May 2018 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Sunday 20 May 2018

Hikimomin da Azumi ya kunsa....Dr.jamilu yusuf zarewa

*HIKIMOMIN DA AZUMI YA KUNSA*

*Tambaya:*

Assalamu alaikum Don Allah malam a taimaka min da bayani game da sababin da yasa ake yin azumi??

*Amsa:*

Wa alaikum assalam Azumi ginshiki ne, daga cikin turakun musulunci, wadanda addinin musulunci, ba zai cika ba sai da su, Allah da manzonsa sun yi umarni da shi, saboda wasu muhimman manufofi, ga wasu daga ciki :

*1.* Samun tsoron Allah, saboda mai azumi yana barin abin da yake so saboda Allah, hakan zai sa, ya kara samun tsoron Allah.

*2.* Samun kariya daga Shaidan, saboda azumi yana takure hanyoyin Shaidan, wannan ya sa zunubai suke karanci a Ramadan.

*3.* Tuna talakawa da wahalar da suke ciki, saboda duk lokacin da mai kudi ya dandana yunwa zai tuna halin da talakawa suke ciki .

*4.* Sabawa rai wajen barin abin da take so, da kuma hakuri akan abin da take sha'awa.

*5.* Kankare zunubai da kuma samun daukakar daraja, saboda azumi yana gyara zuciya, da kuma rai.

*6.* Samun lafiyar jiki, saboda azumi yana kariya daga cututtuka masu yawa, kamar yadda likitoci suka tabbatar da hakan.

*7.* Ta hanyar azumi mutum zai saba da yin aikin don Allah, saboda azumi sirri ne tsakanin Allah da bawansa.
Allah ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*
29/1/2013

Daga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*
Share:

Ramadhaniyyat@1439H [3] - Sheikh Dr. Muhd Sani Umar R/lemo

*Ramadhaniyyat@1439H [3]*

*Daga Sheikh Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*

Tahajjudi

Allah Ta'ala yana cewa:
(Da daddare kuwa sai ka yi tsayuwar dare da shi (Alqur’anin) qarin (daraja) ne gare ka, tare da qaunar Ubangijinka ya tashe ka a matsayin sha-yabo ("watau matsayin mai ceto"). Isra'i, aya ta 79.

A Makka ne Allah ya shar'ata wa Annabinsa (S.A.W) tsayuwar dare watau sallar "Tahajjudi". Wannan dalili ne da yake nuna falalar wannan salla. Domin Allah ya shar'anta Annabi (S.A.W) mafi girma kuma mafi falalar ayyuka a Makka. Shar'anta wani aiki tun a farkon Musulunci dalili ne dake nuna girmansa da falalarsa, saboda haka ne ma aka shar'anta Tauhidi tun a Makka, hakanan aka kuma shar'anta wasu daga cikin rukunan Musulunci tun a farko-farkon Musuluncin.
Share:

Audio:-Darasin Tafsirin Al-Qur'an na Watan Ramadan 1439/2018 - Dr.Muhammad SANI Umar R/Lemo

Darasin Tafsirin Al-Qur'an na Watan Ramadan 1439/2018

Rana ta 0(2)

Tare da Dr.Muhammad  SANI Umar R/Lemo

17-05-2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO A WAYOYINKU SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya.


Share:

Audio:-Ramadan Tafsir 1439/2018 ( Darasi na 2) - Sheikh Abdurrazaq Yahaya Haifan



Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 2

Tare da: Sheikh Abdurrazaq Yahaya Haifan

2/9/1439
18/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO A WAYOYINKU SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya.


Share:

Audio:-Ramadan Tafsir 1439/2018 (Darasi na 2) - Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 2

Tare da: Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo

2/9/1439
18/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO A WAYOYINKU SAIKUBSHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya.


Share:

Audio:-Ramadan Tafsir 1439/2018 ( Darasi na 1) - Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tare da: Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya.


Share:

Audio:- Ramadam Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) - Dr. Jabir Sani Maihula



Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tare da: Dr. Jabir Sani Maihula

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇


Ayi saurare Lafiya.


Share:

Audio:- Ramadam Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) - Sheikh Muhammad Kabiru Haruna Gombe

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tare da: Sheikh Muhammad Kabiru Haruna Gombe

2/9/1439
18/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya


Share:

Saturday 19 May 2018

Audio:- Ramadam Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) - Sheikh Abdurrazaq Yahaya Haifan

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Suratul Ibrahim Ayah 1-5

Tare da: Sheikh Abdurrazaq Yahaya Haifan

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya.


