2018 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Wednesday 5 December 2018

FATAWAR RABON GADO 190


Tambaya:
عندى سؤال ماتت امرأة بدون زوج ، لكن تركت بنت واحدة ، وجمع من أبناء الاشقاء ، وجمع من أبناء لاب.

Amsa:
وعليكم السلام للبنت النصف، والباقي لأبناء الإخوة الأشفاء الذكور منهم فقط، دون الإناث.

والله أعلم.

✍️Amsawa:
_Dr Jamilu Yusuf Zarewa_
27/11/2018.

Share:

FATAWAR RABON GADO(189) Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum inayimaka fatan alheri malam. Mutum ne ya mutu yabar matar aure da yara mata 5 sai yan'uwa shakikay 3 sananan akwai li 'abbai malam yaya rabon zaikasance? Allah yakara lafiya.


*Amsa*
Wa alaikum assalam

Za'a raba gida (24), a bawa matarsa kashi (3) yaransa mata kashi (16) ragowar sai a bawa 'yan'uwa shakikai.

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

12/11/2018

Share:

HUKUMCIN SHAN MAGANIN TAURI ! Dr Jamilu Yusuf Zarewa


 
Tambaya

Assalamu alaikum Allah ya karawa Dr. Lafiya.
Mene ne hukuncin shan maganin tauri wato Maganin karfe ko kauranci a musulunci ?

  Amsa
Wa alaikum assalam
Mutukar babu abin da ya sabawa sharia a ciki, ana iya amfani da shi saboda neman kariya,  saboda duk mua'amalolin da mutane suke yi, in har ba'a samu nassin da ya haramta ba, to sun halatta saboda Ka'idar: الأصل في الأشياء الإباحة.

Da yawa daga cikin magungunan tauri akwai kauce hanya a ciki, akwai wadanda ake barin sallah idan an sha, ka da aje garin-neman-gira a-rasa- IDO.
Mutukar maganin tauri ya kunshi abin da sharia ta haramta, bai halatta ayi amfani da shi ba, Biyayya ga Allah maganin KAU-DA-BARA.

Amsawa✍🏻
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
25/03/1440
03/12/2018

Share:

FATAWAR RABON GADO 190


Tambaya:
عندى سؤال ماتت امرأة بدون زوج ، لكن تركت بنت واحدة ، وجمع من أبناء الاشقاء ، وجمع من أبناء لاب.

Amsa:
وعليكم السلام للبنت النصف، والباقي لأبناء الإخوة الأشفاء الذكور منهم فقط، دون الإناث.

والله أعلم.

✍️Amsawa:
_Dr Jamilu Yusuf Zarewa_
27/11/2018.
Share:

FATAWAR RABON GADO(189) Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum inayimaka fatan alheri malam. Mutum ne ya mutu yabar matar aure da yara mata 5 sai yan'uwa shakikay 3 sananan akwai li 'abbai malam yaya rabon zaikasance? Allah yakara lafiya.


*Amsa*
Wa alaikum assalam

Za'a raba gida (24), a bawa matarsa kashi (3) yaransa mata kashi (16) ragowar sai a bawa 'yan'uwa shakikai.

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

12/11/2018
Share:

HUKUMCIN SHAN MAGANIN TAURI ! Dr Jamilu Yusuf Zarewa


 
Tambaya

Assalamu alaikum Allah ya karawa Dr. Lafiya.
Mene ne hukuncin shan maganin tauri wato Maganin karfe ko kauranci a musulunci ?

  Amsa
Wa alaikum assalam
Mutukar babu abin da ya sabawa sharia a ciki, ana iya amfani da shi saboda neman kariya,  saboda duk mua'amalolin da mutane suke yi, in har ba'a samu nassin da ya haramta ba, to sun halatta saboda Ka'idar: الأصل في الأشياء الإباحة.

Da yawa daga cikin magungunan tauri akwai kauce hanya a ciki, akwai wadanda ake barin sallah idan an sha, ka da aje garin-neman-gira a-rasa- IDO.
Mutukar maganin tauri ya kunshi abin da sharia ta haramta, bai halatta ayi amfani da shi ba, Biyayya ga Allah maganin KAU-DA-BARA.

Amsawa✍🏻
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
25/03/1440
03/12/2018
Share:

Tuesday 20 November 2018

Zan Iya Auran Wanda Ba Shi Da Uba ? - Dr Jamilu Yusuf Zarewa



Tambaya

Assalamu Alaikum, Don Allah Malam, wata dalibata ce ke neman shawara kan auren wani mutumin kirki, amma baida uba !!!
Wane irin kalubale ku ke hange a kanta, a yanzu da nan gaba?
Me ye mafi alkhairi a gare ta?
Jazakumullahu bikhairin Malam. Bissalam


Amsa

Wa alaikum assalam
Mutukar ta yarda da addininsa da kuma dabi'unsa tana iya auransa kamar yadda hadisin Tirmizi ya tabbatar.

Kasancewar an haife shi ba ta hanyar aure ba, ba laifinsa ba ne, Allah ba ya dorawa wani laifin wani.

In dai shegantuwarsa ba ta shahara a tsakanin mutane ba, ta yadda nan gaba za'a dinga aibanta abin da kuka haifa tare, kina iya auransa, tun da mutumin kirki ne.

Duk da cewa ya halatta a shariance ki auri wanda ba'a san mahaifinsa ba, saidai idan kika ji tsoran tozarta zuriyarki, to ana barin halal don kunya, kamar yadda Hausawa suke fadi kuma dalilin sharia ya tabbatar.

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

17/11/2018
Share:

Zan Iya Auran Wanda Ba Shi Da Uba ? - Dr Jamilu Yusuf Zarewa



Tambaya

Assalamu Alaikum, Don Allah Malam, wata dalibata ce ke neman shawara kan auren wani mutumin kirki, amma baida uba !!!
Wane irin kalubale ku ke hange a kanta, a yanzu da nan gaba?
Me ye mafi alkhairi a gare ta?
Jazakumullahu bikhairin Malam. Bissalam


Amsa

Wa alaikum assalam
Mutukar ta yarda da addininsa da kuma dabi'unsa tana iya auransa kamar yadda hadisin Tirmizi ya tabbatar.

Kasancewar an haife shi ba ta hanyar aure ba, ba laifinsa ba ne, Allah ba ya dorawa wani laifin wani.

In dai shegantuwarsa ba ta shahara a tsakanin mutane ba, ta yadda nan gaba za'a dinga aibanta abin da kuka haifa tare, kina iya auransa, tun da mutumin kirki ne.

Duk da cewa ya halatta a shariance ki auri wanda ba'a san mahaifinsa ba, saidai idan kika ji tsoran tozarta zuriyarki, to ana barin halal don kunya, kamar yadda Hausawa suke fadi kuma dalilin sharia ya tabbatar.

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

17/11/2018

Share:

Monday 12 November 2018

Hukunci Kashe Kwadi Da Cin Namansu! - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


Tambaya


  Assalamu alaikum Malam menene ingancin hadisin da yake cewa: "Annabi SAW ya hana kashe Kwadi saboda kukansu Tasbihi ne ga Allah"? 


 Amsa 

 Wa alaikum assalam, Tabbas ya tabbata a hadisin Abu-dawud mai lambata: (5269) da kuma Nas'i (2/202) cewa: wani likita ya tambayi Manzon Allah akan kashe kwadi saboda sanyawa a magani sai Annabi ya hana shi kashe su".  Baihaki ya rawaito daga maganar Abdullahi Bn Amri bn Al-Ass cewa "Kada Ku kashe kwadi saboda kukansu tasbihi ne ga Ubangijinsu". Duk da cewa hadisin zai iya daukar cewa ya ji ne daga Manzon Allah saidai Hafiz Bn Hajar yana cewa " Abdullahi bn Amr bn Ass ya shahara da yin riwaya daga malaman Yahudu da Nasara don haka ba dole ne ya zama daga Annabi SAW ya ji ba.  Kashe kwadi haramun ne saboda hadisin Abu-dawud da Nasa'i da ya gabata, kamar yadda cin su ma haramun ne, saboda ba zai yiwu a ci dabba ba sai bayan ranta ya fita.  Allah ne mafi sani  

 Amsawa
✍🏻  DR. JAMILU YUSUF ZAREWA 11/11/2018

Share:

Kakanta Ba Ta Iya Sallah Saboda Rudewa Ko Za Ta Fadi Akanta? - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


Tambaya

Assalamu alaikum ina fatan Dr yana cikin koshin lafiya, Allah ya kara masa imani da fasaha Amin.Dr kakata ce tsufa ya kamata ga rashin lafiya, yaranta tara bata gane Ko daya daga cikin su gashi bata gane alwala balantana Sallah, Ko an mata alwala bazata gane Sallah ba, ga shi tana yini da pampas a jikinta ya zamuyi da sallanta???

