Shin ana ramawa wanda ya mutu azumi na ramadan ?? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 8 November 2016

Shin ana ramawa wanda ya mutu azumi na ramadan ??

*SHIN ANA RAMAWA WANDA YA MUTU AZUMI NA RAMADAN??*

الحمد الله وكفى وصلى الله على محمد وآله وصحبه وسلم،

Amsa:An yiwa shaeik uthaimeen {Rahimahullah} irin wannan tambaya sai ya amsa dacewa,
Mara lafiya matukar yana cikin rashin lafiya a zumi bai wajaba akan saba, idan ya mutu kafin ya warke, ya mutu kafin yazama wajibi akansa, baza'a ciyar a madadin saba domin ciyarwa a matsayin azumi take, idan azumi bai zama wajibi ba, to mamadin sama bai zama wajibiba,Allah madaukakin sarki yace:
(ومن كان مريضا أو على سفر فعدة من أيام أخر، يريد الله بكم اليسر ولايريد بكم العسر ولتكملو العدة ولتكبر الله على ما هداكم ولعلكم تشكرون،)
Duk wanda yakasance mara lafiya acikinku ko yana halin tafiya, to ya rama awasu kwanakin daban bana ramazan ba, Allah yana nufin saukine a gareku, ba yana nufin quntatawa agareku bane, danku cika kwanakin dan kuma ku godewa Allah abisa abun da ya shiryar daku, ko zaku zamto masu yawan godewa,

Tabbatar  dalili da wananana aya shine idan bai samu dama ba babu komai akansa, saboda Allah ya sanya wajabcin ramuwar azumi a kwanaki nagaba, shikuwa bai kaiba sai yarasu, idan ya mutu kafin yakai zuwa garesu hakika ya mutu kafin lokacin wajabci yazo, sai yakasance kamar wanda ya mutu kafin shi gowar watan ramazan, bai wajaba aciyar masaba sobada watan ramazana da zaizo agaba, koda ya mutu ramazan yana gobe kamawa.

Amma a hadisi manzan Allah salallahu Alaihi wasallam yace, (Duk wanda ya mutu da azumi akansa to waliyyinsa sai yayi masa, bukhari da muslim,
Abunda hadisin ke magan akai shine wanda ya mutu yana da ramuwar azumi akansa, to waliyyinsa sai ya rama masa, ba wanda ya mutu acikin watan azumin ba, idan bazai masa azumi ba to ya ciyar kowacce rana miskini daya, iya adadin azumin dake kansa bai rama ba,

Abun nufi wanda ya mutu babu azumi a kansa baza ai masa azumi ba, mun sani cewa idan mara lafiya cuta taci gaba ajikin sa, azumi bai wajaba akansa ba, ko ramuwa a halin rashin lafiyarsa,

Amma wanda ya mutu ana cikin azumi, to waliyyinsa bazai karasa masa zumiba kuma bazai ciyar ba, domin mara lafiya idan ya mutu aiyukansa sun yanke, kamar yanda Annabi sallahu alaihi wasallam, yafada ( Idan mutum ya mutum ayyukansa sun yanke sai abubuwa uku sadaka mai gudana, ko ilmin daya bari ake amfana dashi, ko da nagari dazai dungai masa addu'a, abisa wannan baza,a rama masaba hatta na ranar daya mutu

والله أعلم،

***********************************

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.

_*��Tambayoyin*_ _*Musulunci��*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_

Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support