November 2017 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Thursday 30 November 2017

MAFI DADIN ABINDA NA KARANTA A YAU

*MAFI DADIN ABINDA NA KARANTA A YAU*


تمنى إبراهيم الخليل أن يكون أبوه مسلماً ولم يشأ الله له رغم أنه أبو خليله ... !!!

Annabi Ibrahim yayi fatan mahaifinshi ya musulunta, amma Allah bai ga damar hakan ta kasance ba, duk da cewa baban babbanmasoyinshi (bada'dayin) ne....

وتمنى نوح العبد الشكور أن يكون ابنه مسلما  ويأبى الله رغم دعاء نوح ...!!!

Haka nan Annabi Nuhu bawa mai yawan godiya ga Allah, yayi fatan danshi ya musulunta, amma Allah ya'ki hakan ta kasance, duk da addu'ar da Annabi Nuhu yayi...

وتمنى محمد  صل الله عليه وسلم أن يسلم عمه ولم يكتب الله له هداية رغم أنه نصر الرسول في دعوته ...!!!

Haka nan Annabi Muhammad S.A.W yayi fatan Baffan shi (Abu 'dalib) ya musulunta, amma Allah bai rubuta mishi shiriya ba, duk da irin taimakon da ya bawa Annabi wajen ya' da da'awar shi....

وجعلني وجعلك مسلماً دون سؤال وأعطانا ما لم يعط إبراهيم في أبيه ونوحًا في ابنه ومحمدًا صل الله عليه وسلم في عمه ..

Amma Allah ya sanya ka ya sanya ni muka zamto musulmai ba tare da mun ro'ka ba, ya bamu abinda bai bawa Annabi Ibrahim ba dangane da mahaifinshi, bai bawa Annabi Nuhu ba dangane da 'danshi, bai bawa Annabi Muhammad S.A.W ba dangane da Baffan shi..!!!

أي فضل هذا ... !!!!! ؟
( إِنَّ اللَّهَ لَذو فَضلٍ عَلَى النّاسِ وَلكِنَّ أَكثَرَ النّاسِ لا يَشكُرونَ )
Wannan Wace irin falala ce....!!!!
"hakika Allah ma'abocin falala ne ga mutane, sai dai mafi yawan mutane basu da godiya "

نعمة اﻹسلام ترجح لو وزنتها بكل النعم ..
الحمد لله الذي هدانا لهذا وما كنا لنهتدي لولا ان هدانا الله ..


Ni'imar musulunci ta rinjayi dukkan wata ni'ima da za'a auna.....
Godiya ta tabbata ga Allah da ya shiryar damu da hakan, kuma bamu kasance masu shiryuwa ba, ba don Allah ya shiryar damu ba.

الحمد لله حتى يبلغ الحمد منتهاه
Godiya Ta tabbata ga Allah, iya matu'kar kurewar godiya.

*Fassara* :
*Malam Anas Assalafy Fagge*

Daga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*


Share:

Saturday 25 November 2017

Audio :- Muhimmancin Amana A Wajen Musulmi - Dr. Muhammad Sani Umar R/Lemo

Muhadara

Mai taken: Muhimmancin Amana A Wajen Musulmi

Tare da: Dr. Muhammad Sani Umar R/Lemo

30/2/1439
19/10/2017​



Download Audio Now

Share:

Naga Wandona A Jike Da Maniyyi Bayan Na Kammala Sallar La'asar? Dr Jamilu Yusuf Zarewa


Tambaya

 Aslamualaikum MALAM na tashi da janaba nayi salar asuba da azahar da kuma laasar, duk nayi sallah sai bayen naje wanka da yemma naga wando na da alamun manniyi shin ya ingancin sallolina na baya ? nagode

Amsa

Wa alaikum assalam, mutukar ka tabbatar a baccin asuba maniyyin ya fito, to ya wajaba ka sake asuba da azahar da la'asar din.

In har ka yi wani baccin bayan azahar to za ka danganta janabar ne zuwa ga baccin karshe da ka yi, ta yadda sallar da ka yi bayan baccin karshe ita za ka sake, kamar yadda Imamu Malik ya rawaito a Muwadda daga Sayyady Umar.
Allah ne mafi sani 

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
13/11/2017
Share:

Siffofin Aboki Nagari !!! Dr Jamilu Yusuf Zarewa

*Tambaya:*

Assslamu alaikum Malam ina da abokai da yawa, amma ina so ka ba ni shawara?

*Amsa:*

Wa alaikum assalam, To dan'uwa Aboki yana da mutukar mahimmanci a rayuwar mutum, idan ya zama abokinka mutum ne mai himma, sai kai ma ka samu himma kamar yadda ake cewa zama da madaukin kanwa yana kawo farin kai, haka nan idan ya zama mutumin banza sai ya yi maka tasiri, Abu Musa Al’ash’ari ya rawaito hadisi daga Annabi ((s.aw.)) yana cewa (misalin aboki na gari da abokin banza, kamar misalin mai daukar turare ne da mai hura zuga-zugi, mai daukar turare ko dai ya shafa maka ko ka sayi turare a wurinsa ko kuma ka ji kamshi mai dadi a wurinsa, mai hura zuga- zugi kuma ko ya kona maka kaya ko ka ji wari a wurinsa) Bukhari ne ya rawaito
Kuma wani malami yana cewa:
• idan ka kasance a cikin mutane, to ka yi abota da zababbensu, kada ka yi abota da halakakke saiku halaka tare.
• Idan kana so ka san waye mutum, to ka tambayi abokinsa, saboda kowanne aboki da abokinsa yake koyi .
Wani kuma yana cewa:
• Kar ka aboci malalaci a kowanne hali, da yawa mutumin kirki yana lalacewa ne idan ya hadu da mara kirki.
• Dakiki yana saurin tasiri akan mai kokari, ba ka ganin garwashe idan aka saka shi a toka shi ma sai ya zama toka.
Da fatan za ka kula da abin da ya gabata.
Allah na mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
11/11/2017
Share:

Wanda Ya Zage Ka, Yafi Wanda Ya Yabe Ka !!!Dr Jamilu Yusuf Zarewa



salamu alaikum Malam wani yana ta zagina ba abin da na yi masa, ina neman shawara ?

