January 2018 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Thursday 11 January 2018

Labari mai girgiza zuciya - Zauren fiqhu

LABARI MAI GIRGIZA ZUCIYA
*******************************
Abdullahi bn Almubarak (rah) yana daga cikin magabata na kwarai, kuma mutum ne Salihi.
Wata shekara bayan yayi niyyar tafiya aikin Hajji, sai ya fita domin yin ban-kwana da abokansa (Almajiransa) kafin tafiyarsa. Amma akan hanyar ne yaga wani abu wanda ya tada masa hankali ya firgitashi.
Ya hangi wata baiwar Allah tana tone juji (bola) tana tonowa wani MUSHEN KAZA wacce aka jefar. Ta daukota ta sanya a Qasan hammatarta, ta juya ta tafi aboye acikin duhu.
Sai yayi kiranta yace "Mai kikieyi ya ke baiwar Allah?!". Sai tace "Ya kai bawan Allah,  kyale halittu da mahaliccinsu. Domin Allah yana da sha'ani acikin lamarin halittunsa".
Sai Ibnul Mubarak yace mata "Ina yi miki magiya don girman Allah ki gaya min labarinki".
Sai matar tace masa "Amma wallahi ba don ka riga kayi mun magiya ba, da ban gaya maka halin da nake ciki ba".
Kafin ta fara gaya masa har hawaye ya fara zuba daga idanunta. Sai tace "Hakika mu Allah ya halatta mana cin mushe. Domin ni Bazawara ce Matalauciya. Kuma (ni) mahaifiyar 'ya'ya mata ne guda hudu".
"Mutuwa ta dauke Mahaifinsu mai kula dasu, Yanayi ya tsananta garemu, kuma dukiya ta Qare daga gareni. Kuma na kwankwasa kofofin mutane (wato na bibbi gidajen jama'a) amma ban samu wata zuciya mai tausayi daga wajensu ba".
"Sai na fita domin nemowa abinci ga 'Ya'yana wadanda wutar yunwa ta riga ta Qone musu hanta. Sai Allah ya azurtani da samun wannan mushen kazar da kake gani. Shin zakayi jayayya dani ne akanta?".
Daga jin wannan labari nan take sai Idanuwan Ibnul Mubarak suka rika zubda hawaye. Sai yace mata "Karbi wannan amanar".
Sai ya damka mata dukkan dunkiyar da yayi niyyar tafiya aikin hajjin nan da ita.
Sai Uwar marayun nan ta karba ta juya wajen 'ya'yanta tana godiya. Shi kuwa Ibnul Mubarak ya juya zuwa gidansa. Alhazai na garinsu kuma suka tafi suka sauke faralinsu sannan suka dawo.
Amma abin mamakin duk da cewar shi bai je aikin Hajji ba, amma duk Alhazan sun dawo suna yin godiya gareshi bisa hidimar da yayi  musu awajen aikin Hajji.
Suan cewa "Allah yaji Qanka Ya Kai Ibnul Mubarak! Babu wani wajen zama da muka zauna fache sai ka bamu wani abu daga ilimin da Allah ya sanar dakai. Kuma bamu ga wanda ya fika wajen bautarka ga Allah Ubangijinka ba, awajen aikin Hajjin nan na wannan shekarar".