Amsa

Wa alaikum assalam Ku yi iya ba-kin kokarinku wajan Ku ga ta kwatanta sallah, in bai yiwu ba ku kyale ta, saboda Allah ba ya dorawa rai abin da ba zai iya ba kamar yadda aya ta karshe a Suratul Bakara ta yi bayanin gamsashshe akan hakan.
A zahirin nassoshin sharia in har ba ta gane komai to za ta dau hukuncin Mahaukata ne, tun da ba ta cikin hayyacinta,
 mahaukaci  hadisi ya tabbatar da sarayuwar sallah daga kansa.

Sallah ba ta karbar wakilci, don haka ba Wanda zai rama mata a cikinku.

Allah ne mafi sani 

Amsawa✍🏻

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

11/11/2018

Share:

Hukunci Kashe Kwadi Da Cin Namansu! - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


Tambaya


  Assalamu alaikum Malam menene ingancin hadisin da yake cewa: "Annabi SAW ya hana kashe Kwadi saboda kukansu Tasbihi ne ga Allah"? 


 Amsa 

 Wa alaikum assalam, Tabbas ya tabbata a hadisin Abu-dawud mai lambata: (5269) da kuma Nas'i (2/202) cewa: wani likita ya tambayi Manzon Allah akan kashe kwadi saboda sanyawa a magani sai Annabi ya hana shi kashe su".  Baihaki ya rawaito daga maganar Abdullahi Bn Amri bn Al-Ass cewa "Kada Ku kashe kwadi saboda kukansu tasbihi ne ga Ubangijinsu". Duk da cewa hadisin zai iya daukar cewa ya ji ne daga Manzon Allah saidai Hafiz Bn Hajar yana cewa " Abdullahi bn Amr bn Ass ya shahara da yin riwaya daga malaman Yahudu da Nasara don haka ba dole ne ya zama daga Annabi SAW ya ji ba.  Kashe kwadi haramun ne saboda hadisin Abu-dawud da Nasa'i da ya gabata, kamar yadda cin su ma haramun ne, saboda ba zai yiwu a ci dabba ba sai bayan ranta ya fita.  Allah ne mafi sani  

 Amsawa
✍🏻  DR. JAMILU YUSUF ZAREWA 11/11/2018
Share:

Kakanta Ba Ta Iya Sallah Saboda Rudewa Ko Za Ta Fadi Akanta? - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


Tambaya

Assalamu alaikum ina fatan Dr yana cikin koshin lafiya, Allah ya kara masa imani da fasaha Amin.Dr kakata ce tsufa ya kamata ga rashin lafiya, yaranta tara bata gane Ko daya daga cikin su gashi bata gane alwala balantana Sallah, Ko an mata alwala bazata gane Sallah ba, ga shi tana yini da pampas a jikinta ya zamuyi da sallanta???

Amsa

Wa alaikum assalam Ku yi iya ba-kin kokarinku wajan Ku ga ta kwatanta sallah, in bai yiwu ba ku kyale ta, saboda Allah ba ya dorawa rai abin da ba zai iya ba kamar yadda aya ta karshe a Suratul Bakara ta yi bayanin gamsashshe akan hakan.
A zahirin nassoshin sharia in har ba ta gane komai to za ta dau hukuncin Mahaukata ne, tun da ba ta cikin hayyacinta,
 mahaukaci  hadisi ya tabbatar da sarayuwar sallah daga kansa.

Sallah ba ta karbar wakilci, don haka ba Wanda zai rama mata a cikinku.

Allah ne mafi sani 

Amsawa✍🏻

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

11/11/2018
Share:

Sunday 11 November 2018

Fatawar Rabon Gado (188) - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum malam mutum ne ya mutu  yabar mahaifi, mahaifiya,  mata, yar mace daya , da yan uwa wanda suke uwa daya uba daya Maza uku mata buyi.

*Amsa*

Wa alaikum assalam Za'a raba kashi (24), a bawa matarshi kashi uku,  mahaifiyarshi kashi hudu, 'yar shi kashi sha biyu, mahaifinsa kashi biyar.

Allah ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
06/11/2018

Share:

Fatawar Rabon Gado (187) - Dr Jamilu Yusuf Zarewa




*Tambaya*

Assalamu alaikum dafatan Malam Yatashi Lafiya.
dan Allah Malam Ya rabon gadon mutumin da ya bar mahaifi, mahaifiya,  mata, yara Maza biyu, da yan'uwa wanda suke uwa daya uba daya Maza uku mata biyu ?

*Amsa*

Wa alaikum assalam Za'a raba gida (24), a bawa matarsa kashi uku, mahaifiyarsa kashi hudu, babansa kashi hudu , ragowar sai a bawa yaransa su raba.

Allah ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
06/11/2018

Share:

Fatawar Rabon Gado (186) - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

ASSALAMU ALAIKUM MALAM MUTUM NE YA RASU YA BAR MAGADA KAMAR HAKA:
AKWAI UWA AKWAI MATAN AURE BIYU AKWAI DIYA (MAZA UKU) MATA (GOMA SHA BIYU) KUMA KUDI NE ZA A RABA MUSU NAIRA DUBU TALATIN DA UKU.

*Amsa*

Wa alaikum assalam Za'a bawa Mahaifiyarsa (5500) matansa biyu kuma za'a ba su (4125) su raba, ragowar (23375) sai a bawa Diyansa su rabe a tsakaninsu, duk namiji ya dau rabon mata biyu.

Allaha ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF  ZAREWA*

05/10/2018

Share:

Babu Bambanci Tsakanin Dan Zina Da Dan Halal A Wajen Rabon Gado ! - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamualaikum dan Allah tambaya nake yi mu biyar mamanmu ta haifa amma biyu daga cikinmu ta hanyan aure aka same su uku kuma ba tahanyar aure aka same su ba, shin sunada gadon ta ko,  ba su ? kuma ta mutu da bashi da yawa akanta kuma ba mu da hanyar biya mata shi domin kudin suna da yawa akalla yakai dubu dari biyu.
Dan Allah mafita muke nema, Mungode

*Amsa*

Wa alaikum assalam, idan mace ta yi cikin shege kuma ta haifi Da, daga baya ta mutu Dan zinar da ta haifa zai gaje ta, saboda Allah madaukakin sarki a cikin suratun Nisa'i aya ta : 10 ya yi wasiyya a bawa 'ya'yaye  gado, Dan zina kuma yana cikin jerin 'ya'yayen mahaifiyarsa, wannan yasa zai gaje ta.                                                                                                                                                               
Don haka babu Bambanci a cikinku tsakanin Wanda aka haifa ta hanyar aure da kuma Wanda aka samu ta hanyar Zina.
Ba'a raba gado sai an fara biyawa mamaci bashinsa, don haka ko da duk abin da ta bari zai kare dole Ku biya kafin a raba, kamar yadda Allah ya bayyana a cikin suratun Nisa'i aya ta (11).

Dan zina baya gadon mahaifinsa ko da kuwa mahaifin ya amince Dansa ne a wajan mafi yawan malamai.

Allah ne mafi sani.

*Dr. Jamilu Zarewa*

03/11/2018

Share:

Fatawar Rabon Gado (188) - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum malam mutum ne ya mutu  yabar mahaifi, mahaifiya,  mata, yar mace daya , da yan uwa wanda suke uwa daya uba daya Maza uku mata buyi.

*Amsa*

Wa alaikum assalam Za'a raba kashi (24), a bawa matarshi kashi uku,  mahaifiyarshi kashi hudu, 'yar shi kashi sha biyu, mahaifinsa kashi biyar.

Allah ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
06/11/2018
Share:

Fatawar Rabon Gado (187) - Dr Jamilu Yusuf Zarewa




*Tambaya*

Assalamu alaikum dafatan Malam Yatashi Lafiya.
dan Allah Malam Ya rabon gadon mutumin da ya bar mahaifi, mahaifiya,  mata, yara Maza biyu, da yan'uwa wanda suke uwa daya uba daya Maza uku mata biyu ?

*Amsa*

Wa alaikum assalam Za'a raba gida (24), a bawa matarsa kashi uku, mahaifiyarsa kashi hudu, babansa kashi hudu , ragowar sai a bawa yaransa su raba.

Allah ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
06/11/2018
Share:

Fatawar Rabon Gado (186) - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

ASSALAMU ALAIKUM MALAM MUTUM NE YA RASU YA BAR MAGADA KAMAR HAKA:
AKWAI UWA AKWAI MATAN AURE BIYU AKWAI DIYA (MAZA UKU) MATA (GOMA SHA BIYU) KUMA KUDI NE ZA A RABA MUSU NAIRA DUBU TALATIN DA UKU.

*Amsa*

Wa alaikum assalam Za'a bawa Mahaifiyarsa (5500) matansa biyu kuma za'a ba su (4125) su raba, ragowar (23375) sai a bawa Diyansa su rabe a tsakaninsu, duk namiji ya dau rabon mata biyu.