Share:

Audio:- Ramadan Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) - Dr. Muhammad Mansur ibrahim sokoto

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Suratul Nur 1-2

Tare da: Dr. Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto

Malam yaja hankali sosai akan masifar da take fadawa Mazinci

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya
Share:

Friday 18 May 2018

Audio:- Ramadan Tafseer 1439/2018 (Darasi na 1) -.Sheikh Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tare da: Sheikh Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya.
Share:

Audio:- Ramadan Tafseer 1439/2018(darasi na 1) - Mal. Umar shehu Zaria

TAFSIRIN RAMADAN 1439/2018

Darasi na 1

Daga bakin: _Umar Shehu Zaria_

Alhamis 1 Ramadan, 1439 (17/05/2018). Masallacin Aliyu Usman Kurmin Mashi, Kaduna.

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare Lafiya


Share:

Audio:- Lecture A Ramadan - Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Lecture A Ramadan

Tare da: Sheikh Aminu Ibrahim daurawa

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi Saurare Lafiya


Share:

Audio:- Ramadam Tafseer 1439/2018 (darasi na 01) - Sheikh Musa Yusuf Asadussunnah

Ramadan Tafsir 1439 2018

Darasi na 1

Tafsir Yamma

Tare da: Sheikh Musa Yusuf Asdusunnah

1/9/1439
17/5/2018

DOMIN SAUKO DA WANNAN AUDIO SAIKU SHIGA WANNAN BLUE RUBUTU DAKE KASA 👇👇👇

DOWNLOAD AUDIO NOW

Ayi saurare lafiya

Kuci gaba da kasancewa da wannan shafin akowa da yaushe

More Tafseer is loading 100%.......

Share:

Video:- Ya masu wadata zasu More Watan A Ramadan - Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

JAMI'AR RAMADAN [ZUWA GA MAWADATA]

YAYA MASU WADATA ZASU MORE A WATANA
RAMADAN

Daga👇
*SHEIKH AMINU IBRAHIM DAURAWA*

Domin sauko da wannan Video saiku shiga wannan blue Rubutu dake kasa👇👇👇

DOWNLOAD VIDEO NOW


Ayi saurare Lafiya

DAGA
ZAUREN FIQHUS SUNNA / MIMBARIN SUNNAH


Share:

Wednesday 16 May 2018

Shin yana halasta a nemawa dan bidi'a gafara da rahamar Allah??

SHIN YA HALASTA A NEMAWA DAN BID'AH GAFARA DA RAHAMAR ALLAH?

Farko dai Aqeedar Al-Wala'u Wal Bara'u (Soyayya da kiyaya) ginshiki ne na Addini, wajibine Musulmi ya so 'yan uwanSa Musulmi kuma yaki kafirai kamar yadda wajibine Dan Salafiyyah yaso 'yan uwan sa kuma yaki 'yan bid'ah GWARGWADON ABINDA YAKE TARE DA SU NA BID'AH KAMAR YADDA ZAI SO SU GWARGWADON ABINDA YAKE TARE DA SU NA SUNNAH. Idan kuma bid'ar ta kafircine to wannan babu wani nau'i ko kaso na soyayya da yake da shi daga Musulmai.

Sai dai shi wannan kiyayyar ba a sake ake yin sa ba, akan yi dubi ne zuwa ga maslaha, wani lokaci bayyana shi kiyayyar shine Daidai, wani lokaci kuma kuskure ne sbd rashin maslaha dake ciki.

2- Nemawa dan bid'ar da bid'arSa ta kafircine gafara da rahamar Allah to, wannan kuskure ne kuma haramunne domin Allah Madaukaki ya hana.
Shaikhul Islam Ibnu Taimiyah yace:
من علم منه النفاق والزندقة فإنه لا يجوز لمن علم ذلك منه الصلاة عليه وإن كان مظهرا للإسلام.
الفتاوى الكبرى (3/18).
Wanda aka san Munafunci da Zindiqanci tattare da shi to, bai halasta ga wanda yasan hakan yayi masa sallah ba koda kuwa ya kasance yana bayyana Musulunci.

2- Dan bid'ar da bid'arSa bata kai ga kafirci ba to, ya halasta a nema masa gafara da rahamar Allah Madaukaki domin shi yana matsayin Musulmi mai sabo da zunubi ne.

Shaikhul Islam Ibnu Taimiyyah yace:
فكل مسلم لم يعلم أنه منافق جاز الاستغفار له، والصلاة عليه وإن كان فيه بدعة أو فسق لكن لا يجب على كل أحد أن يصلي عليه.
منهاح السنة (5/178).
Duk wani Musulmi da ba a san cewa shi Munafuki bane to nema masa gafara ya halasta, da kuma yi masa sallah koda kuwa akwai wani bid'ah ko fasikanci tattare da shi, sai dai bai wajaba akan kowa da yayi masa sallah ba.