*Amsa:*

Wa alaikum assalam To dan'uwa Ibnuhazm Azzahiry (456) yana cewa a cikin littafinsa Assiyar Wal-aklaak : "Wanda ya zage ka yafi wanda ya yabe ka, saboda wanda ya yabe ka ko dai ya fadi abin da kake da shi, ko kuma ya fadi abin da ba ka da shi.
idan ya fadi abin da kake da shi bai kare ka da komai ba, idan kuma ya fadi abin da baka da shi to ya cutar da kai.

Wanda ya zage ka kuwa : ko dai ya aibantaka da wani hali da kake da shi ka ga hakan sai ya sa ka gyara, ko kuma ya aibanta ka da halin da baka da shi , sai ya zama ya maka tanaji a lahira."

Daya daga cikin magabata ya hadu da wani sai ya ci mutuncinsa, sai ya ce masa dan jira kadan, ya shiga gida ya tuba ga Allah kankan da kai zuwa gare shi.
Bayan ya fito mutumin ya kasa zaginsa sai ya ce me ya faru da kai ? sai ya ce: Na tuba ga Allan da ya dora ka a kaina.
Da yawa zagin da mutane suke maka wani zunubi da ka aikata ya jawo maka.
Allah ne mafi sani

 *Amsawa* ✍🏻 

                                                                               *DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
11/11/2017
Share:

Zan Iya Rantsuwa Da Al-Qur'ani ? Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*TAMBAYA*
Salamun alaikum Dr. Don Allah mene ne hukuncin rantsuwa da Al-Qur'ani?, kamar ka ce: Alquran.

Allah Ya kara ma Dr. Lfy Amin.

*AMSA*
Wa alaukum assalam, Ya halatta mana tun da qur'ani sifa ne daga cikin sifofin Allah .

Annabi S.A.W. Yana cewa: "Duk wanda zai yi rantsuwa, to ya rantse da Allah ko kuma ya yi shiru" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta: (6270).

Rantsuwa da Allah ya kunshi rantsewa da daya daga cikin sunayanSa ko daya daga cikin sifofinSa, kamar yadda malamai suka yi bayani.

 kasancewar daga cikin sifofin Allah akwai zance,  kuma Al-Qur'ani maganar Allah ce ba halittarsa ba, kamar yadda aya ta: (6) a suratu Attaubah ta yi bayani, hakan sai ya halatta rantsuwa da shi.

Allah mafi sani.

✍🏼Amsawa:
*_Dr Jamilu Yusuf Zarewa_*
09/11/2017.
Share:

kada Tufar Musulmi Ta Wuce Idon Sawu Dr Ibrahim Jalo Jalingo



Duk inda Musulmi yake wajibi ne ya daure ya bi Allah a cikin suturar da yake sanyawa; watau wajibi ne ya tabbatar da cewa wandonsa, ko rigarsa, ko alkebbarsa ba su kasance kasa da idanun sawunsa ba. Wannan shi ne abin da Allah Ya wajabta masa a wannan babin.

Lalle ba daidai ba ne mutum musulmi a bisa zabinsa, da ganin damarsa, saboda kawai neman ado ya je ya biya tela kudi ya dinka masa Zunubi da Bala'I; watau: wandon da ya zarce idon sawunsa, ko rigar da ta zarce idon sawunsa, ko alkebbar da ta zarce idon sawunsa. Lalle wannan Bala'I ne babba cikin wannan Al'ummah Muhammadiyyah.

Imam Malik ya ruwaito Hadithi na 1,631 cikin Muwataa, da Imam Ahmad Hadithi na 11,023 cikin Musnad, da Abu Dawud Hadithi na 4,095 cikin Sunan, da Nasaa'iy Hadithi na 9,633 cikin Sunan, da Ibnu Majah Hadithi na 3,573 cikin Sunan, da Ibnu Hibban Hadithi na 5,447 cikin Sahih, da Dabaraaniy Hadithi na 13,113 cikin Muujam, da Ibnu Abi Shaibah Hadithi na 25,318 cikin Musannaf da isnadi sahihi daga Abu Sa'id Al-Khudriy ya ce: Manzon Allah mai tsira da amincin Allah ya ce:-
((ازرة المسلم الى نصف الساق، ولا حرج فيما بينه وبين الكعبين، ما كان أسفل من الكعبين فهو في النار، من جر إزاره بطرا لم ينظر الله اليه)).
Ma'ana: ((Suturar Musulmi zuwa tsakiyar kwabri ne, amma babu laifi cikin abin da ya kasance tsakaninsa da idanun sawu, abin da kuma ya kasance kasa da idanun sawu wannan shi yana cikin Wuta, wanda kuma suturarsa ta ja kasa saboda nuna ado sam Allah ba zai dube shi ba)).

