye yin raka'o'i 12 na nafila kowace rana, bayan yayi na farillah face Allah bai gina masa gida a aljannah ba"...

A wata ruwayar hadisin kuma wanda Tirmizi (415) ya ruwaito daga ita din Ummu Habeebah(Allah ya yarda da ita) tace: Manzon Allah (sallallahu alaihi wasallam) yace: " Duk wanda ya kiyaye yin raka'o'i goma sha biyu (12) a dare da rana, to za'a gina masa gida a cikin Aljannah: raka'a hudu kafin zuhr da kuma raka'a biyu bayanta, raka 2 bayan maghrib da kuma raka'a biyu bayan Isha'i sai kuma raka'a biyu kafin sallar subhi" Sheikh Albani ya ingantarda hadisin a cikin Saheeh Sunan at- Tirmizi.

Saboda haka dan uwa ko yar uwa da fatan zamu kiyaye yin wadannan sallolin nafilolin domin samun gida a Aljannah. Allah yasa muna cikin wadanda zasu tsinci kansu a aljannah Firdaus.

Wallahu a'alam

سبحانك اللهم وبحمد ك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

Tambayoyin Musulunci
WhatsApp group
+2348164884055
+2347068043652

Share:

Wednesday 26 October 2016

Rayuwarmu a yau kenan

*RAYUWARMU A YAU KENAN*

Ko ka taba karanta _*English Version*_ na irin wannan labari, ka dan daure karanta wannan akwai wani dan qarin bayani a ciki....

Wata rana wata malamar Lissafi (Mathematics Teacher) ta shigo aji sai ta rubuta wannan rubutun dake a qasa akan allo..

_*9×1=7*_
_*9×2=18*_
_*9×3=27*_
_*9×4=36*_
_*9×5=45*_
_*9×6=54*_
_*9×7=63*_
_*9×8=72*_
_*9×9=81*_
_*9×10=90*_

Bayan ta kammala rubutunta, koda ta juyo ta kalli dalibanta tuni aji ya kacame da dariya suna nuna mata hannu akan allo saboda wancan kuskuren da tayi na farkon wanda ta sanya _*9×1=7*_ a maimakon _*9×1=9*_ wanda yake shine daidai.

Sai malamar tayi murmushi tana mai gaya musu cewa:

_*" Ai dama nayi haka ne da gangan ( a sane ) saboda inason ku koyi darasi daga wannan kuskuren nawa"*_

Wannan zai zamo darasi gareku kusan cewa haka mutane ke biye daku. Yanzu ku duba ba tare da duba da irin wahalar da nake yi daku ba wajen koya muku wannan lissafi har kuka iya, ban taba yi muku kuskure ba sa'annan kuma a wannan rubutun kadai na rubuta amsoshi guda tara *_9*_ gaba dayansu daidai, sa'annan kuma baku yi la'akari da cewa wadannan amsoshin guda tara gaba dayansu sunfi waccan amsar ta farko wuya ba kuma duka nayi su daidai amma a cikinku ba wanda ya jinjina min sai wannan kuskuren shi kawai kuka gani kuma kuke dariya da tuhumata akansa.

Lallai ina mai qara jaddada muku ku sani wannan babban qalubale ne zuwa gare ku, haka rayuwar take.......

Mutane ba zasu taba gode ko jinjina maka ba a duk dimbin miliyoyin ayukan alkhairi da kayi, amma kuma zasu saka maka ido tare da zargin/tuhuma akan kuskure qwaya daya kacal da kayi. _*AMMA FA KADA KU KARAYA SABODA WANNAN*_

_*SABODA HAKA A KULLUM IDAN KA MIQE ZUWA AIKATA ALKHAIRI TO KA KAUDA KAI DAGA DARIYA, ZARGI DA KUMA TUHUMAR MUTANE. KADA KA NEMI GODIYA, JINJINAWA KO SAKAYYAR MUTANE. KAWAI DUK ABINDA ZAKA YI TO KAYI DAN ALLAH. KUMA KA NEMI TSARI DA GAFARA DAGA GARE SHI SABODA SHI YANA GANIN DAIDANKA KUMA YANA GANIN KUSKURENKA.*_