Allaha ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF  ZAREWA*

05/10/2018
Share:

Babu Bambanci Tsakanin Dan Zina Da Dan Halal A Wajen Rabon Gado ! - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamualaikum dan Allah tambaya nake yi mu biyar mamanmu ta haifa amma biyu daga cikinmu ta hanyan aure aka same su uku kuma ba tahanyar aure aka same su ba, shin sunada gadon ta ko,  ba su ? kuma ta mutu da bashi da yawa akanta kuma ba mu da hanyar biya mata shi domin kudin suna da yawa akalla yakai dubu dari biyu.
Dan Allah mafita muke nema, Mungode

*Amsa*

Wa alaikum assalam, idan mace ta yi cikin shege kuma ta haifi Da, daga baya ta mutu Dan zinar da ta haifa zai gaje ta, saboda Allah madaukakin sarki a cikin suratun Nisa'i aya ta : 10 ya yi wasiyya a bawa 'ya'yaye  gado, Dan zina kuma yana cikin jerin 'ya'yayen mahaifiyarsa, wannan yasa zai gaje ta.                                                                                                                                                               
Don haka babu Bambanci a cikinku tsakanin Wanda aka haifa ta hanyar aure da kuma Wanda aka samu ta hanyar Zina.
Ba'a raba gado sai an fara biyawa mamaci bashinsa, don haka ko da duk abin da ta bari zai kare dole Ku biya kafin a raba, kamar yadda Allah ya bayyana a cikin suratun Nisa'i aya ta (11).

Dan zina baya gadon mahaifinsa ko da kuwa mahaifin ya amince Dansa ne a wajan mafi yawan malamai.

Allah ne mafi sani.

*Dr. Jamilu Zarewa*

03/11/2018
Share:

Tuesday 30 October 2018

HUKUNCIN KOYAN ILIMIN TAURARI !!! Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum Dr. dafatan anwuni lafiya, Allah yasa haka amin.
Akwai wani abu mai kama da ilimi kuma kamar tsafi ta wani fuskar. A turanche ana kiran sa Astrology, har akwai Makarantu da ake karantar da course din a Jami'a, kama daga degree, masters har P.hd, wasu kuma suna sana'a dashi a kasashen waje, ta bangaren bada shawarwari.
Abin ya dogara ne da sanin taurari, juyawar duniya, rabe raben ruhi da sauransu. Sun raba ruhin Dan Adam gida hudu, akwai; Ruwa, Kasa, Iska da kuma Wuta.
Ko wane ruhi yana tare da wasu taurari wadanda ake ganesu ta hanyar sanin ranar haihuwar mutum. Masu irin wadannan ilimin suna iya fadan halin mutum, kuma a mafi yawanchin lokuta yana zama daidai. Suna bada shawarwari gameda abinda mutum zaiyi, har suna fadawa mutum chewa lura da taurari ko makamanchin haka, yanada sa'a a wuri kaza, ko kuma bashida sa'a. Suna fadan chewa wane yanada taurarin nasara ko kuma wani abu mai kama da haka.
Ina bibiyar abin a mafi yawanchin lokuta, har nafara fahimtan  wasu abubuwa gameda hakan.
Minene matsayin sharia

*Amsa*

Wa alaikum assalam, To dan'uwa  yin irin wannan nau'i na ilimin taurari haramun ne yana kuma iya kaiwa zuwa ga shirka, saboda  Camfi ne da kuma da'awar sanin Gaibu, wanda Allah ya kebanta da shi.

Imamu Katadah yana  cewa: "Allah ya halicci taurari ne saboda abubuwa guda uku kawai:

*1.* Gane hanya, kamar yadda Allah ya fada a suratu Annahl aya ta(16)
وعلامات وبالنجم هم يهتدون

*2.* Ado ga saman duniya.
*3.* Jifan kangararrun Shaidanu masu sato Ji daga sama, Allah madaukakin sarki yana cewa a suratul mulki aya ta (5)
ولقد زينا السماء الدنيا بمصابيح وجعلناها رجوما للشياطين.

Yin amfani da Taurari wajan gane Nasara ko rashinta harka ce ta Bokaye, kuma Allah bai tanade su don yin hakan ba, yana kuma kaiwa zuwa hallaka.

Ya halatta ayi amfani da ilmin Taurari wajan gane Alkibla da kuma tabbatar da maslahohin addini.
Don neman karin bayani duba Alkaulu al-mufid 2/102 da kuma Al-mulakkas fi-sharhi kitabittauhid (236)
Allah ne mafi sani

*Amsawa

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*

17/10/2018

Share:

HUKUNCIN KOYAN ILIMIN TAURARI !!! Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum Dr. dafatan anwuni lafiya, Allah yasa haka amin.
Akwai wani abu mai kama da ilimi kuma kamar tsafi ta wani fuskar. A turanche ana kiran sa Astrology, har akwai Makarantu da ake karantar da course din a Jami'a, kama daga degree, masters har P.hd, wasu kuma suna sana'a dashi a kasashen waje, ta bangaren bada shawarwari.
Abin ya dogara ne da sanin taurari, juyawar duniya, rabe raben ruhi da sauransu. Sun raba ruhin Dan Adam gida hudu, akwai; Ruwa, Kasa, Iska da kuma Wuta.
Ko wane ruhi yana tare da wasu taurari wadanda ake ganesu ta hanyar sanin ranar haihuwar mutum. Masu irin wadannan ilimin suna iya fadan halin mutum, kuma a mafi yawanchin lokuta yana zama daidai. Suna bada shawarwari gameda abinda mutum zaiyi, har suna fadawa mutum chewa lura da taurari ko makamanchin haka, yanada sa'a a wuri kaza, ko kuma bashida sa'a. Suna fadan chewa wane yanada taurarin nasara ko kuma wani abu mai kama da haka.
Ina bibiyar abin a mafi yawanchin lokuta, har nafara fahimtan  wasu abubuwa gameda hakan.
Minene matsayin sharia

*Amsa*

Wa alaikum assalam, To dan'uwa  yin irin wannan nau'i na ilimin taurari haramun ne yana kuma iya kaiwa zuwa ga shirka, saboda  Camfi ne da kuma da'awar sanin Gaibu, wanda Allah ya kebanta da shi.

Imamu Katadah yana  cewa: "Allah ya halicci taurari ne saboda abubuwa guda uku kawai:

*1.* Gane hanya, kamar yadda Allah ya fada a suratu Annahl aya ta(16)
وعلامات وبالنجم هم يهتدون

*2.* Ado ga saman duniya.
*3.* Jifan kangararrun Shaidanu masu sato Ji daga sama, Allah madaukakin sarki yana cewa a suratul mulki aya ta (5)
ولقد زينا السماء الدنيا بمصابيح وجعلناها رجوما للشياطين.

Yin amfani da Taurari wajan gane Nasara ko rashinta harka ce ta Bokaye, kuma Allah bai tanade su don yin hakan ba, yana kuma kaiwa zuwa hallaka.

Ya halatta ayi amfani da ilmin Taurari wajan gane Alkibla da kuma tabbatar da maslahohin addini.
Don neman karin bayani duba Alkaulu al-mufid 2/102 da kuma Al-mulakkas fi-sharhi kitabittauhid (236)
Allah ne mafi sani

*Amsawa

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*

17/10/2018
Share:

Friday 28 September 2018

Labarin Yajuju wa majooju - Zauren Fiqhu



LABARIN YAJUJU WA MAJOOJU


***********************************
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM

Tsira da aminci su tabbata bisa Mafi girman matsayi acikin dukkan halittun Allah, Shugabanmu Annabi Muhammadu Tare da iyalan gidansa tsarkaka da Sahbbansa zababbu.

Yau in sha Allahu muna tare da daliban ZAUREN FIQHU WHATSAPP (3) kuma zamu gudanar da darasinmu akan tarihin wasu Qabilu ne wadanda yanzu haka suna nan da ransu. Amma ba zasu bayyana ba, sai akarshen zamani. Sunansu YAJOOJU WA MAJOOJU.

Acikin Alqur'ani, Allah ya bamu labarin tafiye tafiyen da Sarki Dhul-Qarnaini yayi.

Acikin tafiye tafiyen nasa, yaje wajen da rana take faduwa, sannan yaje yaje mahudarta.

Sannan a tafiyarsa ta uku kuma yaje chan karshen duniya, kusa da bangon duniya.

Achan din ne mutanen wajen suka kawo masa Qara. Suka ce masa :

"YA KAI DHUL QARNAINI, HAKIKA YAJOOJU DA MAAJOOJU MASU 'BARNA NE ADORON QASA. SHIN KO ZAMU SANYA MAKA WANI HARAJI (WANDA ZAMU BAKA) DOMIN KA SANYA WATA KATANGA ATSAKANINMU DA TSAKANINSU?".

Shi kuma sai yace "ABINDA UBANGIJINA YA BANI, SHINE YAFI ALKHAIRI. KU DAI KAWAI KU TAIMAKENI DA QARFI (KARFIN JAMA'A)  ZAN SANYA WATA KATANGA MAI QARFI TSAKANINKU DA TSAKANINSU".

Daga nan Dhul-Qarnaini ya kama aiki, ya gina wata Katafariyar katanga ta Qarfe da dalma, wacce tafi Qarfin wadannan mutanen su haurata.

SHIN SU WANENE YAJOOJU WA MAJOOJU??