Sayyidina Abubakar Allah Ya kara masa yarda ya kasance Idan ya dan gafala mayafinsa na jan kasa, Sannan nan da nan sai ya daga shi; kamar yadda Imam Ahmad da Baihaqiy suka ruwaito.

Saboda fa'idah ga wasu ayyuka da maganganun Sahabbai game da isbaalin sutura:-
روى الامام النسائي في السنن: ٩٦٢٠ عن ابن عباس رضي الله عنه قال: ((ان الله لا ينظر الى مسبل)).
وروى الدارمي في السنن: ٢٨١٠ عن عبادة بن قرط قال: ((إنكم لتأتون أمورا هي ادق في اعينكم من الشعر كنّا نعدها على عهد رسول الله صلى الله عليه وسلم من الموبقات. فذكر لمحمد يعني ابن سيرين فقال: صدق فارى جر الإزار من ذلك)).
وروى ابن ابي شيبة في المصنف: ٢٥٣٢٤ عن أنس بن مالك قال: ((الإزار الى نصف الساق أو الى الكعبين، لا خير فيما هو أسفل من ذلك)).
وروى ابن ابي شيبة في المصنف: ٢٥٣٢٦ ان عمر دعا بشفرة فرفع ازار رجل عن كعبيه ثم قطع ما كان أسفل من ذلك)).
وروى ابن ابي شيبة في المصنف: ٢٥٣٢٧ عن ابي إسحاق قال: ((رأيت ناسا من اصحاب رسول الله صلى الله عليه وسلم ياتزرون على أنصاف سوقهم؛ فذكر اسامة بن زيد، وابن عمر، وزيد بن أرقم، والبراء بن عازب)).
وروى ابن ابي شيبة في المصنف: ٢٥٣٣١ ان عثمان بن عفان كان إزاره الى نصف ساقيه، قال: فقيل له في ذلك؟ فقال: هذه ازرة حبيبي، يعني النبي صلى الله عليه وسلم)).

Allah Ka tausaya wa wannan Al'ummah Ka cusa mata ganin kyawun abin da duk yake sunna ce ta ManzonKa. Ameen.
Share:

Hadarin Zama Da Mace Daya!!! Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa


Zama da mace daya yana kawo illoli da dama ga magidanci da su mata kansu da kuma
al`umma.
****
ILLOLI GA MAGIDANCI.

1:-Yana rage masa nishadin aure.
2:-Yana kawo tsufa da wuri.
3:-Yana saka maigida cikin damuwa
4:-Yana saka wa mace ta rika daga masa kai, tayi masa yadda taso saboda ta san ba shi da yadda zai yi.
5:-Yana rage masa samun soyayya da tarairaya da kulawa da ya cancanta a matsayinsa na maigida. 
6:-Yakan hana shi tantance so na gaskiya daga bangaren matarsa ko wanin haka.
****
ILLOLI GA SU MATAN.

1:-Yana hana wadansu samun mazajen aure.
2:-Yana dorawa matar gida aiyukan da suka shige misali kamar, kulawa da maigida,  yaran gida da ita ma kanta. 
3:-Yakan hana mace samun isasshen hutu da kuma lokacin kulawa da kanta.
4:-Yana rage wa mace kuzarin nuna soyayya ga maigidanta.
5:-Yana saka matar gida cikin tsoro da fargaba maras yankewa na ko za ai mata kishiya.
6:-Yana haifar da rashin amincewarta ga maigidanta da dauwamar da tuhuma ta har abada.
7:-Yana saka mace cikin shirin yaki da dawainiyar dakon makamai marasa ranar yankewa na nuna kin ayi mata kishiya. 
8:-Yana saka mata yawan zargi ga dukkan matan da suke da alaka da maigidanta ko ma wace iri ce koda ma yar uwa ce ko abokiyar kasuwancinsa. 
9:-Yana kara mata zafin kishi da rashin nutsuwa marasa ranar yankewa.

****
ILLOLIN GA AL`UMMA
1:-Yana haifar da karuwai mata marasa aure.
2:-Yana bunkasa yawan zawarawa acikin al`umma.
3:-Yana dorawa al`umma karin nauyin kulawa da mata iyayen marayu da marayun kansu. 
4:-Yana bunkasa zinace-zinace a cikin
al`umma.
5:-Yana rage tausayi da son bada taimako da agaji daga zukatan al`umma. 
6:-Yana kara saka fargaba da tsoro a zukatan iyaye wadanda suke da `ya`ya mata a gaba. 
7:-Yana bunkasa kasuwar malaman tsibbu da bokaye.

WADAN NAN SU NE KADAN DAGA ILLOLIN ZAMA DA MACE DAYA, 
DA FATAN MAGIDANTA ZASU GANE, 
SU KUMA MATA ZA SU TAIMAKAWA JUNANSU WAJEN TUNAWA MAI GIDA YA QARA AURE.
Share:

Wednesday 22 November 2017

Hadarin Zama Da Mace Daya !!! Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Zama da mace daya yana kawo illoli da dama ga magidanci da su mata kansu da kuma
al`umma.
****
ILLOLI GA MAGIDANCI.