Sai Ibnul Mubarak yayi mamaki kuma hankalinsa ya tashi game da al'amarinsa, da kuma al'amarinsu. Shi dai bai bar garinsa ba (ballantana ace har an ganshi awajen aikin Hajji). Kuma shi ba yaso ya bayyanar musu da sirrinsa. (wato ba yaso ya gaya musu cewar yayi sadaqah ne da kudinsa).
To da ya kwanta barci sai yaga wani kyakkyawan mutum wanda haske ke fita daga fuskarsa. Yana ce masa "AMINCIN ALLAH YA TABBATA AGAREKA YA KAI ABDULLAHI. SHIN BAKA SAN KO NI WANENE BA? AI NINE MASOYIN NAN NAKA MUHAMMADUR RASULULLAHI (SAWW) NINE MASOYINKA ADUNIYA DA LAHIRA, KUMA NINE MAI CETONKA ARANAR LAHIRA. ALLAH YA SAKA MAKA DA ALKHAIRI BISA ABINDA KAYI MA AL'UMMATA".
"YA KAI ABDULLAHI 'DAN MUBARAK! HAKIKA ALLAH YA GIRMAMAKA (YAYI MAKA KARAMCI) KAMAR YADDA KA GIRMAMA MAHAIFIYAR MARAYUN NAN. KUMA ALLAH YA RUFA MAKA ASIRI KAMAR YADDA KA RUFA ASIRIN MARAYUN NAN".
"HAKIKA ALLAH MADAUKAKIN SARKI YA HALICCI WANI MALA'IKA NE DA SIFFARKA. YA KASANCE YANA TAFIYA TARE DA ALHAZAN GARINKU AWAJEN GUDANAR DA AYYUKAN HAJJI".
"KUMA HAKIKA ALLAH YA BAMA KOWANNE ALHAJI LADAN AIKIN HAJJI GUDA 'DAYA NE. AMMA KAI KUMA ALLAH YA RUBUTA MAKA LADAN AIKIN HAJJI GUDA SABA'IN!!".
Allahu Akbar!! Ya jama'a kunji fa!!!. Ya ku masu alfahari da yawan aikin Hajji!! (Nayi arfa sau kaza! Naje Umrah sau kaza!! Nayi dawafi sau kaza!!).
In dai yardar Allah kuke nema, ku zagaya gidajen Marayu da Miskinai da Fakirai mana! Zaku samu yardar Allah anan!!
Ka kwashi Matanka da Qananan 'ya'yanka ka tafi dasu Umrah alhali Makwabcinka ko limamin masallacin Unguwarku, ko 'yan uwanka suna kwana da yunwa.. (Wallahi ba lallai ne Allah ya karbi Umrar taku ba).
Wallahi ladan ciyar da Mayunwata guda goma yafi ladan zuwa Umrarka. Wasu daga cikin magabata suna cewa :
"Loma guda daya wacce aka sanya acikin cikin Mayunwaci, tafi alkhairi fiye da gina masallatan juma'a guda dubu".
Ka bar Makobcinka ko 'dan uwanka acikin yunwa da talauci, amma kaje kana LABBAIKAL LAHUMMA LABBAIKA". (Kai kanka kasan Allah ba zai amshi gaisuwarka ba).
Wannan Qissar tana nan acikin Sifatus Safwah na Ibnul Jawzee.
DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990 (10-01-2017).
In sha Allahu daga nan kafin kamawar watan Ramadhan Zauren Fiqhu zai kafa wani bangare mai suna GIDAUNIYAR MARAYU wacce in sha Allahu zamu tara wani abu atsakaninmu domin ciyar da marayu da Miskinai alokacin Azumi. Sannan da kulawa da majinyata marassa galiho. In sha Allahu.
Allah shi taimakemu ameeen.
Share:

Fa'idodin sadaqah - Zauren fiqhu


FA'IDODIN SADAQAH [DAGA ZAUREN FIQHU]
*********************************************
Ya kai 'Dan uwa Musulmi!! Ya ke 'Yar uwa Musulma!! Shin ko kun san cewa sadaqah tana da Mutukar amfani arayuwar 'Dan Adam?
Bari kuji wasu daga cikin fa'idodin dake cikinta :
1. Sadaqah wata Qofa ce daga kofofin samun shiga Aljannah.
2. Acikin dukkan ayyukan lada, Sadaqah tana daga sahun gaba. Kuma mafificiyar sadaqah ita ce "Ciyar da abinci domin Allah".
3. Sadaqah tana inuwantar da Ma'abotanta aranar Alqiyamah, Kuma tana 'Yantar dashi daga shiga Wuta. (Gwargwadon yawan sadaqarka, shine gwargwadon ni'imar da zaka shiga aranar Alqiyamah).
4. Sadaqah tana bushe fushin Ubangiji. (Allah yana son masu yinta, don haka ba zai yi fushi da kai ba).
5. Sadaqah tana kiyaye mutum daga Azabar Qabari.
6. Sadaqah ita ce mafificiyar kyautar da zakayi ma Mamacinka.
7. Sadaqah, Ubangiji ne ke rainonta har sai ranar Alqiyamah za'a nuna maka ladanta.
8. Sadaqah tana tsarkake zuciya daga Qazantar nan ta rowa da kyashi.
9. Sadaqah tana janyo maka soyayyar Allah da soyayyar Mala'ikunsa da Soyayyar bayin Allah.
10. Sadaqah tana janyo maka ninninkuwar ladan ayyukanka.
11. Sadaqah tana janyo maka hasken fuska aranar Alqiyamah.
12. Sadaqah tana janyo maka farin ciki anan duniya da kuma lahira.
13. Sadaqah tana zama dalilin yayewar damuwarka. Kuma tana kiyayeka daga bakin ciki akan abinda ya wuce.
14. Sadaqah tana kiyayeka daga Firgita aranar Alqiyamah.
15. Sadaqah tana janyo kankarewar zunubanka, da kuma gafarar laifukanka.
16. Sadaqah tana janyo ma masu yinta su samu kyakywar cikawa da imani aranar Mutuwarsu.
17. Sadaqah tana sanya Mala'ikun Allah su rika yi maka addu'ar alkhairi.
18. Masu yin sadaqah suna daga cikin mafifitan mutane awajen Allah.
19. Sadaqah tana sanya albarka acikin dukiyarka. Sannan ta tsare dukiyarka daga kowacce irin asara.
20. Sadaqah tana da albarka. Kuma da wanda ya fitar, da wanda aka wakilta ya bayar, da wanda ya mika, da wanda ya rarraba duk suna cikin ladanta.
21. Ma'abocin yawaita sadaqah, yana da alkawarin samun lada mai yawa tare da babban sakamako awajen Ubangijinsa.
22. Yana daga cikin siffofin masu tsoron Allah, zaka iske suna ciyar da dukiyarsu domin Allah,
23. Sadaqah tana daga cikin manyan alamomin Kyauta da karamci.
24. Sadaqah babbar dalili ce wajen samun karbuwar addu'o'inka, da yayewar bakin cikinka.
25. Sadaqah tana kiyaye masu yinta daga afkawa cikin bala'i.
26. Sadaqah sau daya (in dai an yita domin Allah) tana toshewa kofofi saba'in na Musibu da miyagun abubuwa tun anan duniya.
27. Sadaqah tana Qara maka tsawon rai da albarkar rayuwa da albarkar dukiya.
28. Sadaqah tana janyo maka samun nasara tare da taimakon Ubangiji acikin dukkan abinda kasa agabanka.
29. Sadaqah tana sanyawa ka samu gagarumar nasara akan Maqiyanka da mahassadanka. Kuma kaidinsu ba zai cuceka ba.
30. Idan wani ciwo yana damunka har ka rasa maganinsa, to yawaita sadaqah. In sha Allah ita Sadaqah magani ce, waraka ce, kuma kariya ce daga dukkan cututtuka.
31. Sadaqah garkuwa ce daga sharrin 'barayi, ko gobara, kuma tana kiyaye masu yinta daga mummunar cikawa.
32. Sadaqah ladanta yana tabbatuwa awajen Allah. Koda dabbobi kayi wa sadaqar, ko tsuntsaye, ko Qwaruka.
33. Babbar sadaqar da zaka fara gabatarwa ayanzu, ita ce kayi "sharing" (wato ya'da) wannan rubutun daga Zauren Fiqhu ba tare da goge koda harafi guda daga ciki ba.
Idan kayi haka da niyyar sadaqah, to duk wanda ya gani ya karanta kaima kana da lada akansa.
An gabatar da karatun ne a ZAUREN FIQHU WHATSAPP (31-12-2016).
Share:

Dausayin iyali 002 - Dr.Mansur Ibrahim Sokoto


*DAUSAYIN IYALI 002*
Matsayin Mata da Hakkokinsu a Musulunci
Littafin *Dr. Mansur Sokoto*
Matsayin Mata Kafin Zuwan Musulunci
Abu ne da tarihi ya tabbatar cewa, Macce ba a dauke ta a matsayin
kammalallen dan Adam ba kafin zuwan Musulunci. Domin kuwa an
mayar da ita kamar Haja wacce ake saye kuma ake sayarwa, ake kuma
gadon ta kamar yadda ake gadon gida ko gona ko duk wata kaddara
da Namiji ya mutu ya bar ta. Akan umurci Macce ta yi Zina don ta kawo
kudi, kuma ana aurar da ita ne yadda aka ga dama, ba tare da neman
zabinta ko ma shawartar ta ba.
A da Namiji yakan auri ko Mata nawa yake so kuma ya ga dama kamar
yadda yake iya mallakar riga da hula ko nawa yake so.
A wasu sassan duniya ba a yarda Macce mutum ce ba ma sam. Misali,
a qasar Rasha Malaman addini sun ba da fatawar cewa, Macce najasa
ce, matsayinta daya ne da na Kare.
A yankin Larabawa, zamanin Jahiliyya, uba yakan sayar da diyarsa.
Yakan kuma rufe ta cikin qasa babu gaira babu dalili. Kawai dai
haifuwar ta ba abin farin ciki ba ne balle ai alfahari. Budurwa tana goge
gumi daga fuskar babanta a lokacin da yake haqa ramin rufe ta, amma
ita ba ta sani ba.
Kashe Macce - kafin zuwan Musulunci - ba wani babban laifi ba ne da
har za ayi maganar Qisasi ko Diyya a kan sa.
A qasar Indiya akan qone Macce ne tare da mijinta idan ya mutu,
alhalin tana da ranta da lafiyarta. Wannan ya sa sau da yawa Macce
takan kashe kanta bayan mutuwar mijinta irin mutuwar da take ganin
ta fi mata sauqi, don kauce ma wannan baqar mutuwa da mummunan
bala'i.
Malaman addinai biyu da ake a da su a lokacin wadan da suka samo
koyarwarsu daga manyan Annabawa ba su tabuka komai a kan wannan
- Yahudawa - mabiyan Addinin Annabi Musa Alaihis Salam sun dauki
Macce a matsayin najasa duk lokacin da take Haila. Ba za su ci abincin
da ta dafa ba, ba kuma za su kusance ta ba. A maimakon haka sai su
kafa ma ta rumfa a bayan gida - kamar yadda ake turke Akuya - su riqa
ba ta ruwa da gurasa har sai lokacin da ta gama al'ada sannan ta dawo
cikin gida.
- Su kuma Kiristoci duk da ba su nuna qyamar ta a wannan lokaci.
Kuma ma har saduwa suke yi da ita a lokacin da take Haila. Amma ba
za mu dauka cewa sun mutunta ta ba tun da yake suna kallon ta a
matsayin ita ce ummul-haba'isin duk wani laifi da sharri da cuta da ake
yi a duniya. Kuma wai, ita ce qofar shiga wuta. Suna kafa hujja da
cewa, wai, ita ce ta bai wa Annabi Adam (Alaihis Salam) shawarar cin
bishiyar da Allah ya hana shi har ta jawo ma su uqubar fita daga gidan
aljanna.
*Kusaurari cigaba da izinin Allah*
Gabatarwa a social Media
*Ibrahim Nasidi Baban Ilham*
Share:

Dausayin iyali 004 - Dr.Mansur Ibrahim Sokoto



*DAUSAYIN IYALI 004*
Matsayin Mata da Hakkokinsu a Musulinci
Littafin *Dr. Mansur Sokoto*
Kai, wace daraja muke nema ma Macce bayan abinda kowa ya sani a
tarihi ne, Macce guda daya ce ta yi sa’ayi tsakanin Safa da Marwa tana
nemar ma danta ruwan sha, amma Shari’ar Musulunci ta mayar da
wannan sa’ayin nata a matsayin wani rukuni daga cikin rukunan
Musulunci shi ne aikin Hajji? Tare da haka aka yafe wa Mata yin
Sa’ayin, aka ce Maza kawai za su yi. Kamar yadda aka yafe ma wani
mutum zuwa Jihadi saboda ya raka matarsa wurin aikin Hajji. Sahih Al￾Bukhari (3006) da Sahih Muslim (1344).
Kula da iyali, da ciyar da su abinci, yana da wani gurbi na musamman
wanda ya zarce na sauran wasu ayyuka na neman lada da neman
shiga aljanna. Ban da wannan ma, kasancewa tare da su, da faranta
ransu ta hanyar rashin yin nisa da su, shi ma abu ne mai girman lada.
Mu dubi girman ladar kasancewa a birnin Makka da yin salloli masu
ninkin daraja da lada a cikin ta, amma duk da haka Annabi Sallallahu
Alaihi wa Sallam yake cewa: “Idan dayanku ya kammala aikin Hajjinsa,
to ya gaggauta komawa gida wajen iyalansa. Domin wannan ya fi
girman lada a gare shi”. Sahih al-Jami’ (732)
*Kusaurari cigaba da izinin Allah*
Gabatarwa a social media
*Ibrahim Nasidi Baban Ilham*.
Share:

Dausayin iyali 003 - Dr.mansur ibrahim sokoto


*DAUSAYIN IYALI 003*
Matsayin Mata da Hakkokinsu a Musulunci
Littafin *Dr. Mansur Sokoto*
*Macce 'Yar Gatan Musulunci*
Addinin Musulunci shi ne ya qwato ma Macce dukkan haqqoqinta, ya
hana a zalunce ta, ya tabbatar mata da mutuntaka da daraja, ya sanya
mata rabo a cikin gado, ya ce duk aikin lada idan ta yi shi tana da lada
kamar Namiji.
Har a mintunansa na qarshe a duniya, Manzon Allah Sallallahu Alaihi
wa Sallam ya kasance yana wasici ga al'ummarsa da su kula da
haqqen Mata. Yana cewa:

""استوصو"ا بالنساء خيرا"
“Ina umurnin ku da ku kyautata kula da mata”. Sahih Al-Bukhari
(5185).
A musulunci, da zaran ka haifi 'ya Macce to ka samu wani babban
dalilin shiga aljanna. To ballai kuma wanda ya samu biyu.
Hadisi ya zo a cikin Sahih Al-Bukhari daga uwar Mummunai A’isha
Radhiyallahu Anha tana ba da labarin wata baquwa da ta zo bara a
gidanta tana neman abin da za ta jefa a bakin salati. Tare da ita akwai
yara tagwaye guda biyu. Sai ta dauko dabino qwara daya ta ba ta. Sai
matar ta raba dabinon biyu ta ba ‘yan tagwayenta. Wannan abin ya ba
ni sha’awa, har na fada ma Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam. In
ji ta. Sai ya ce,”Ai duk wanda Allah ya jarabce shi da ‘ya’ya mata ko