Bari mu leka cikin litattafan Tafseeri da hadisan Manzon Allah (saww) domin mu binciko labarinsu.

Al Imam Alqurtubiy (rah) daya daga cikin jerin Manyan Malaman tafseeri, yace "An samo hadisai da labarai dangane da fitowarsu da kuma siffofinsu. Kuma cewa suna daga cikin 'ya'yan YAFITHU ne.

Sayyiduna Abu Hurairah (rta) ya ruwaito daga Manzon Allah (saww) yana cewa:

"An haifa ma Annabi Nuhu ('ya'ya guda uku) SAAMU, da HAAMU, da YAFITHU.

Shi samu shine ya haifi Larabawa da Mutanen Farisa (Iran kenan) da kuma mutanen Ruum (turawa kenan). Kuma akwai alkhairi acikinsu.

Shi kuma YAFITHU shine ya haifi YAAJOOJ da MAJOOJU da Turkawa da mutanen Saqalib, amma babu alkhairi acikinsu.

Shi kuma HAAMU shine ya haifi Qibtawa (mutanen Misra) Da Barbar (berbers, wasu mutanen daji ne, masu tsananin Yaki) da kuma Bakaken fata".

Abu Sa'eed Alkhudriy (ra) ya riluwaito daga Manzon Allah (saww) yana cewa:

"(Su Yajooju wa Majooju) Mutum guda daga cikinsu ba zai mutu ba, har sai bayan ya haifi 'Ya'ya Maza guda dubu daga cikin tsatsonsa.

Imamul Qushairiy ya ambato Abu Sa'eed Alkhudriy yana cewa "SU QABILU ASHIRIN DA BIYAR NE ABAYAN SU YAJUJU WA MAJUJU. MUTUM GUDA DAGA CIKINSU DA KUMA CIKIN YAJOOJU WA MAJOOJU BA ZAI MUTU BA, HAR SAI NAMIJI GUDA DUBU SUN FITA DAGA CIKIN TSATSONSA.

Lallai bisa ga wadannan hadisan zamu iya cewa indai kowanne mutum guda daga cikinsu yana haifar mutum dubu, to lallai ba Qaramin yawa ne dasu ba.

Abdullahi bn Mas'ud (ra) yace: "Na tambayi Manzon Allah (saww) dangane da Yajooju wa Majooju, Sai shi Mai tsira da aminci) yake cewa :

"SU YAJUJU WA MAJOOJU AL'UMMATAI NE GUDA BIYU. (WATO YAJOOJU DABAN, MAJOOJU MA DABAN).

Kowacce Al'ummah daga cikinsu tana Qunshe da wasu Al'ummatai (ko Qabilu) guda dubu dari hudu (400,000 tribes). Kuma kowacce al-ummah babu wanda yasan iyakar yawansu sai dai Allah".

"KUMA MUTUM GUDA DAGA CIKINSU BA ZAI MUTU BA, HAR SAI BAYAN AN HAIFA MASA MAZAJE GUDA DUBU DAGA CIKIN TSATSONSA, KOWANNENSU YANA DAUKE DA KAYAN YAQI".

Sai wani Sahabi yace "Ya Rasulallahi, Siffanta mana su mana!".

Sai yace : "SU NAU'I UKU NE (KAMANNIN HALITTARSU).

1. AKWAI WADANDA SUKE (DA TSAWO) MISALIN BISHIYAR NAN TA URZU. WATA BISHIYA CE NAI TSAWON ZIRA'I 'DARI DA ASHIRIN.

2. SAI KUMA WASU NAU'I WADANDA TSAYINSU DA KAURINSU DUK 'DAYA NE - WATO ZIRA'I GUDA. (TSAWONSU ZIRA'I DAYA, KAURINSU MA HAKA).

3. SAI KUMA WANI NAU'IN WADANDA SUKE (DA MANYAN KUNNUWA) SUNA SHIMFIDA KUNNE 'DAYA SUYI KAFITA DASHI.

'DAYA KUNNEN NASU KUMA SUYI MAYAFI DASHI".

BA ZASU WUCE TA KUSA DA WATA GIWA KO NAMAN DAJI, KO ALADE (AL-HANZIR) BA, FACHE SAI SUN CINYESHI.

KUMA DUK WANDA YA MUTU DAGA CIKINSU MA, CINYESHI SUKE YI (WATO SUNA CIN NAMAN 'YAN UWANSU).

NA GABANSU SUNA KASAR SHAM, 'YAN BAYANSU KUMA SUNA KHURASAN (WATO AFGHANISTAN).

ZASU SHANYE KOGUNAN GABASHIN DUNIYA, KUMA ZASU SHANYE BUHAIRATUT TABRIYYAH (WANI KOGI NE A KASAR FARISA).

AMMA ALLAH ZAI KANGESU DAGA SHIGA GARIN MAKKAH DA MADINA DA BAITUL MAQDIS".

Sayyiduna Aliyu bn Abi Talib (ra) yace: "akwai wasu nau'i daga cikinsu wadanda tsawonsu kamar kamu guda ne (wato tsawon yatsa guda biyu).

Suna da farata (farce) da kuma Hakora irin na Zakoki. Da jiki irin na dabbobi, suna kuka irin na Kuraye, kuma suba taruwa kamar yadda tattabaru sukeyi.

Suna da gashi duk jikinsu, wanda yake karesu daga Sanyi da zafi.

Suna da manyan kunnuwa guda biyu. Daya kunnen na gashi ne. Suna fakewa daga Sanyi acikinsa. 'daya kunnen kuma na fata ne. Dashi suke fakewa alokacin zafi.

Suna tonon wannan katangar, sai sun kusan tureshi sai kuma Allah ya mayar dashi kamar yadda yake.

Sai sunce gobe zamu tureshi "IN SHA ALLAHU TA'ALA". Sannan zasu tureshi, su fito (zuwa cikin duniya).

Mutane zasu tsere daga garesu acikin manyan katangu da benaye (saboda suna kashewa duk mutanen da suka kama, sannan su cinye namansa 'danye).

Daga nan sai su rika harba kibiyoyinsu zuwa sararin samaniya, sai adawo musu da kibiyoyin chakude da jini.

Daga nan sai Allah ya sanya musu wata chuta (mai kamar tsotsa) a wuyansu, ya hallakar dasu.

Manzon Allah (saww) yace "NA RANTSE DA WANDA NUMFASHINA KE HANNUNSA, DABBOBIN DA SUKE DORON QASA SAI SUN QOSHI SUNYI KITSE SOSAI DAGA CIN NAMAN YAJOOJU WA MAJOOJU DA KUMA JININSU

Imamu Ahmad da Tirmiziy, da Ibnu Maajah ne suka ruwaitoshi.

Abu Sa'eed Alkhudriy (ra) yaji Manzon Allah (saww) yana cewa:

"Za'a bude ma Yajooju wa Majooju Qofa su shigo cikin duniya, kamar yadda Allah ya fada, "SUNA TAFIYA DA SAURI TA CIKIN DUKKAN SASANNI".

Mutane zasu firgita su gudu daga garesu, zasu fake daga garesu acikin katangu da birane. Kuma zasu taho da dabbobinsu ma tare dasu.

Mutanen Yajooju wa Majooju din zasu yi yawo adoron Qasa, zasu shanye duk ruwan dake doron Qasa.  Wani daga cikinsu zai wuce ta kusa da wani kogi, sai yace "Da chan kuwa, akwai ruwa anan wajen".

Bayan kowanne mutum ya riga ya buya daga garesu, sai wani daga cikin YAJOOJU WA MAJOOJU yace : "Wadannan duk Mazaunan doron Qasa ne, mun gama dasu. Saura yanzu mazauna cikin Sammai".

Sai wani daga cikinsu ya harba kibiyarsa zuwa sama, sai adawo masa da ita, tana jike da jini. Suna cikin wannan halin sai Allah ya turo musu da wata irin chuta awuyansu, kamar tsutsotsin nan na Aljaraad zasu kama wuyansu. Zasu mutu, ko motsinsu ba Za'a ji ba.

(Imamu Ahmad ne ya ruwaito).

Awata ruwayar kuma, Annabi Eisa (as) shine zai yi addu'a sai Allah ya turo da Mala'iku suzo su kawar da Gawarwakin YAJUJU WA MAJUJU din, bayan sun cika duniya da warinsu.

Anan zamu tsaya sai a karatu na gaba. In sha Allahu zamu dauko wani batun mu tattauna akai.