1:-Yana rage masa nishadin aure.
2:-Yana kawo tsufa da wuri.
3:-Yana saka maigida cikin damuwa
4:-Yana saka wa mace ta rika daga masa kai, tayi masa yadda taso saboda ta san ba shi da yadda zai yi.
5:-Yana rage masa samun soyayya da tarairaya da kulawa da ya cancanta a matsayinsa na maigida. 
6:-Yakan hana shi tantance so na gaskiya daga bangaren matarsa ko wanin haka.
****
ILLOLI GA SU MATAN.

1:-Yana hana wadansu samun mazajen aure.
2:-Yana dorawa matar gida aiyukan da suka shige misali kamar, kulawa da maigida,  yaran gida da ita ma kanta. 
3:-Yakan hana mace samun isasshen hutu da kuma lokacin kulawa da kanta.
4:-Yana rage wa mace kuzarin nuna soyayya ga maigidanta.
5:-Yana saka matar gida cikin tsoro da fargaba maras yankewa na ko za ai mata kishiya.
6:-Yana haifar da rashin amincewarta ga maigidanta da dauwamar da tuhuma ta har abada.
7:-Yana saka mace cikin shirin yaki da dawainiyar dakon makamai marasa ranar yankewa na nuna kin ayi mata kishiya. 
8:-Yana saka mata yawan zargi ga dukkan matan da suke da alaka da maigidanta ko ma wace iri ce koda ma yar uwa ce ko abokiyar kasuwancinsa. 
9:-Yana kara mata zafin kishi da rashin nutsuwa marasa ranar yankewa.

****
ILLOLIN GA AL`UMMA
1:-Yana haifar da karuwai mata marasa aure.
2:-Yana bunkasa yawan zawarawa acikin al`umma.
3:-Yana dorawa al`umma karin nauyin kulawa da mata iyayen marayu da marayun kansu. 
4:-Yana bunkasa zinace-zinace a cikin
al`umma.
5:-Yana rage tausayi da son bada taimako da agaji daga zukatan al`umma. 
6:-Yana kara saka fargaba da tsoro a zukatan iyaye wadanda suke da `ya`ya mata a gaba. 
7:-Yana bunkasa kasuwar malaman tsibbu da bokaye.

WADAN NAN SU NE KADAN DAGA ILLOLIN ZAMA DA MACE DAYA, 
DA FATAN MAGIDANTA ZASU GANE, 
SU KUMA MATA ZA SU TAIMAKAWA JUNANSU WAJEN TUNAWA MAI GIDA YA QARA AURE.
Share:

Tuesday 14 November 2017

ABOKAI KALA HUDU NE - Zauren fiqhu

ABOKAI KALA HUDU NE
*************************
Hakika kowanne mutum da Allah ya bama daukaka ko daraja awani fanni na rayuwa, dole zai samu masoya kala-kala. Kamar yadda kuma zai iya samun Makiya da Mahassada nau'i daban daban.

1. Akwai wanda yake da'awar cewa shi Masoyinka ne. Amma ba zai tashi matsowa jikinka ko kuma nuna maka soyayya ba, sai lokacin da yaga wata nasara ta samu gareka. Amma idan kishiyar nasara (wato Asara) ta samu, ba zaka ganshi ba. Dama ni'imar ce ta kawoshi.

- Wannan ba abokin kirki bane, ba masoyin gaske bane. Kayi hankali dashi.

2. Akwai wanda yana nan tare dakai ko yaushe, amma duk abinda kasa agaba sai ya tayaka kuyi. Ba ya yi maka musu, ko gyara acikin lamarinka koda ya ganka akan kuskure haka zai tayaka kuyi.

- Wannan masoyi ne amma yana da rauni acikin soyayyarsa. Kayi hankali dashi.

3. Akwai wanda yana tare dakai ko yaushe amma idan yaga abin alkhairi tare dakai sai ya binne labarin. Idan kuma yaga mummunan abu tare dakai sai ya watsa ma duniya. Ta wajensa ake samun Miyagun labarai game dakai.

- Wannan Makiri ne, Mahassadi ne. Ka nisanceshi tun kafin yayi maka illa. Idan kuma ba zai yiwu ka nisanceshi ba, to lallai ne ka rika boye masa sirrinka.

4. Akwai masoyin da ko yaushe yana tare dakai azuciyarsa ko kuma afili. (Koda ba ya yi maka zakin kalamai).

Duk lokacin da ya ganka akan alkhairi sai ya taimakeka kuyi. Idan kuma ya ganka akan kuskure sai ya gyara maka koda ranka ba yaso.

- Wannan shine masoyi na gaskiya. Ka rikeshi da kyau domin irinsa suna da wahalar samu.

Hakika Allah yana cewa:

"MASOYA AWANNAN RANAR (WATO ALKIYAMAH) SASHENSU ABOKAN GABA NE GA SASHE. SAI DAI MASU TSORON ALLAH".

Wato aranar Alqiyamah abokai zasu zamanto masu Qin gamuwa da abokansu, saboda tsoron ko zasuyi jayayya dasu agaban Allah.

 Amma wadanda suka gina abotarsu bisa gaskiya da rikon amanar juna da tsoron Allah, sune zasu rabauta.

Zasu zama sanadiyyar samun rahama ga junansu (Kamar yadda hadisai da dama suka tabbatar).

Ya Allah ka hadamu da mutanen kirki masu Qaunarka, kuma wadanda Soyayyarmu dasu zata amfanemu awajenka.

Ka rabamu da miyagun abokai na fili da boye. Ka kiyayemu daga sharrinsu da makircinsu. Ameeen.

Wannan sadaukarwa ce ga dukkan abokai da Masoya.