kadan ne kuma ya kyautata ma su, za su zamo ma sa kariya daga
shiga wuta”. Sahih Al-Bukhari (1418) da Sahih Muslim (2629).
A daya Hadisin na cikin Sahihu Muslim daga Anas Radhiyallahu Anhu
Annabi Sallallahu Alaihi wa Sallam cewa ya yi: “Wanda ya kula da
‘ya’ya mata biyu har suka balaga zai zo a ranar Alqiyama muna tare
da shi kamar haka”. Sai ya gwama yatsunsa wuri daya.
Wannan a matakin farko na haifuwar Macce da rainon ta kenan. Idan ta
girma aka yi ma ta aure Musulunci ya ce, ita ce ta kammala rabin addinin mijinta. Idan kuwa ta haifu sai aka ce aljannar ‘ya’yanta na
qarqashin qafafunta. A nan ba ina nuni ne da Hadisin da aka sani sosai
ba, shi ne: “Aljanna tana qarqashin qafafun iyaye Mata”.
Wannan Hadisi da'ifi ne, kuma ma babu shi a littafan Hadisi sai dai na
Tarihi irin su "Al-Kamil" na Ibnu Adiy, da na Uqaili. Amma akwai Hadisin
Mu'awiya bn Jaahimata wanda Imam An-Nasa'i da Hakim suka ruwaito
cewa, wani mutum ya zo wurin Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa
Sallam yana neman izininsa don ya tafi Jihadi. Sai Annabi Sallallahu
Alaihi wa Sallam ya tambaye shi, ko mahaifiyarka tana raye? Ya amsa
ma sa, eh. Sai ya ce:
"To, ka lizimce ta. Domin Aljanna na qarqashin qafafunta".
Wannan kam ingantaccen Hadisi ne babu tantama. Imam Nasa’i (2/54)
da Hakim (4/151) da dabarani (1/225) duk sun fitar da shi. Kuma
Hakim da Dhahabi da Mundhiri (3/214) duk sun inganta shi. A
ma’anarsa kuma ba shi da banbanci da wancan.
Hadisin da ya fi wannan inganci shi ne wanda ya ce, uwa Macce tana
da haqqoqi uku, a lokacin da uba Namiji yake da haqqi guda daya. Ga
yadda Hadisinyake: Wani mutum ya zo wurin Manzon Allah Sallallahu
Alaihi wa Sallam sai ya tambaye shi, wa ya fi dacewa a duniya in
kyautata ma? Sallallahu Alaihi wa Sallam ya ce,”Mahaifiyarka”. Ya ce,
sai kuma wa ye? Ya ce,”Mahaifiyarka”. Ya sake tambaya, sannan wa?
Ya ce, ”Mahaifiyarka”. Sai kuma wa? Sallallahu Alaihi wa Sallam ya ce,
“Sannan Mahaifinka”. Sahih Al-Bukhari (5626).
Kai, wace daraja muke nema ma Macce bayan abinda kowa ya sani a
tarihi ne, Macce guda daya ce ta yi sa’ayi tsakanin Safa da Marwa tana
nemar ma danta ruwan sha, amma Shari’ar Musulunci ta mayar da
wannan sa’ayin nata a matsayin wani rukuni daga cikin rukunan
Musulunci shi ne aikin Hajji? Tare da haka aka yafe wa Mata yin
Sa’ayin, aka ce Maza kawai za su yi. Kamar yadda aka yafe ma wani
mutum zuwa Jihadi saboda ya raka matarsa wurin aikin Hajji. Sahih Al￾Bukhari (3006) da Sahih Muslim (1344).
*Kusaurari cigaba da izinin Allah*
Gabatarwa a social media
*Ibrahim Nasidi Baban Ilham*
Share:

Monday 8 January 2018

Alkaki da Ruwan Zuma - Dr.mansur ibrahim sokoto



ALKAKI DA RUWAN ZUMA

Fitowa ta 001

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinqai
Godiya ta tabbata ga Allah. Tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta.
Gabatarwa
Da yawa daga cikin mutane suna tsammanin malaman Sunna da suka ce
a kame baki daga kutsawa a cikin rikittan da suka faru a tsakanin iyayenmu
Musulmin farko sun faxi haka ne don suna son a voye gaskiya. Wannan kuwa
kuskure ne babba.
Tarihin magabata, musamman ma dai almajiran Manzon Allah Sallallahu
Alaihi wa Sallam na da banbanci da sauran tarihin mutane baki xaya. Dalili kuwa
shi ne, ba zaka iya raba tarihinsu ba da na maigidansu wanda shi ne Allah ya
xora ma alhakin tarbiyyar su da shiryar da su zuwa ga gaskiya.
Dalili na biyu kuma shi ne kasancewar su mutanen da Allah ya zava kuma
ya fifita su albarkacin zamowar su tare da amintaccen Allah; masu ba shi
shawara, masu taimakon sa, masu bin sa sallah, masu ba shi zakka, masu
tanyon sa jihadi, masu ba shi aure, masu maqwautaka da shi, kuma waxanda
tarihi ya tabbatar sun fifita shi a kan kowa da kowa. Kai, har ma sun kashe
iyayensu da danginsu a wajen kariyar sa. Haka ma duk abin da suka mallaka na
duniya sun sadaukar da shi domin wannan farin masoyi da basu tava haxa kowa
da shi ba.
Wannan magana ba na-ji-na-ji ba ce, maganar Allah ce. Mutum har ya kan
yi mamakin irin yadda wannan lamari zai shige ma wasu duhu alhalin ga shi nan
varo varo a wurare cikin Alqur'ani da ba su qirguwa.
Sahabbai mutane ne kamar kowa ta fuskar cewa suna iya yin kuskure ko
laifi. Amma banbancinsu da sauran mutane shi ne, suna da tsarkin zuciya da
shaidar Alqur'ani. Ba ni zaton wannan magana ta buqaci a kafa mata hujja, sai fa ga wanda ba shi da wata masaniya sam sam game da Alqur'ani. Don haka idan
sun yi kuskure to, sun samu yafewar Allah da tabbacin su yardaddu ne, 'yan
aljanna.1
 Wannan shi ne dalilin da ya sa malaman Sunna suka fifita kame baki
daga faxin abin da ya gudana a tsakanin Sahabbai domin bakin rijiya ba wurin
wasar makaho ne ba. Wanda kuwa duk ya shagaltu da neman kurakuransu da
ayubbansu zai wayi gari yana raina su ko ya qyamace su alhalin Allah ya umurce
shi da darajanta su da qaunar su da yi ma su addu'a. Ka ga a nan shi ne ya faxa
ruwa. Daga cikin abin da ke nuna mana cewa, ba wai nufin malamai shi ne a
voye gaskiya ba, zamu ga ai duk tarihin nan da suka ce mu kame baki daga ce-
ce-ku-ce a kan sa su suka rubuta shi, ba su voye komai daga cikinsa ba,
sawa'un mai daxi da maras daxi, na gaskiya da na qarya. Sun hikaito mana ko
wanne a matsayin ruwaya da aka faxa kuma sun kawo wanda ya faxe ta.
Dalili na uku da ya sanya malaman Sunna sukar wannan matsayi shi ne
la'akari da suka yi da yadda tarihi ya gauraya da ra'ayoyi da son zuciya na
Daikaiku da na qungiyoyi wadanda ba su jin ciwon fesa qarya don cimma wata
manufa, ko aibanta wani ko gwarzanta shi. Ga shi kuma tarihi bai samu irin
hidimar da Hadisin Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam ya samu ba na
cikakkiyar kulawa da tantancewa tare da banbanta ingantacce daga wanda ba
shi ba.
Bugu da qari kuma sai marubuta iri iri suka bayyana kowa da irin fassarar
da yake yi ma abin da ya auku. A dalilin haka, sai aka yi ta yi ma wasu riwayoyi
gyaran fuska, wasu aka sauya su, aka karkata alhairansu suka koma sharri,
wasu kuma aka qara masu matsayi suka kai inda ba su cancanta ba.

Duba alal misali: Suratul Hashri: 8-10 da Suratul Fathi: 18 da Suratul Mujadala: 22 da
Suratut Taubah: 100.

Littafin: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

Mu gamu a darasi na 2

25/4/1439
15/12/2017​

» Zauren Minbarin Malamai+2347037477743
Share:

Thursday 4 January 2018

Shi'a: Kura da fatar Akuya 01 - Mal.Umar shehu zaria


*SHI'A: KURA DA FATAR AKUYA*

FITOWA TA 1

Imamu Malik Bn Anas, Rahimahullah, ya ce:

*_"Su wadannan mutane - 'Yan Shi'a - wasu mutane ne da suka yi nufin su ci mutuncin Manzon Allah, sallallahu' alaihi wa sallama, amma sai suka ga haka ba zai yiwu ba kai tsaye wannan ya sanya sai suke cin mutuncin Sahabbai don a ce Manzon Allah ba mutumin kirki ba ne, kuma don mutane su ce ai inda mutumin kirki ne da SahabbanSa ma sun zama mutanen kirki"_*. A duba al-Saarimul Masluul na Sheikhul Islam Ibn Taimiyyah shafi na 580.

Don haka, duk mai neman gamawa da duniya lafiya, to ya nisanci addinin Shi'a.

✍🏼Dan uwanku a Musulunci:
*_Mal Umar Shehu Zaria_*
03/01/2018.

Daga: *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*

Keep stay with us more updates is coming..... 
Share:

Archive

Unordered List

Support