DAGA ZAUREN FIQHU WHATSAPP (3). 05/09/2015.
Share:

Sunday 23 September 2018

Shin ko kunsan Cewa Sallar Jana'Iza kabbarorinta suna wuce 4

*JANA'IZA A MAHANGAR SUNNAH??-07!!*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*KITABU WAS SUNNAH*
.
.
*ﻣﺠﻠﺲ ﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ*
📓📔
Watsaps
08036222795
09031200070
.
.
...
Yau 09-04-1439 wacce tayi dai dai da, 27-12-2017, Cigaban Lekca mai taken *JANA'IZA A MAHANGAR SUNNAH:*
...
=
Wannan shine bayani na Bakwai:
=
=
*«ﺇِﻥَّ ﺍﻟْﺤَﻤْﺪَ ﻟِﻠَّﻪِ، ﻧَﺤْﻤَﺪُﻩُ ﻭَﻧَﺴْﺘَﻌِﻴﻨُﻪُ، ﻣَﻦْ ﻳَﻬْﺪِﻩِ ﺍﻟﻠﻪُ ﻓَﻠَﺎ ﻣُﻀِﻞَّ ﻟَﻪُ، ﻭَﻣَﻦْ ﻳُﻀْﻠِﻞْ ﻓَﻠَﺎ ﻫَﺎﺩِﻱَ ﻟَﻪُ، ﻭَﺃَﺷْﻬَﺪُ ﺃَﻥْ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻟَّﺎ ﺍﻟﻠﻪُ ﻭَﺣْﺪَﻩُ ﻟَﺎ ﺷَﺮِﻳﻚَ ﻟَﻪُ، ﻭَﺃَﻥَّ ﻣُﺤَﻤَّﺪًﺍ ﻋَﺒْﺪُﻩُ ﻭَﺭَﺳُﻮﻟُﻪُ*
_Bayan haka yanzu kuma kai tsaye zamu shiga bayanine gameda Sallar jana'iza, Ita sallar gawa fardu kifaya ce wato wasu suna dauke ma wasu, idan akayi mutuwa a gari ko unguwa sai wasu jama'a koda 'yan kadanne daga cikin mutanen wannan unguwar suka tsayu sukaima wannan gawar sallah to shikenan babu zunubi ko laifi akan sauran jama'a wadanda basuzo akayi wannan sallar dasu ba, Amma mutane guda biyu sukuma ba dole bane sai anyi musu sallar gawa. Nafarko shine yaro qarami wanda bai balaga ba, idan yaro karami ya rasu to ba dole bane sai kunyi mishi sallah, kuna iya rungumar gawar kawai kuje ku birneta ba tareda kunyi mata sallah ba, amma dai babu laifi idan kunyi sallar saboda akwai gagarumin lada wanda ake samu idan akayiwa gawa sallah kunga sai ku rabauta da wannan ladan, na biyu kuma shine shahidi wanda ya mutu a fagen jihadi shima wannan ba dole bane akanku sekunyi masa sallah, amma dai shima din kuna iya yin masa sallan dan ku samu ladanda ake samu bawai saboda yin sallar wajibi bane****_
      _Sannan kuma wannan sallar anso yazama ansamu a qalla sahu uku koda kuwa mutanen basuda yawa koda basu wuce mutane gomaba inso samune arabasu zuwa sahu uku, inkuma sunyi yawa to ana iya qara yawan sahun yafi uku*****_
      _Kuma ya halasta ayima gawa sallah acikin masallaci, amma bai halasta ayi sallar a tsakanin qaburbura ba, wato qabarine guda biyu ko sama da haka sai a ajjiye gawa a tsakaninsu sai ayimata sallah anan wajan wannan bai halastaba kenan dai zamuce baya halasta ayima gawa sallah acikin maqabarta****_
     _Sannan kuma idan gawar namijine to limamin zai tsayane saitin kansa idan kuma mace ce liman zai tsaya tsakiyarta daidai saitin qugunta****_
      _Yadda akeyin sallar kuwa shine: Anayin kabbara hudu, ko biyar ko shida ko bakwai ko takwas ko tara, amma anfi yin guda hudu sedai ana duba darajar mamacin da irin gwagwarmayar da yayi wajen cigaban addini sai ayi masa kabbarorin gwargwadon yadda akaga ya kamata walau biyar ko shidan har zuwa tara****_
       _Amma yanada kyau shi liman kafin afara sallah ya gayawa mutane cewa kabbara kaza zamuyi, sedai kuma fadin hakan ba dole bane akan liman amma dai kyautatawace dan susan abinda zakayi, sannan kuma yanada kyau kagaya musu bayan kowacce kabbara ga abinda ake karantawa saboda mafiya yawan mutane sallar kawai sukeyi amma basusan mene ake fadi abayan kowacce kabbara ba, wannan kuma yafarune saboda irin yadda mutane mukayi sakaci da karatu muka kauracewa malamai babu ruwanmu da yin sallah kamar yadda Annabi (s.a.w) ya koyar kawai dai munayin sallah ne kamar yadda mukaga wadansu mutane sunayi, wanda kuma hakan babu shakka kuskure ne yazama wajibi akanmu lallaine mutashi munemi ilimin addininmu saboda yazama duk ibadarda zamu aikata to munayintane akan basira dakuma haske na ilimi****_
        _Hujja kuwa akan cewa ana yin kabbarori sama da hudu a sallar gawa daga ciki akwai hadisi wanda Imamu Muslim ya ruwaito acikin littafinsa hadisi mai lamba 957, Abu Dawuda 3181, Tirmizi 1028, Ibnu Majahi 1505****_
       _Hujjarmu kuma akan cewa anayin  kabbarbari masu yawane da gwargwadon irin gudun muwarda mamacin yaba addini, Akwai hadisin Sallar gawar Imrana Dan Hussaini wanda Aliyu dan Aby Dalib ne yayi masa kabbarori tara, gakuma sallar gawar Sahlu dan Hanif wanda shima dai Aliyu dinne yayi masa sallah da kabbarori shida, sannan ya fuskanci mutane yace aishi Sahlu ya halarci yaqin badar, wannan hadisin yana cikin Ahkamul Jana'iz shafi na 113, Har ila yau kuma akwai sallar gawar Abu Qatada wadda itama dai Sayyidina Ali ne yayi kuma yaimasa kabbara bakwai shima Abu qatada ya halarci yaqin badar****_
      _Hakadai sayyidina Aliyu yakasance yanayin kabbarori shida zuwa sama akan duk sahabinda ya halarci yakin badar, amma sahabinda baije badar ba Aliyu yanayin masa kabbara biyar ne, Tabi'i kuma wanda ba sahabi ba Aliyu yanayi masa kabbara hudu****_
      _Kankat kuma idan muka duba hadisin Sallar gawar Sayyidina Hamza Annabi (s.a.w) yaimasa kabbarori guda tara shima, Imamu Dahawi ya ruwaito wannan acikin Sharhu Ma'anil Athar mujallad na farko shafi na 290*****_
=
=
_Zan tsaya anan saikuma darasi nagaba idan Allah yakaimu***_
.
_Almajirinku ne kamar kullun_
.
```Jameel Alhassan Haruna kabo```
.
_(Abu khausar)_
.
 .
Allah ta,ala ya tsaremu
.
.
.
Zaku iya samun shafinmu na facebook tawannan hanyar
https:/t/m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-1522000298067561/
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Subhanak Allahumma wabi hamdika ash hadu anla ila ha illa h anta astagfiruka  Wa,atubu ilaika
Share:

Thursday 16 August 2018

[Audio] :- Karyarku 'Yan Shi'a Asirinku Ya Tonu - Sheikh Kabiru Haruna Gombe

Sheikh : _*MUHAMMAD KABIRU HARUNA GOMBE*_
( *Sakataren kungiyar Izala ta kasa*)


Asabar : *11 August 2018*


Wuri : *Masallacin Sultan Bello Kaduna*

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAUKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇🏼👇🏼👇🏼

DOWNLOAD AUDIO NOW

_*Kar  Ku  Sake  A  Baku  Labari .........*_

Ayi Sauraro  Lafiya  👂🏻



Share:

Wednesday 8 August 2018

HUKUNCIN WANDA YA SADU DA MATARSA ACIKIN HAILA

HUKUNCIN WANDA YA SADU DA MATARSA ACIKIN HAILA :

TAMBAYA TA 2547
*******************
SALAMUN ALAIKUM MALAM MENENE HUKUNCIN WANDA YASADU DA MATARSHI TANA HAILA AMMA ARASHIN SANI ?

NAGODE MALAM.

AMSA
*******
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Allah Madaukakin Sarki ya haramta wa Mazaje saduwa da Matayensu alokacin da suke cikin jinin haila. Allah yace :

"SUNA TAMBAYARKA GAME DA JININ HAILA, KACE (MUSU) SHI NAJASA NE. KU NISANCI MATAYE ACIKIN FARJOJINSU KADA KU KUSANCESU (DA JIMA'I) HAR SAI SUNYI TSARKI".

(Suratul Baqarah ayah ta 223).

Kuma akwai hadisin da Manzon Allah (saww) yace Wanda yayi jima'i da matarsa alhali tana haila,  to sai yayi sadaqah da dinare guda (Kamanin naira dubu sittin ₦60,000).

Acikin Maluman Fiqhu akwai wadanda suka tafi bisa doron hadisin. Akwai kuma wadanda suka ce zai yi istighfari ne tunda ya aikata babban laifi. Amma babu kaffara akansa.

Imamun Nawawiy yace "Da ache mutum zai aikata haka (wato jima'i da mai haila) cikin Mantuwa ko rashin sanin cewa tana haila, ko rashin sanin haramcinsa to babu laifi akansa kuma babu kaffarah.