DAGA ZAUREN FIQHU WHATSAPP -3 07064213990 {08-11-2016} 08-02-1438.
Share:

LABARIN ABU HANIFAH DA WANI KAFIRI- Zauren fiqhu

LABARIN ABU HANIFAH DA WANI KAFIRI
*****************************************
Watarana acikin garin Baghdad akwai wani babban kafiri wanda bai yarda da tauheedi ba, kuma bai yarda da cewa akwai Allah ba.

Har ma ya kirkiri wasu tambayoyinsa na shirme yana ta neman wanda zai amsa masa su. Duk Maluman garin sun kyaleshi basu daukeshi da muhimmanci ba, shi kuma yana ci gaba da bankaurarsa.

Alokacin nan Imam Abu Hanifah (rah) yana yaro Qarami bai fi shekara goma ba. Watarana yazo wucewa sai yaji mutumin nan yana da kurarin cewa wai Musulmai sun kasa amsa tambayoyinsa.

Sai Imam Abu Hanifah ya matsa kusa dashi yace masa "In sha Allahu ni zan amsa tambayoyin naka komai wahalarsu".

Mutumin ya amsa gayyatar, Kuma Jama'a suka cika da mamaki. Ta yaya wannan 'dan Qaramin yaro zai iya jayayya da Kafirin nan wanda manyan Maluma suka kasa ja dashi!

Da ranar Mukabalar tazo sai Jama'ar garin gaba daya suka taru a wani fili a tsakiyar garin Baghdad wanda dama anan ake gabatar da duk wani Muhimmin taro.

Sai shi wannan kafirin ya hau kan tudun dake tsakiyar taro. Sannan ya bude muryarsa ya jefo tambayarsa ta farko zuwa ga Abu Hanifah kamar haka :

"SHIN MENENE ALLAHN NAKU YAKE YI A DAIDAI YANZU?"

Abu Hanifah ya tsaya yayi tunani na 'yan mintuna kadan, sai yace ma mutumin "To ina so kai ka sauko Qasa, ni kuma in hau sama sannan in baka amsarka".

Wannan yaro Qaramin yaro 'dan shekara goma (wato Imam Abu Hanifah) ya hau saman kan tudun sannan yace "Ya Allah kaine shaida gareni agaban duk wadannan Mutanen cewar na shaida lallai yanzun nan kai ka Qaddara saukowar wannan kafiri zuwa Qasa, kuma ka Qaddara cewar Mumini zai hau sama (wato zai daukaka akansa)".

Da Mutane ('yan kallo) suka ji wannan amsar ta fito cikin fasaha daga bakin Abu Hanifah, sai suka fara kabbara "Allahu Akbar!" Allahu Akbar!"

Tun daga nan kafirin nan ya fara ganin Qaskanci. Amma sai ya sake jefowa tambayarsa ta biyu "SHIN MENENE YAKE RAYE KAFIN ALLAHN NAKU?" (Subhanallah).

Imam Abu Hanifah (rah) yayi tunani zuwa wani lokaci sai yace ma kafirin ya Qidaya masa lambobi daga goma zuwa Qasa.

Sai kafirin ya fara "Goma, tara, takwas, bakwai, shida, biyar, hudu, uku, biyu, daya, sufiri"

Sai yaron (wato Imam) yace masa "Shin me ka gani bayan sufiri (wato zero)?". Mutumin yace "Babu komai kafinsa, ni ban sani ba".

Da jin haka sai Imam yayi murmushi yace masa "To gashi nan ka riga ka bama kanka amsa.. Hakika Allah shine rayayye kuma dawwamamme. Babu kowa kuma babu komai kafinsa".

Daga wannan sai waje ya rude da kabbara,  suna Qara jinjina ma Imam Abu Hanifah (rah).

Kafirin nan zuciyarsa ta harzuka, ransa ya baci. Sai ya jefo tambayarsa ta Qarshe "SHIN YANZU WAJEN INA (WACCE KUSURWA) ALLAHN NAKU YAKE KALLO?" (Shin gabas yake kallo ko yamma ko kudu ko Arewa?).

Imam Abu Hanifah bayan yayi tunani zuwa wani lokaci sai yace a kawo masa Fitila (Aci-balbal ko kuma kyandir). Da aka kawo masa sai ya damka wa kafirin nan. Yace masa ya kunna masa.

Bayan kafirin ya kunna kyandir din sai ya tambayi Imam to menene dalikin haka?.

Sai Imam Abu Hanifah yace masa "Shin wanne waje ne wutar hasken kyandir din nan take kallo?"

Sai kafirin yace "Tana kallon dukkan kuskuwoyi ne. (wato gabas, yamma, kudu, arewa, sama da Qasa) Babu inda bata kallo"

Sai Imamu yace masa "Ai ka riga ka amsa tambayarka. Hakika Hasken Allah ya mamaye ko ina. Yana nan ako ina, babu wajen da babu shi".

Daga nan sai mutane suka rude da kabbarori "Allahu Akbar! Allahu Akbar!! Allahu Akbar!!!".

Shi kansa wannan kafirin yayi mamakin ilimi da basirar yaron nan. Don haka anan wajen ya furta kalmar Shahada, ya zama Musulmi kuma ya zama Almajirin Imam Abu Hanifah (ra).

Yardar Allah ta tabbata gareka Ya Imam Abu Hanifah. Allah ya saka muku da alkhairi bisa hidimar da kukayi ma addininsa.