_*Idan kuma kace kana jiran godiya da sakayya daga mutane babu shakka za ka sha mamaki kuma idan aikin lada ne kake yi zaka rasa ladar, kaga ka tashi a tutar babu kenan.*_

_*YA ALLAH KA QARA KYAUTATA MANA NIYYOYINMU*_

_*YA ALLAH KA KARBI AYUKANMU NA ALKHAIRI KA YAFE MANA KURA-KURANMU*_

*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Ya mutun zayyi ramuwar sallar daya manta bayan lokacin wata ya shigo??

*YA MUTUM ZAYYI RAMUWAR SALLAR DA YA MANTA BAYAN LOKACIN WATA YA SHIGO??*

Aslamu alaikum warahamatull lahi taala wabara katuhu malan ya mutum zaiyi ramuwar sallah wadda baiyi bah a baya

الحمد لله والصلاة والسلام على محمد وآله وصحبه وسلم.

AMSA:Dafarko kafin mu amsa tambayar zamuyi wani bayani dazai bada haske akan ramuwar sallar da mutum yamanta ko kuma takubuce masa baiyiba.

Hukuncin jeranta sallolin dasuka riga suka wuce mutum bai yiba.

Malaman mazahabobi guda uku Abu hanifa, Ahmad, Malik. suntafi akan wajabcin jeranta sallolin da suka wuce, yayin ramasu, dalili akan haka shine manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam ya rama wasu sallar data wuce masa ajere alokacin yakin kandaq.

Imamul bukhari ya ruwaito hadisi(641) da muslim(631). daka jabir dan Abdullahi manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam ya rama sallar la'asar data wuce baiyi taba aranar yakin kandaq, bayan rana tafadi, sannan sai yayi magriba bayan ya rama la'asar,
haka kuma bukhary ya ruwaito (631) Manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam yace ( kuyi sallah kamar yadda kukaga inayi. Almugny(2/336).

Idan mutum ya manta jerantawar wajan ramuwa shin jerantawar tafadi akansa?

Na'am idan mutum ya manta jeranta salloli wajan ramasu jerantawar tafadi akansa, saboda fadin manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam yace:(Allah madaukakin sarki yadaukewa al'ummata abunda suka aikata bisa kuskure bada niyyah ba, dakuma abunda suka aikata bisa mantuwa da kuma abunda aka tursasau akai) Ibnu majah (2043) Albany ya ingantashi acikin sahihu ibnu majah (1662) kuma wannan itace mazhabar limamai biyu Abu hanifa da Ahmad Allah yai musu rahama.fat hul qadeer(1/424). da Almugny (2/340).

Duk wanda yamanta sallah har lokacin wata ya shigo,yana da halaye guda uku

1-ya tuna sallar data wuce masa kafin ya shiga wacce lokacin tane, awannan lokacin wajibine yafara yin wacce ta wuce kafin yin wacce lokacin tane.
2-Ya tuna ana binsa sallar data kubuce masa bayan ya kammala wacce take alokacin ta, to sallar dayayi wacce take alokacin ta tayi, sai yarama wacce ake binsa abayanta, saboda yana da uzurin rashin jerantawa da mantuwa
3-Ya tuna ana binsa sallar data wuce akansa yana cikin yin wacce lokacinta yake, awannan hali zai cika wacce lokacinta yake nan saita zamto masa amatsayin nafila, sannan sai yayi wacce ake binsa, sai yasake wacce take alokacinta saboda kiyaye jerantawa, wannan itace mazhabar imamu Ahmad Rahimahullah Almugny (340-2/336).
itace maganar Abdullahi bin umar Yardar Allah takara tabbata agaresu.

Imamu malik ya ruwaito acikin muwaddah, daka nafi'u cewa Abdullahi dan umar yana cewa: wanda ya manta sallah bai tuna ana binsa sallah ba saida yana cikin bin liman a wata sallar, idan liman yayi sallama, sai yayi sallar data wuce masa yasake wacce yayi tare da liman.