Amma idan mutum ya aikata hakan da gangan, tare da sanin cewa akwai hailar, da kuma sanin haramcinsa, to hakika ya dauki zunubi mai girma kuma wajibi ne gareshi ya tuba".

Kuma acikin maganar wajibcin yin kaffarar akwai zantuka guda biyu. Amma abinda yafi inganci shine babu kaffarah akansa".

WALLAHU A'ALAM.

DAGA ZAUREN FIQHU (30/07/2018  17/11/1439).
Share:

Tamabaya da Amsa :- Shin yana hallatta macce budurwa tashafa turaree Sannan tafito waje dashi??

*|```Assalamu alaikum*```
*```Malam ko ya hallatta macce budurwa tashafa turaree Sannan tafito waje dashi??*```



_*AMSA:*_
*******

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،


Haramun ne mace ta sanya turare ta fita inda wasu maza zasuji kamshinsa. Dalili kuwa shine:


ﺛﺒﺖ ﻋﻦ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺃﻧﻪ ﻗﺎﻝ: ﺃَﻳُّﻤَﺎ ﺍﻣْﺮَﺃَﺓٍ ﺍﺳْﺘَﻌْﻄَﺮَﺕْ ﻓَﻤَﺮَّﺕْ ﻋَﻠَﻰ ﻗَﻮْﻡٍ ﻟِﻴَﺠِﺪُﻭﺍ ﻣِﻦْ ﺭِﻳﺤِﻬَﺎ ﻓَﻬِﻲَ ﺯَﺍﻧِﻴَﺔٌ.
ﺭﻭﺍﻩ ﺍﻹﻣﺎﻡ ﺃﺣﻤﺪ‏(19212‏) ﻭﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ ‏(5126‏) ﻭﺣﺴﻨﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ.

_Ya tabbata daga *Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam)* yace idan mace ta sanya turare ta wuce ta gaban mutane (Maza) domin suji kanshin turaren ta, toh ita mazinaciya ce._
*Imam Ahmad ya ruwaito shi a hadisi mai lamba 19212.* da *Nisaa'i hadisi mai lamba 5126.*
_Albani ya inganta shi Cikin sahihul jami'i._


ﻋَﻦْ ﺯَﻳْﻨَﺐَ ﺍﻣْﺮَﺃَﺓِ ﻋَﺒْﺪِ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺑﻦ ﻣﺴﻌﻮﺩ، ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﺎ ﻭﻋﻦ ﺯﻭﺟﺎ، ﻗَﺎﻟَﺖْ: ﻗَﺎﻝَ ﻟَﻨَﺎ ﺭَﺳُﻮﻝُ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺻَﻠَّﻰ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻭَﺳَﻠَّﻢَ: ﺇِﺫَﺍ ﺷَﻬِﺪَﺕْ ﺇِﺣْﺪَﺍﻛُﻦَّ ﺍﻟْﻤَﺴْﺠِﺪَ ﻓَﻠَﺎ ﺗَﻤَﺲَّ ﻃِﻴﺒًﺎ.
ﺭﻭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ ‏(443).

_An karbo daga *Zainab* matar *Abdullahi Ibn Mas'ud* (radiyallahu anha Wa zaujaha) tace: *Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam)* yace damu; Idan dayanku zata tafi masallaci kada a shafa turare._
*Muslim ya ruwaito shi a hadisi mai lamba 443.*



والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_
Share:

Tuesday 7 August 2018

Hukunce-Hukuncen Mai Takaba ?? Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

*HUKUNCE-HUKUNCEN MAI TAKABA*


*Tambaya:*

Assalamu alaikum wa rahmatullaah. gafarta Malam pls ayi mana bayani koda a takaice ne dangane da hukunce - hukuncen takaba... Na shiga wajen mahaifiya dazu, take cewa in tambaya mata Malamai tanadin shari'a akan wannan al'amari. Nagode


*Amsa:*

Wa alaikum assalam.To dan'uwa ina rokon Allah ya jikan mahafinku, akwai hukunce-hukunce  da suka shafi takaba, ga muhimmai daga ciki:

*1.* Mai takaba za ta zauna a gidan mijinta ba za ta fita ba, har sai ta gama iddarta, wacce take wata hudu da kwana goma, kamar yadda aya ta: 234 a suratul Bakara take nuni zuwa hakan .

*2.* Ba za ta saka kaya masu kyau ba, don haka za ta guji ado, kamar yadda hadisin Abu-dawud mai lamba ta: 2304, ya yi bayanin hakan.

*3.* Shari'a ta hana mai takaba ta sanya turare, kamar yadda hadisin Bukhari mai lamba ta: 5343, ya tabbatar da hakan,

*4.* Malamai suna cewa mai takaba ba za ta sanya tozali ba , kamar yadda hadisin Nasa'i mai lamba ta: 3565 ya bayyana hakan.

*5.*  An hana mai takaba yin lalle,  kamar yadda hanin ya zo a hadisin Abu-dawud mai lamba ta: 2304.

*6.* Idan wata bukata ta kama za ta iya fita daga gida, ko da rana ne ko da dare.

*7.* Za ta iya yin Magana da mazan da ba muharramanta ba, idan bukatar hakan ta kama, saidai ta guji, sanyaya murya, kamar yadda aya ta 32 a suratul-ahzab ta hana sanyaya murya ga wadanda ba muharramai ba.

*8.* Babu wani launi na kaya na musamman da aka shar'anta mata ta sanya, don haka, duk kayan da ba kwalliya a jikinsu ya halatta ta sanya su .

*9.* Za ta iya yin wanka da sabulun da yake ba mai kanshi ba .

*10.* Za ta iya zama ta yi hira da makusantanta, har ma za ta iya bude gashin kanta, idan su duka muharramanta ne .

*11.*  Bai halatta wani ya nemi auranta ba, har sai ta gama idda, saidai za'a iya yin jirwaye mai kama da wanka, kamar yadda aya ta 235 ta yi nuni zuwa hakan.

*12.* Idan mai takaba tana da ciki, to iddarta ita ce:  haife abin da take dauke da shi, kamar yadda hadisin Subai'a mai lamba ta: 5014 a Sahihul Bukhari ya tabbatar da hakan.

Allah ne mafi sani.

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*

27\3\2015
Share:

Sunday 1 July 2018

Tufka da Warwara!!! Daga Dr.Muhammad Rabi'u R/lemo

*TUFKA DA WARWARA!!!*
Daga👇🏽
*Dr. Muhammad Rabi'u R/ Lemo*

Kullum ihu suke suna siffata malamai masu kira zuwa ga sunnah da bin tafarkin magabata da Yan Ikhwan, suna kira a nisance su, a nisanci majalisansu da wuraren karantarwarsu da wa'azinsu, amma su suna cikin jami'o'in da suke cike da yan Ikhwan din na hakika, kai! Har ma da wadanda suke zagin addinin da masu addinin, suna zama aji su karantar da su, amma su daidai suke yi, su ne salaf, alhali da yawa daga cikin malaman da suke suka da batawa suna sun yi karatu ne wurin manya-manya malaman sunnah, sun halacci majalisan su, sun zauna da su.
Haka nan da zaka dawo tarihin wadannan masu ihun ba a kan salafiyya malaman mu suke ba, zaka taras mafi yawancinsu ba su fahimci addini da ilimin addini ba, sai ta hanyar wadannan malamai ko almajiransu, su ne suka kama hannunsu zuwa ga ilimi da sunnah, amma yau su ne yan Ikhwan, wanda da zaka tambaye su tsakani da Allah, tunda kuke karatu wurinsu ko wurin almajiransu, sun taba kiranku ga wata kungiya wai ita Ikhwan, za su ce maka, a'a. To ta yaya yanzu suka zama yan Ikhwan.

Na rantse da Allah babu wani abu da suke sukan malaman mu da shi, suke siffata su da yan Ikhwan saboda shi, face sai ka samu, su da malaman da suke ganin su ne kadai yan salafiyya suna cikin irin wannan abun.

Dan uwa ka maida hankali ga karatunka, ka watsar da rudu da hayaniya.
Allah ka jikan malaman mu, wadanda suka kare rayuwarsu wajen yada sunnar Annabinka (S.A.W) irin su :  Sheikh Abubakar Mahmud Gumi, sheikh Isma'il Idris, Sheikh Ja'afar, Sheikh Albani Zari'a, da sauran malaman Sunnah. Ameen.

Daga
*ZAUREN FIQHUS SUNNAN* / *MINBARIN SUNNAH*
Share:

Thursday 28 June 2018

Tambaya da Amsa :- Shin yana halatta ga Mutum bayan yayi zina da mace, kuma ya Aureta ??

*```Assalamu alaikum Malam yana halatta ga mutum bayan yayi zina da mace, yana halatta ya aure ta?*```


_*AMSA:*_
*******

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ


A shari'ance baya halatta ga mutum ya auri wacce yayi Zina da ita har sai sun tuba _*(Taubatan Nasuuhan)*_ su biyun.

*TUBA* yana tabbatuwa ne idan mutum yayi nadama akan abinda ya aikata da yin kyakkyawar niyyar bazai sake aikatawa ba.

Saboda haka idan sun tuba kuma sunyi nadamar abinda sukayi kuma sunyi alwashin bazasu sake aikatawa ba, to yana halatta agaresu suyi aure abisa ra'ayin mafi yawan malamai.

*Ibn Qudaamah (rahimahullah)* yace: Idan mace tayi Zina, to baya halatta ga Wanda yasani ya aureta har sai an cika sharudda biyu;