Ya Jama'a wadannan fa sune wadanda suka yiwa addinin Allah hidima, suka rairayo mana garin Ilimi, suka dafa mana tuwonsa yanzu muke ci.

Amma abun Mamaki sai kaji mutum ya hura lasifika yana kushesu yana fadin cewa basu iya ba, shi ya fisu iyawa, ko kuma Malaminsa ya fisu.

Su fa sun rayu ne acikin mafiya alkhairin zamanunnuka, a Qalla dai sun riski wadanda suka ga Sahabbai. Kuma duk Mutanen da sukayi zamani dasu sun tabbatar da nagartarsu da gaskiyarsu.

Allah shi bamu albarkar masu albarka. Ameeen.

DAGA ZAUREN FIQHU WHATSAPP -1 Juma'ah 11-11-2016 (11-02-1438).
Share:

MAZINACI DA MAZINACIYA IDAN BASU TUBA BA, ZASU HADU DA BALA'O'I GUDA GOMA SHA BIYAR KAMAR HAKA

MAZINACI DA MAZINACIYA IDAN BASU TUBA BA, ZASU HADU DA BALA'O'I GUDA GOMA SHA BIYAR KAMAR HAKA :

⚫ BALA'O'I GUDA BIYAR TUN DAGA NAN DUNIYA :

1. Zubewar Imani (hadisi yace duk mai yin zina bashi da imani alokacin da yake aikatawa).

2. Zubewar Mutuncinsu (su kansu sun san cewa basu acikin lissafin mutanen kirki awajen Allah da bayin Allah).

3. Lalacewar Zuriyyarsu (Duk wanda yayi zina sai anyi da 'Yarsa ko 'Yar Uwarsa ko Qanwarsa).

4. MUMMUNAN TALAUCI : Zina tana haifar musu da mugun talauci. da kuma rashin albarkar duk abinda ya shigo hannunsu.

5. MUMMUNAR JINYA : Jinya acikin zuciyark
Su (bushewar zuciya), ko kuma ajikinsu (Qanjamau, Ciwon sanyi, da sauransu).


⚫ BALA'O'I GUDA BIYAR ACIKIN QABARINSU :

1. Rashin Kyawun Qarko, ko kuma rashin cikawa da Imani (idan ba suyi sa'a sun tuba ba).

2. Tsananin Matsi da duhun Qabari. (saboda rashin kulawarsu da ibada tun aduniya).

3. Rashin samun kyakyawar addu'a daga bayin Allah. (Allah ba zai sanya tausayinsu azukatan al'ummah ba, balle su tunasu, suyi musu addu'a).

4. Za'a nuna musu mummunan mazauninsu acikin Jahannama,  tare da sauran Mazinata.

5. Ci gaba da samun Qaruwar zunubai akansu saboda alhakin 'ya'yan mutane wadanda sukayi lalata dasu, suka gurbata musu rayuwa.


⚫ BALA'O'I GUDA BIYAR ARANAR ALQIYAMAH:

1. Za'a tashesu acikin Qungiyar Manyan Mazinata, akarkashin tutarsu. (SUBHANALLAH).

2. Mummunan ruwa mai Mugun doyi zai rika fita daga cikin al'aurorinsu.

3. Mummunan Hisabi da wulakantuwa agaban dukkan halittun Allah, Mala'iku zasuyi shelar cewa KUN GA WANNAN MAZINACI NE!! (KO KUMA KUN GA WANNAN MAZINACIYA CE!! ).

4. Za'a sanyasu acikin Kwazazzabon Jahannama,  kuma kunamai da macizai zasu rika cizonsu. Ga kuma tsananin bugu daga Mala'ikun Azaba.

5. Allah ba zai dubesu da rahamarsa ba..

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN!!!

ZAUREN FIQHU ya rairayo wannan ne daga ingantattun hadisai acikin Littafin AHWALUL QUBOOR na Ibnul Jawzee da Kuma KITABUL KABA'IR na Zahabiy.

Wannan tunatarwa ce. duk wanda yaga dama ya dauki hanyar tuba zuwa ga Ubangijinsa. Allah mai gafara ne, kuma mai karbar tuba ne.

DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990 (07-11-2014).
Share:

IDANUWAN MANZON ALLAH (SAWW) Zauren fiqhu

IDANUWAN MANZON ALLAH (SAWW)
**************************************
Wadannan idanuwa na Manzon Allah (saww), idanuwa ne wadanda darajarsu tafi duniya da lahira da abinda ke cikinsu. Kai har alahirar ma babu abinda ya fisu daraja.

Idanuwa ne wadanda basu ta'ba sa'ba ma Allah ba. Allah ya tsarkakesu ya girmamasu,  Har ma yana yabonsu acikin Alqur'ani mai girma yana cewa:

"MA ZAAGHAL-BASARU WAMA TAGHAA".

Idanuwa ne wadanda suka kalli abinda wani ido bai ta'ba gani ba. Allah Madaukakin Sarki ya shaidar da haka inda yake cewa :

"LAQAD RO'AA MIN AAYATI ROBBIHIL KUBRAA".

"HAKIKA YA GANI DAGA MANYAN AYOYIN UBANGIJINSA".

Kuma akwai hadisai da dama wadanda acikinsu Manzon Allah (saww) yake bamu labarin wasu daga cikin abubuwan da ya gani da wannan idanuwan, wadanda babu wani mahalukin da ya ta'ba gani in banda SHI (SAWW).

