MAZINACI DA MAZINACIYA IDAN BASU TUBA BA, ZASU HADU DA BALA'O'I GUDA GOMA SHA BIYAR KAMAR HAKA ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 14 November 2017

MAZINACI DA MAZINACIYA IDAN BASU TUBA BA, ZASU HADU DA BALA'O'I GUDA GOMA SHA BIYAR KAMAR HAKA

MAZINACI DA MAZINACIYA IDAN BASU TUBA BA, ZASU HADU DA BALA'O'I GUDA GOMA SHA BIYAR KAMAR HAKA :

⚫ BALA'O'I GUDA BIYAR TUN DAGA NAN DUNIYA :

1. Zubewar Imani (hadisi yace duk mai yin zina bashi da imani alokacin da yake aikatawa).

2. Zubewar Mutuncinsu (su kansu sun san cewa basu acikin lissafin mutanen kirki awajen Allah da bayin Allah).

3. Lalacewar Zuriyyarsu (Duk wanda yayi zina sai anyi da 'Yarsa ko 'Yar Uwarsa ko Qanwarsa).

4. MUMMUNAN TALAUCI : Zina tana haifar musu da mugun talauci. da kuma rashin albarkar duk abinda ya shigo hannunsu.

5. MUMMUNAR JINYA : Jinya acikin zuciyark
Su (bushewar zuciya), ko kuma ajikinsu (Qanjamau, Ciwon sanyi, da sauransu).


⚫ BALA'O'I GUDA BIYAR ACIKIN QABARINSU :

1. Rashin Kyawun Qarko, ko kuma rashin cikawa da Imani (idan ba suyi sa'a sun tuba ba).

2. Tsananin Matsi da duhun Qabari. (saboda rashin kulawarsu da ibada tun aduniya).

3. Rashin samun kyakyawar addu'a daga bayin Allah. (Allah ba zai sanya tausayinsu azukatan al'ummah ba, balle su tunasu, suyi musu addu'a).

4. Za'a nuna musu mummunan mazauninsu acikin Jahannama,  tare da sauran Mazinata.

5. Ci gaba da samun Qaruwar zunubai akansu saboda alhakin 'ya'yan mutane wadanda sukayi lalata dasu, suka gurbata musu rayuwa.


⚫ BALA'O'I GUDA BIYAR ARANAR ALQIYAMAH:

1. Za'a tashesu acikin Qungiyar Manyan Mazinata, akarkashin tutarsu. (SUBHANALLAH).

2. Mummunan ruwa mai Mugun doyi zai rika fita daga cikin al'aurorinsu.

3. Mummunan Hisabi da wulakantuwa agaban dukkan halittun Allah, Mala'iku zasuyi shelar cewa KUN GA WANNAN MAZINACI NE!! (KO KUMA KUN GA WANNAN MAZINACIYA CE!! ).

4. Za'a sanyasu acikin Kwazazzabon Jahannama,  kuma kunamai da macizai zasu rika cizonsu. Ga kuma tsananin bugu daga Mala'ikun Azaba.

5. Allah ba zai dubesu da rahamarsa ba..

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN!!!

ZAUREN FIQHU ya rairayo wannan ne daga ingantattun hadisai acikin Littafin AHWALUL QUBOOR na Ibnul Jawzee da Kuma KITABUL KABA'IR na Zahabiy.

Wannan tunatarwa ce. duk wanda yaga dama ya dauki hanyar tuba zuwa ga Ubangijinsa. Allah mai gafara ne, kuma mai karbar tuba ne.

DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990 (07-11-2014).
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support