*1.* Ta gama iddarta.
*2.* Ta tuba daga Zinar da ta aikata
      Idan wadannan sharuddan sun cika, to ya halatta a aureta abisa ra'ayin lafiya yawan malamai, wannan shine ra'ayin Abubakar Al-siddiqu, Umar ibn Khaddab, Ibn Umar, Ibn Abbaas, Jaabir, Sa‘eed ibn Al-Musayyab, Tawoos, Jaabir Ibn Zayd, Ata’, al-Hasan, Ikrimah, Az-Zuhri, ath- Thawri, Ash-Shaafa‘i, Ibn Al- Mundhir da Ashaab ar-ra’y.
_*(All-Mughni , 7/108.)*_


والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_
Share:

Tambaya da Amsa:- Menene Hukuncin mata masu huda Hanci ??

*```ASSALAMU ALAIKUM!!!*```
*```MENENE HUKUNCIN MATA MASU HUDA HANCI??*```



_*AMSA:*_
********


وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ


An tambayi _*Shaykh Muhammad Saalih Al-Uthaymeen (Rahimahullah)*_ gameda Huda Hanci da Huda kunnuwa da ake yiwa yara mata saboda suyi kyau? Sai yace:
Ra'ayin da yake daidai shine babu laifi akan Huda kunne, saboda daya daga cikin dalilan huda kunne shine sanya halatattun kayan ado (Yan Kunne). An san cewa mata sahabbai sunada yan kunne da suke sanyawa a kunnuwansu.

Zafin ciwon hudawar mai sauki ne, kuma idan anyi huduwar ne a lokacin da yarinya tana karama, yafi saurin warkewa.


Abinda ya shafi *HUDA HANCI* kuma bazan iya tina cewa malamai sunce wani abu akan Huda Hanci ba, amma dai wani nau'in ne na canza halitta da gurguntawa idan muka kalli fuskar daga wajenta, duk dayake wasu basa kallonsa ta wannan fuska.

Idan mace tana acikin kasa ko gari Wanda sanya kayan ado a Hanci ana kallonsa wani nau'i ne na kwalliya da ado, to, babu wani abin laifi ga huda Hanci.
_*(Majmu'ul Fataawa Ibn Uthaymeen, shafi na 11, tambaya ta 69).*_



والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_
Share:

Wednesday 27 June 2018

Maganin Fitsarin Kwance daga Zauren Fiqhu

MAGANIN FITSARIN KWANCE :

TAMBAYA TA 2161
****************
Assalamu'alaikum Malam muna lafia, ya aiyuka ya Dalibai? Allah yayi mana jagoranci na alheri. Amin.

Malam Dan Allah a taimaka mana da maganin fitsarin kwance, wata  diyar yar'uwata ce ta kusa shekara 10 take fama dashi.

Sannan kuma ina barar addu'arka data dalibanka akan Allah ya kawo mani mijin aure mafi alheri. Amin. Jazakallahu Khair. Pls hide my I. D.


AMSA
***
Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Ita wannan matsalar ana iya shawo kanta ne ta hanyoyi guda biyu kamar haka :

MAGANI : A nemi kwayoyin habbatus sauda, a rika yiwa yaro hayaki dasu. Kuma yana dan tsugunawa akan hayakin. Sannan kuma a rika gauraya masa habbatus sauda din yana shan cokali guda tare da zuma. Ko kuma ya shafe jikinsa da man Habbatus sauda din wanda akayi tofi acikinsa. In sha Allahu zai dena.

2. ADDU'A : Arika tofa masa wannan addu'ar, ko kuma akoya masa ya rika yinta da kansa, ko kuma a rubuta masa ajikin takarda ya sanya ajikinsa yayin da zai kwanta.

Kamar yadda aka ruwaito daga Abdullahi bn Amru bn Al-As Sahabin Manzon Allah (saww) yana rataya ma 'ya'yansa Qanana wannan addu'ar. Gata nan kamar haka :

"أعوذ بكلمات الله التامات من غضبه وعقابه ومن شر عباده و من همزات الشياطين و أن يحضرون".

'A'udhu bi kalimatil Laahit tammati min ghadhabihee wa 'iqabihee wa min sharri ibadihee wa min hamazatish shayateen wa an yahdhurooni.

FASSARA : Ina neman tsari da cikakkun kalmomin nan na Allah daga fushinsa da Uqubarsa, kuma daga sharrin bayinsa, kuma daga sharrin fizge-fizgen shaitanu, kuma (ina neman tsarinsa) kada su halartoni.

In sha Allahu koda babban mutum ne yake fama da matsalar fitsarin kwance, in dai ya lazimci wadannan abubuwan tare da gaskatawa zai ga biyan bukatarsa.

WALLAHU A'ALAM.

Muna rokon Allah da albarkar sunayensa da siffofinsa da kalmominsa, ya baki Miji nagari. Ya tsare miki mutuncinki da imaninki dake da dukkan dalibanmu da 'yan uwanmu Mata marassa aure. Ameeen.

DAGA ZAUREN FIQHU.
Share:

Tambaya da Amsa :-Hukuncin yin sallar jam'i A Gida !!! Dr. Jamilu yusuf zarewa

*_HUKUNCIN YIN SALLAR JAM'I A GIDA !!!_*

*_Tambaya_*

Assalamu alaikum.  Malam mene hukuncin sallar  namiji da ba ya son zuwa masallaci  jam'i saidai ya tara iyalinsa a gida ayi sallah tare?


*_Amsa_*
Wa alaikum assalam

To 'yar'uwa Malamai sun yi sabani game da sallar jam'i a masallaci.

1. A wajan malaman Malikiyya zuwa sallar jam'i sunna ne saboda fadin Annabi S. A.W. "Sallar jama'a tafi sallar mutum daya da lada ashirin da bakwai" hadisin yana nuna ingancin sallar wanda ya yi sallah shi kadai, tun da an tabbatar masa da lada daya.

2. Ya wajaba yin sallah a masallatai a cikin jama'a saboda fadin Annabi (SAW)  "Na yi niyyar na yi umarni a tsayar da sallar jam'i, ni kuma na je na kona gidajan wadanda ba Sa halarta sallah a masallaci" wannan ita ce maganar Malamai da yawa.
Ibnu-Mas'ud yana cewa: "Babu wanda yake kin zuwa sallar jam'i sai munafiki, wanda aka san  shi da munafunci,  akan kawo mutum ranga-ranga ba shi da lafiya a tsayar da shi a tsakanin Sahu".
Wani Makaho ya zo wajan Annabi (SAW)  ya nemi ya yi masa izni ya yi sallah a gida saboda ba shi  da Jagora, ya ba shi izni,  bayan ya tafi sai ya Kira shi ya ce masa kana jin kiran sallah? sai ya ce E, sai ya ce to ka amsa".

Allah yana cewa a Suratul Bakara aya ta (43): "Kuma ku yi sallah tare da masu yin sallah"

A bisa dalilan da suka gabata za mu fahimci cewa: Yin sallar jam'i a masallaci shi ne abin da Shari'a ta zo da shi, kuma wajibi ne ga wanda yake da iko, tun da ga shi har Annabi (SAW) ya yi niyyar zai kona gidan wadanda ba sa halarta.
Idan akwai nisa tsakaninsa da masallaci ko kuma yana da lalura ba za'a ce ya aikata haramun ba in ya yi sallah a gida tare da iyalansa saboda fatawar Malikiyya da ta gabata da kuma aya ta karshe a suratul Hajj wacce take nuna sauki da rashin kunci a addinin musulunci.

Allah ne mafi sani.

*_Dr. Jamilu Zarewa_*

27/06/2018

Daga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*
Share:

Tuesday 26 June 2018

Tambaya da Amsa :- Idan mutum ya rasu ya bar Mata guda daya1 da 'ya'ya maza guda uku 3 da 'ya mace guda daya1, kuma ya bar dukiya ta miliyan takwas da dubu 'dari biyar (8.5million). Ya Kason kowa zai kasance?

*```Assalamu alaikum*```
*```Tambaya na shine:*```
*```Idan mutum ya rasu ya bar Mata guda daya1 da 'ya'ya maza guda uku 3 da 'ya mace guda daya1, kuma ya bar dukiya ta miliyan takwas da dubu 'dari biyar (8.5million). Ya Kason kowa zai kasance?*```




_*AMSA:*_
*******

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،



Abu Na farko daza'a aiwatar akan dukiyar mamaci shine biyan bashi da wasiyya, kafin a shiga gundumar rabon gado.


Idan namiji ya rasu yabar mata daya da yara maza uku (3) da 'ya mace daya.
Idan wadannan sune magadansa kadai wadanda ya bari.

To anan kason matar zai kasance 1/8 (Sumuni) Na dukiyar da yabari, 'yarsa daya mace za'a bata Rabin kason namiji daya.
Kamar yadda Allah ya fada acikin Suratun Nisaa'i ayah ta 11 da 12.

ﻳُﻮﺻِﻴﻜُﻢُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻓِﻲ ﺃَﻭْﻟَﺎﺩِﻛُﻢْ ۖ ﻟِﻠﺬَّﻛَﺮِ ﻣِﺜْﻞُ ﺣَﻆِّ ﺍﻟْﺄُﻧْﺜَﻴَﻴْﻦ

Allah yana yimuku wasiyyah acikin 'ya'yanku, namiji yanada rabon mata biyu.........(Nisaa'i 11)