Shaikul islam ibnu taimiyyah Rahimahullahu yace:( Duk lokacin da mutum ya tuna ana binsa wata sallah  yana cikin yin wata zai kasance kamar baifara yin wacce take alokacinta ba, Amma dazai tuna ana binsa sallah bayan yagama wacce take alokacinta, to wacce yayi alokacinta ta isar masa awajan mafiya yawan malamai kamar Abu hanifah, da shafi'i da Ahmad.)Fatawal kubra (1/112).

Cewa da akayi zai cika wacce yake alokacinta mustahabbine ba wajibiba da zai yanke wacce yake alokacinta, yayi wacce ake binsa sannan yayi wacce take alokacinta hakan ya isar masa.

Wasu malaman suntafi akan cewa zai karasa wacce yake alokacinta bazai sake maimaita taba, sannan sai yayi wacce ake binsa, wannan shine mazhabar imamul shafi'i, kamar yanda yazo Acikin Al majmu'u (3/70).
kuma shine zabin uthaimeen rahimahullah, kamar yanda yazo acikin fatawarsa(12/221). Maganar farko ita tafi daidai.

Idan mun fahimci yanda ake rama sallar data kubucewa mutum da mantuwa ko wani dalili karbabbe ashari'a, to ga yanda zai rama din kuma shine muka dan fadada bayani asama.

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Dalilan dake sa a hade salloli

DALILAN DAKE SA A HADE SALLOLI...

assalamu alaiku malan ya halatta wusu lokutta ahade magariba da isha to malan wadanni lokuttane allah ya kara sani.

AMSA:

الحمد لله

Wa'alaikumus salam..
Ana hade salloli azzahar da Asr, da kuma maghrib da Isha'i saboda dalilai kamar haka�����

��� Lokacin hajji: A arafah mutum zai hade zuhr da asr a yayi su lokacin zuhr. Haka kuma zai hade maghrib da isha'i yayi su a lokacin isha'i a Muzdalifah. #Hadis

��� Matafiyi: Idan akwai wahala ga matafiyi idan yace zai yi kowace sallah a lokacinta to zai iya hadewa. #Hadisai masu dama  sun nuna haka sa'annan kuma ������

ﻳُﺮِﻳﺪُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺑِﻜُﻢُ ﺍﻟْﻴُﺴْﺮَ ﻭَﻟَﺎ ﻳُﺮِﻳﺪُ ﺑِﻜُﻢُ ﺍﻟْﻌُﺴْﺮَ

[al-Baqarah 2:185]

��� Idan ana ruwan sama.. Sunnah ce a hade salloli; zuhr da la'asar, maghrib da isha'i #Hadis

��� Rashin lafiya mai tsanani: Ya halatta idan yin sallah kowace lokacinta ga majinyaci akwai wahalarwa to ya hade sallolin. #Hadis da kuma ayar qur'ani������

ﻳُﺮِﻳﺪُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺑِﻜُﻢُ ﺍﻟْﻴُﺴْﺮَ ﻭَﻟَﺎ ﻳُﺮِﻳﺪُ ﺑِﻜُﻢُ ﺍﻟْﻌُﺴْﺮَ

[al-Baqarah 2:185]

��� Sai kuma sallah a cikin jirgin ruwa ko jirgin sama, tarago etc...  #Hadis kuma������

ﻳُﺮِﻳﺪُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺑِﻜُﻢُ ﺍﻟْﻴُﺴْﺮَ ﻭَﻟَﺎ ﻳُﺮِﻳﺪُ ﺑِﻜُﻢُ ﺍﻟْﻌُﺴْﺮَ

[al-Baqarah 2:185]

6.��� Sa'annan mutane suna iya hade sallolin a duk wani lokaci na tsanani, rudani ko wahala idan har yinsu kowace lokacinta zai saka su cikin tsanani ko wahala.