SIFFAR IDANUNSA DA GASHIN GIRARSA(SAWW) :
**************************
MASU SIFFANTA SHI (SAWW) irinsu Ameerul-Mu'umineen Sayyiduna Aliy bn Aby Talib, Sayyiduna Abu Huraira, Sayyiduna Hind bn Aby Haala, Sayyidah Ummu Ma'abad Al-Khuza'iyyah (Allah ya kara musu yarda) Sunce:

"MANZON ALLAH (saww) yana da Mayalwatan Idanuwa masu tsananin kyawu. Wajen Farin, Fari Qal yake. Hakanan Qwayar idanunsa baki-Qirin take.

Sannan akwai ratsin-Jaa acikin kwayar idanun. Wanda hakan yana daga alamomin cikar Annabtarsa kamar yadda Annabawan Farko suka gayawa al'ummominsu.

Hafiz Al-Iraaqee ya ruwaito cewa Lokacin da Manzon Allah (saww) Ya hadu da Raahib dinnan alokacin da suka je fatauci tare da Maisara (bawan Nana Khadeeja ra) acikin garin Basra, Farkon shaidar da Raahib din ya fara dubawa ajikin Manzon Allah (saww) ita ce Wannan RATSIN JA na cikin idanunsa.

Daga gani sai ya tabbatar cewa WANNAN SHINE ANNABIN QARSHE (SAWW).

(aduba Sharhin Shama'il na Imamul-Manawy juzu'i na 1, shafi na 55).

Sannan yana da Mayalwacin gashin idanu. Gashin baqi ne, ko yaushe haka zaka ganshi kamar yasa tozali.
Na saman ya Tankwara izuwa sama, sannan na kasan shi kuwa ya tintsira Izuwa Qasa.

Yana da cikakken Gashin girarsa mai kyawu ga Tsawo, kuma ya lankwashe kamar baka.

saboda kwarjininsa da kyawunsa Zaka ga girarsa ta dama data haggu kamar sun hade, amma basu hadu ba. Karan Hancinsa ya dan raba tsakaninsu.

(haka Ibnul Atheer ya fada acikin Nihaya, da kuma Sheikh Yusufun-Nabahany acikin Wasa'ilul-Wusul, Shafi na 73, da kuma Mulla Aliyul-Qary acikin JAM'UL-WASA'IL Juzu'i na 1 shafi na 44.).

YA ALLAH KA QARA MANA SOYAYYAR NAJAMUL-HUDA (SAWW).

Idan an ta'ba Allah yakan yi fushi (saww) sai kaga wata jijiya ta fito atsakanin girarsa (saww).

TOZALINSA MAI ALBARKA (SAWW)
************************************
Sanya tozali yana daga cikin Sunnoninsa (saww). Domin ko sanda aka haife shi (saww), yazo Idanunsa radau da tozali.

Sayyiduna Abdullahi bn  Abbas ya ruwaito cewar Manzon Allah (saww) ya kasance yana shafa tozalin Ithmud acikin Idanunsa kullum da daddare kafin ya kwanta, Sau Uku a idon dama sannan sau uku a idon haggu.

Har ma yana cewa "Kuyi tozali da Ithmud. Domin yana Qara Qarfin idanu, kuma yana tsirar da gashi".

(aduba Sunanut-Tirmidhy, Hadisi na 1757, da Kuma Mustadrak na Imamul-Hakim Hadisi na 8249).

QARFIN IDANUNSA (SAWW)
****************************
MANZON ALLAH (AS) Ya kasance yana gani acikin duhu kamar yadda yake gani acikin haske. Sannan yana ganin abinda ke nesa kamar yadda yake ganin na Kusa.

Idan ya kalli gabas yana iya ganin Mahudar rana, hakanan idan ya kalli yamma yana iya ganin mafadar rana.Kuma Yana iya shaida matafiyin dake nesa tun kafin afara ganin Qurarsa.

An ruwaito cewar Manzon Allah (saww) yana iya Qirga taurari 11 acikin Taurarin nan mafiya nisa na Surayyah.

Mala'ika Jibreelu yakan nado masa Doron Qasar nan gaba dayanta ya, ajiye masa agabansa ya kalli kowanne sashe.

In banda SHI (SAWW) babu wani Annabin da ya ta'ba ganin Mala'ika JIBREELU (AS) abisa Surar da Allah ya halicce shi da ita. Kuma da wannan idanuwan ya kalleshi.

Wannan Idanun nasa masu albarka, dasu ne yaje yaga Aljannah da ni'imomin da suke cikinta, Sannan yaga wuta da Ukubobin da suke cikinta.

Wadannan idanun na Manzon Allah (saww) dasu ne yayi kallo izuwa AJA'IBU (ABUBUWAN MAMAKI) NA MALAKUTUN UBANGIJINSA acikin daren da akayi Isra'i da Mi'iraji dashi (saww).

Yaga dukkan Annabawan Allah (as). Yaga Al'arshu da Kursiyyu da Lauhu da Qalamu da Haudhu da Raf-rafu. Kuma yaga Kogunan haske, Sannan ya ratsa Miliyoyin hijabai duk da wannan idanun.

Yaga Baitul-Ma'amur yaga Mala'iku nau'i-nau'i. Yaga Raf-Rafu da Farshu, har sanda yaga UBANGIJINSA (SWT) alokacin da sukayi Munajati awajen da Ubangijin nasa yaso.

