Zan Iya Auran Wanda Ba Shi Da Uba ? - Dr Jamilu Yusuf Zarewa ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 20 November 2018

Zan Iya Auran Wanda Ba Shi Da Uba ? - Dr Jamilu Yusuf Zarewa



Tambaya

Assalamu Alaikum, Don Allah Malam, wata dalibata ce ke neman shawara kan auren wani mutumin kirki, amma baida uba !!!
Wane irin kalubale ku ke hange a kanta, a yanzu da nan gaba?
Me ye mafi alkhairi a gare ta?
Jazakumullahu bikhairin Malam. Bissalam


Amsa

Wa alaikum assalam
Mutukar ta yarda da addininsa da kuma dabi'unsa tana iya auransa kamar yadda hadisin Tirmizi ya tabbatar.

Kasancewar an haife shi ba ta hanyar aure ba, ba laifinsa ba ne, Allah ba ya dorawa wani laifin wani.

In dai shegantuwarsa ba ta shahara a tsakanin mutane ba, ta yadda nan gaba za'a dinga aibanta abin da kuka haifa tare, kina iya auransa, tun da mutumin kirki ne.

Duk da cewa ya halatta a shariance ki auri wanda ba'a san mahaifinsa ba, saidai idan kika ji tsoran tozarta zuriyarki, to ana barin halal don kunya, kamar yadda Hausawa suke fadi kuma dalilin sharia ya tabbatar.

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

17/11/2018
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support