ﻻَ ﻳُﻜَﻠِّﻒُ ﺍﻟﻠّﻪُ ﻧَﻔْﺴًﺎ ﺇِﻻَّ ﻭُﺳْﻌَﻬَﺎ

[al-Baqarah, 2: 286]

ﻳُﺮِﻳﺪُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺑِﻜُﻢُ ﺍﻟْﻴُﺴْﺮَ ﻭَﻟَﺎ ﻳُﺮِﻳﺪُ ﺑِﻜُﻢُ ﺍﻟْﻌُﺴْﺮَ

[al-Baqarah 2:185].

Wallahu a'alam

سبحانك اللهم وبحمد ك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

Tambayoyin Musulunci
WhatsApp group
+2348164884055
+2347068043652

Share:

Abinda ake so wanda yaji kiran sallah yayi daga lokacinda yaji kiran sallah har izuwa iqamah

*ABINDA AKE SO WANDA YAJI KIRAN SALLAH YAYI DAGA LOKACINDA YAJI KIRAN SALLAH HAR I ZUWA IQAMAH*

Assalamu alaikum
Malam dan Allah ina so amin bayani akan yanda ake amsa kiran Sallah
Nagode

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ

_*AMSA:*_
*******
Da farko dai abinda ake son wanda yaji kiran sallah yayi shine: Maimata wato fadin irin abinda duk ladan ya fada. Amma wajenda ladan ke cewa:

*ﺣﻲ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺼﻼﺓ*
*"Hayya alal Salah"*

da

*ﺣﻲ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻔﻼﺡ*
*"Hayya alal falah"*

Anan sai ace

*ﻻ ﺣﻮﻝ ﻭﻻ ﻗﻮﺓ ﺇﻻ ﺑﺎﻟﻠﻪ*
*"La haula wala quwwata illa billah"*

[Bukhari da Muslim 385]

Idan kuma mai kiran sallah ya kammala kiran sallah sai kace:

*"Ashhadu an la'ilaha illallah wahdahu la sharika lahu, wa anna Muhammadan abduhu wa rasuluhu, raditu billahi rabban, wa bi Muhammadin rasulah, wa bil islami dinan"* [Muslim]

Bayan wannan sai mutum yayi wa Annabi sallallahu alaihi wasallam salati:

Daga Jabir (Allah ya yarda dashi) yace: Annabi (sallallahu alaihi wasallam) yace: "Dukkan wanda yace a lokacinda yaji kiran sallah:

*ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺭﺏ ﻫﺬﻩ ﺍﻟﺪﻋﻮﺓ ﺍﻟﺘﺎﻣﺔ ﻭﺍﻟﺼﻼﺓ ﺍﻟﻘﺎﺋﻤﺔ ﺁﺕ ﻣﺤﻤﺪﺍ ﺍﻟﻮﺳﻴﻠﺔ ﻭﺍﻟﻔﻀﻴﻠﺔ ﻭﺍﺑﻌﺜﻪ ﻣﻘﺎﻣﺎ ﻣﺤﻤﻮﺩﺍ ﺍﻟﺬﻱ ﻭﻋﺪﺗﻪ*

*"Allahumma Rabba hazihid da'watit tammat wassalatil qaimati, ati Muhammadan waseelata wal fadeelata, wab'athhu maqaman mahmoodal lazi wa'adtahu"*

Cetona ya halatta akansa ranar alqiyamah". [Bukhari, 589]

Wato duk wanda aka gama kiran sallah yayi wannan addu'ar zuwa ga Annabi (sallallahu alaihi wasallam) dake a sama to cetonsa ya halatta a gare shi ranar qiyamah. Allah yasa muna daga cikin wadanda zai ceta.

Sai kuma tsakanin kiran sallah zuwa tada iqamah ana son mutum yayi addu'a saboda ana amsar addu'a a wannan tsakanin. Daga Anas (Allah ya yarda dashi) yace: Annabi (sallallahu alaihi wasallam) yace:

*Haqiqa ba'a mayarda addu'a tsakanin kiran sallah da iqamah, saboda haka kuyi addu'a*. [Tirmizi 212, Abu Dawud 437, Ahmad 12174]

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

Archive

Unordered List

Support