Akwai sa'bani atsakanin Malaman Farko har zuwa yanzu game da maganar Shin Annabi (saww) yaga Allah ne ko bai ganshi ba?.

Nana A'ishah (ra) tace bai ganshi ba. Amma Sayyiduna Abdullahi bn Abbas (Malamin al'ummah) yayin da aka tambayeshi yace : "YA GANSHI! YA GANSHI! YA GANSHI! YA GANSHI! (Yayi ta maimaitawa har sai da ya shiɗe).

Anan zan Tsaya sai mun hadu acikin wani darasin da zamu gabatar a Zauren Fiqhu Whatsapp in sha Allah.

YA Allah kara salati da sallama marasa iyaka abisa Zababben Zababbu (saww).

DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990 (Asalin rubutun na yishi ne aranar 09/APRIL/2013).
Share:

Zuciya tafarkin tsira:Akwai Ma'ajiyar alkhairi, sannan kuma akwai Ma'ajiyar sharri.

*ZUCIYA TAFARKIN TSIRA*
**************************
```Zuciya wata ajiyar Allah ce dake cikin jikinka wacce acikinta akayi maka Ma'ajiya guda biyu. Akwai Ma'ajiyar alkhairi, sannan kuma akwai Ma'ajiyar sharri.

Zuciya ita ce tsoka guda 'daya tal wacce lalacewarta yakan janyo maka asarar da babu fanshewa.. Kuma gyaruwarta da nagartarta zai iya janyo maka cin ribar da babu fa'duwa bayanta.

Zuciya ita ce Muhallin da Allah ke kallo acikin jikinka.. Mai yasa ba zaka gyarata ba, kamar irin yadda kake yiwa jikinka kwalliya da gyara kafin ka shiga cikin jama'a?.

Zuciya ita ce Kadara mafi tsada, Mafi daraja, mafi Soyuwa wacce zaka mallaka amatsayinka na Mumini. Idan ka mallaki Zuciyarka ka gama samun dukkan arziki.

Zuciya ita ce Hanyar tafiyarka zuwa ga Allah, Kuma kyawawan ayyukanka sune Motoci da jiragen da zaka hau kayi tafiyar.. Idan hanyarka ta zaka kyakkyawa,to lallai tafiyarka zatayi sauki koda abin hawan naka Qankani ne. Amma idan hanyarka tayi muni, to tafiyarka ba zatayi kyawu ba, koda abin hawan naka mai girma ne.

Tafiya zuwa ga Allah ba da Qafa akeyi ba.. Ana yinta ne da zuciya. Yi kokari ka tsaftace zuciyarka domin samun tafiya mai nisa, mai tsafta, mai sauri..```

_Allah Madaukakin Sarki yace :_

*"RANAR DA DUKIYA KO 'YA'YA BA ZASUYI AMFANI BA. SAI DAI WANDA YAZO MA ALLAH DA LAFIYAYYAR ZUCIYA".*

_Ya Allah! Ya mai juya zukata!! Ka tabbatar da zukatanmu akan addininka._

*DAGA ZAUREN FIQHU (17-02-1439 06-11-2017).*


Share:

Sunday 12 November 2017

Audio:-Huduba:Lokacin sanyi da hukunce-hukuncen sa??

*HUDUBA HUDUBA :

Mai taken:-

LOKACIN SANYI DA HUKUNCE-HUKUNCEN SHI

Daga:-

IMAM:
*MALAM ANAS ASSALAFY FAGGE*

(DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA)

DOWNLOAD AUDIO NOW


DAGA MASALLACIN JUMA'A NA :
*ABUBAKAR SIDDIQ* DAKE DAN TAMASHE, ZANGO

20/SAFAR/1439 A. H = 10/11/2017

*JIBWIS NIGERIA*

Gadukkan mai son shiga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH* sai ya yi saving wanan number +2348122248585 sannan ya tura da sunanshi da adireshinsa ta what's App. Duk abun da mutum ya turo matukar ba suna ba ne ba za a kula shi ba


Share:

Thursday 9 November 2017

KUBUTAR MAHAIFA BA SHI NE MANUFAR IDDA BA ! ! | DR JAMILU YUSUF ZAREWA

*KUBUTAR MAHAIFA BA SHI NE MANUFAR IDDA BA ! !*

*Tambaya*

Assalamu alaikum mal dan Allah ga tambaya nan
Nice nai aure na ya rabu da mijina, wato ya bani takardan saki, kafin ya bani wannan takardar,mun samu matsala na bar gidanshi tsawon shekara daya da wata tara,kuma Daman tsawon zaman mu tare shekara bakwai ban taba samun ciki ba,yaya iddata zata kasance ?

*Amsa*
Wa alaikum assalam, Za ta jira tsarki uku, tun da sun taba kawanciyar aure kamar yadda aya ta 228 a Suratul Bakara  ta tabbatar da hakan.
                                                               Hukunce-hukuncen Saki suna farawa ne daga lokacin da aka yi saki, ba daga sanda aka samu hatsaniya ba.                          Allah ya shar'anta idda saboda manufofi da yawa daga ciki akwai: bawa miji damar kome Idan saki daya ne ko biyu, ta yiwu wani daga cikin ma'aurata ya yi nadama, Tare da cewa babban makasudin shi ne tabbatar da kubutar mahaifa, Amma ba shi kadai ba ne.
Allah ne mafi sani

*Amsawa*
*DR Jamilu Yusuf Zarewa*
25/11/2016
Share:

Archive

Unordered List

Support