Menene hukuncin mutumin da yake take wandonsa, shin ya halatta a bi shi salla? ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 7 November 2017

Menene hukuncin mutumin da yake take wandonsa, shin ya halatta a bi shi salla?

*TAMBAYA DA AMSA DAGA SHEIKH MUHAMMAD BELLO AHMAD AL-ADAMAWIY, RAHIMAHULLAH*

*001*

*TAMBAYA*
Assalamu alaikum, Mene ne hukuncin mutumin da yake take wandonsa, shin ya halatta a bi shi salla?

*AMSA*
Take wanda a Musulunci haramun ne domin hadisai masu yawa sun zo suna hani akan haka, kuma ba lallai sai wando ba.

Manzon Allah, sallallahu 'alaihi wa sallama, ya ce:

 *"مَا أَسْفَلَ مِنْ الْكَعْبَيْنِ مِنْ الْإِزَارِ فَفِي النَّارِ"* رواه البخاري (5787).

Duk abun da ya wuce idon sawu (na tufafi), to yana wuta. Bukhari ne ya ruwaito hadisi na 5787.

Malamai suka ce tun da har Allah Ta'ala Ya yi barazana da wuta, to wannan ya nuna babban laifi ne.

Dangane da batun bin shi salla matukar babu najasa a jikin tufan shi za a bi shi salla, domin laifin mai laifi bai hana a karɓa sallansa matukar ya yi ta yanda shari'a ta koyar kamar yadda Abdullahi Bn Umar ya yi salla a bayan Hajjaj Bn Yusuf al-Thaqafee.

Wallahu A'alam.

✍🏼Tattarawa:
*_Umar Shehu Zaria_*
Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support