ﻭَﻟَﻬُﻦَّ ﺍﻟﺮُّﺑُﻊُ ﻣِﻤَّﺎ ﺗَﺮَﻛْﺘُﻢْ ﺇِﻥْ ﻟَﻢْ ﻳَﻜُﻦْ ﻟَﻜُﻢْ ﻭَﻟَﺪٌ ﻓَﺈِﻥْ ﻛَﺎﻥَ ﻟَﻜُﻢْ ﻭَﻟَﺪٌ ﻓَﻠَﻬُﻦَّ ﺍﻟﺜُّﻤُﻦُ ﻣِﻤَّﺎ ﺗَﺮَﻛْﺘُﻢْ ﻣِﻦْ ﺑَﻌْﺪِ ﻭَﺻِﻴَّﺔٍ ﺗُﻮﺻُﻮﻥَ ﺑِﻬَﺎ ﺃَﻭْ ﺩَﻳْﻦ

........Kuma (Su Matan) sunada rubu'i daga abinda kuka bari (Na dukiya) idan reshe ('ya'ya) bai kasance ba gareku, to, idan kuwa reshe ya kasance gareku, to sunada sumuni (1/8) daga abinda kuka bari, daga bayan wasiyya wanda kukayi ko kuma bashi (debt)............(Nisaa'i 12).

Reshe acikin ayah ta 12 yana nufin 'ya'ya. Idan miji ya mutu yabar mata ita kadai babu 'ya'ya, to rabon ta shine 1/4.

Idan kuma akwai 'ya'ya to rabonta shine 1/8 kamar yadda ya tabbata a ayar.

A tambayar mu ta sama. Namiji ya rasu yabar masu gadonsa kamar haka:
1. Mata daya
2. Yara Maza uku (3)
3. Yarinya daya

Sannan yabar kudi naira miliyan takwas da dubu dari biyar:
N8,500,000

Ga yadda kason kowa zai kasance:

MATA
******
Za'a bata 1/8 Na N8,500,000
Shine ya kama miliyan daya da dubu sittin da biyu da naira dari biyar.

====N1062500


Idan an cire rabon matarsa, za'a bar N7,437,500.

Anan maza uku ne, kowanne kashi biyu za'a bashi, mace kuma kashi daya.

Idan ka hada kashi biyu sau uku zai baka kashi shida.
       (2×3)=6

Sannan a tara da kashi daya Na mace zai bamu kashi bakwai
6+1=7

Yanzu zamu raba N7,437,500 zuwa gida bakwai

(N7,437,500/7)==N1062500.

Mace kashi daya
Kowanne namiji kashi biyu.

Kashi biyu zai bamu
1062500+1062500
      ==N2,125,000


YARA MAZA
**************
Kowannensu zai samu " Naira Miliyan biyu da dubu dari da ashirin da biyar"

======N2,125,000


'YARSA MACE
***************
Zata samu "Naira miliyan daya da dubu sittin da biyu da naira dari biyar"

======N1,062,500.




والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_
Share:

Sunday 20 May 2018

Hikimomin da Azumi ya kunsa....Dr.jamilu yusuf zarewa

*HIKIMOMIN DA AZUMI YA KUNSA*

*Tambaya:*

Assalamu alaikum Don Allah malam a taimaka min da bayani game da sababin da yasa ake yin azumi??

*Amsa:*

Wa alaikum assalam Azumi ginshiki ne, daga cikin turakun musulunci, wadanda addinin musulunci, ba zai cika ba sai da su, Allah da manzonsa sun yi umarni da shi, saboda wasu muhimman manufofi, ga wasu daga ciki :

*1.* Samun tsoron Allah, saboda mai azumi yana barin abin da yake so saboda Allah, hakan zai sa, ya kara samun tsoron Allah.

*2.* Samun kariya daga Shaidan, saboda azumi yana takure hanyoyin Shaidan, wannan ya sa zunubai suke karanci a Ramadan.

*3.* Tuna talakawa da wahalar da suke ciki, saboda duk lokacin da mai kudi ya dandana yunwa zai tuna halin da talakawa suke ciki .

*4.* Sabawa rai wajen barin abin da take so, da kuma hakuri akan abin da take sha'awa.

*5.* Kankare zunubai da kuma samun daukakar daraja, saboda azumi yana gyara zuciya, da kuma rai.

*6.* Samun lafiyar jiki, saboda azumi yana kariya daga cututtuka masu yawa, kamar yadda likitoci suka tabbatar da hakan.

*7.* Ta hanyar azumi mutum zai saba da yin aikin don Allah, saboda azumi sirri ne tsakanin Allah da bawansa.
Allah ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
29/1/2013

Daga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*
Share:

Ramadhaniyyat@1439H [3] - Sheikh Dr. Muhd Sani Umar R/lemo

*Ramadhaniyyat@1439H [3]*

*Daga Sheikh Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*

Tahajjudi

Allah Ta'ala yana cewa:
(Da daddare kuwa sai ka yi tsayuwar dare da shi (Alqur’anin) qarin (daraja) ne gare ka, tare da qaunar Ubangijinka ya tashe ka a matsayin sha-yabo ("watau matsayin mai ceto"). Isra'i, aya ta 79.

A Makka ne Allah ya shar'ata wa Annabinsa (S.A.W) tsayuwar dare watau sallar "Tahajjudi". Wannan dalili ne da yake nuna falalar wannan salla. Domin Allah ya shar'anta Annabi (S.A.W) mafi girma kuma mafi falalar ayyuka a Makka. Shar'anta wani aiki tun a farkon Musulunci dalili ne dake nuna girmansa da falalarsa, saboda haka ne ma aka shar'anta Tauhidi tun a Makka, hakanan aka kuma shar'anta wasu daga cikin rukunan Musulunci tun a farko-farkon Musuluncin.
Share:

Audio:-Darasin Tafsirin Al-Qur'an na Watan Ramadan 1439/2018 - Dr.Muhammad SANI Umar R/Lemo

Darasin Tafsirin Al-Qur'an na Watan Ramadan 1439/2018

Rana ta 0(2)

Tare da Dr.Muhammad  SANI Umar R/Lemo

17-05-2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO A WAYOYINKU SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya.


Share:

Audio:-Ramadan Tafsir 1439/2018 ( Darasi na 2) - Sheikh Abdurrazaq Yahaya Haifan



Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 2

Tare da: Sheikh Abdurrazaq Yahaya Haifan

2/9/1439
18/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO A WAYOYINKU SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya.


Share:

Audio:-Ramadan Tafsir 1439/2018 (Darasi na 2) - Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 2

Tare da: Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo

2/9/1439
18/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO A WAYOYINKU SAIKUBSHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya.


Share:

Audio:-Ramadan Tafsir 1439/2018 ( Darasi na 1) - Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tare da: Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya.


Share:

Audio:- Ramadam Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) - Dr. Jabir Sani Maihula



Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tare da: Dr. Jabir Sani Maihula

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇


Ayi saurare Lafiya.


Share:

Audio:- Ramadam Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) - Sheikh Muhammad Kabiru Haruna Gombe

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tare da: Sheikh Muhammad Kabiru Haruna Gombe

2/9/1439
18/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya


Share:

Saturday 19 May 2018

Audio:- Ramadam Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) - Sheikh Abdurrazaq Yahaya Haifan

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Suratul Ibrahim Ayah 1-5

Tare da: Sheikh Abdurrazaq Yahaya Haifan

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya.


Share:

Audio:- Ramadan Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) - Dr. Muhammad Mansur ibrahim sokoto

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Suratul Nur 1-2

Tare da: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

Malam yaja hankali sosai akan masifar da take fadawa Mazinci

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya
Share:

Friday 18 May 2018

Audio:- Ramadan Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) -.Sheikh Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tare da: Sheikh Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya.
Share:

Audio:- Ramadan Tafseer 1439/2018(darasi na 1) - Mal. Umar shehu Zaria

TAFSIRIN RAMADAN 1439/2018

Darasi na 1

Daga bakin: _Umar Shehu Zaria_

Alhamis 1 Ramadan, 1439 (17/05/2018). Masallacin Aliyu Usman Kurmin Mashi, Kaduna.

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya


Share:

Archive

Unordered List

Support