Ina jin Sheik Rabee'i Almadkhaly yana da magana irin wannan yace:
أما الترحم على أهل البدع، فإنه يجوز الترحم عليهم، وهذا شيء عليه السلف الصالح ومنهم أحمد بن حنبل، ودل على ذلك نصوص من كتاب الله -تبارك وتعالى- ومن سنة رسول الله عليه الصلاة والسلام، والذي ينازع في هذا جاهل ضال، وصلى الله على نبينا محمد وعلى آله وصحبه وسلم.
شريط بعنوان: لقاء مع الشيخ في مسجد الخير.
Amma nemawa 'yan bid'ah rahama to, lalle ya halasta a nema musu rahama, wannan wani abune da magabata suke kansa, daga cikin su akwai Imam Ahmad dan Hanbal, kuma nassosa daga Littafin Allah da Sunnah sun yi nuni akan hakan, wanda yake jayayya a cikin hakan to shi JAHILI NE BATACCE".

Sbd haka duk wani nassi daga Magabata da yake nuna rashin halascin nemawa 'yan bid'ah gafara da rahama to, za a dauke su ne akan 'yan bid'ah din da bid'ar su ta kai ga kafirci.
Share:

Tuesday 15 May 2018

Tambaya/Amsa:- Shin ya halasta ayiwa mutum Allurar Zazzabi a lokacin Azumi??


*```Assalamu alaikum*```
*```Malam shin ya halasta ayiwa mutum allurar Zazzabi lokacin da yake azumi? nagode*```


_*AMSA:*_
*******

وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،


Ya halatta ga mai azumi ayi masa allura a lokacin da yake azumi da rana.

Amma bai halatta ba ayiwa mutum allurar abinci da rana lokacin da yake azumi. Domin wannan yana daukar hukuncin cin abinci ne da shan abin sha. Yin haka zai zama sanadin karya Azumin Wanda aka yiwa allurar (Allurar abinci ko abinsha). Saboda idan za'ayi allurar da daddare shine mafi a'alaa.

_*(Al-lajnatu al-da'imah lil buhuusil ilmiyyat wal ifta'a, 10/252).*_



والله أعلم،

***********************************


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


_*🌙Tambayoyin*_ _*Musulunci🌙*_
            _*WhatsApp*_ _*Group*_
_*+2347068043652*_
_*+2348164884055*_

Allah yasa mudace.
Share:

Nasiha:- Babana yace naje wurin dabbobi 4 bayan ya mutu!!! - Dr.jamilu zarewa


*BABANA YA CE NA JE WAJAN DABBOBI GUDA HUDU BAYAN YA MUTU!!!.*

Wani Bawan Allah yayi wa Dansa nasiha da
Da yaje wajen wasu Dabbobi guda (4) Amma kar yaje sai bayan ya mutu!!!.

Dabbobin da ya umarce shi yaje wajen su- sune:-

1- Doki.
2- kiyashi.
3-Maciji.
4-Kare.

Bayan mahaifinsa ya
Rasu sai ya fara zuwa Wajen Doki yace, Baba yace in ya mutu in zo
Wajen ka, Doki yace Baban ka yana da hikima, kasan abinda
Yasa yace kazo
Waje na?

Yace a'a Sai Doki yace kalli inda nake zaune ya
Duba yaga wajen duk ya baci da kashinsa, Ga jikin sa duk datti, Sai yace kalli wancan
Matashin dokin👉🐴
Sai yaga wajensa a share anyi masa Wanka ga ciyawa mai
Kyau da ruwa- a gaban sa, sai Doki yace kaga yanzu ni Na tsufa bani da wani
Amfani shiyasa-aka Kyale ni a wulakance, Shi kuma Matashin
Doki yana da karfin jiki, Ana da bukatarsa shiyasa ake kula dashi dan haka BabanKa yana yi maka Nasiha da ka mori Kuruciyar ka wajen Abinda zai amfane ka,
Domin lafiyar ka da Kuruciyar ka mutane Suke bukata inka Tsufa ba ruwan kowa da kai.

Daga nan sai yaje wajen kiyashi 🐜yai
Masa bayani kamar Yanda yaiwa Doki- kiyashi yace, zo muje sukaje wajen mushan
Kyankyaso, yayi kokarin ya jawo shi shi kadai ya kasa, sai yaje ya kirawo yan'uwan sa, suna zuwa suka janye Shi.
yace Baban ka
Yana nufin komai
Zaka yi ka hada kai Da yan'uwan ka karkayi kai kadai.

Daga nan sai yaje wajen Maciji 🐍 ya Tarad dashi a cikin
Kogo a la6e yace, yanzu ma, yunwa nakeji, da zan futa a ganni
Kashe ni za'a yi, sai Dare yayi sahu ya dauke, nake futa, ba Wani abu, da ya jawo min wannan bakin Jini sai Bakina da
Harshena😛

Babanka yana nufin ka iya
Harshan ka, ka kiyayi barin zance.

Daga nan sai yaje wajen kare🐺 shima
Yai masa bayani, sai yace, zo muje cikin Gari, suna zuwa sai Yara suka fara jifan
Kare, da kyar suka sha, sai kare yaja shi
Wajen mafarauta suna Zuwa sai Suka fara Murna suna kiran sa
Da sunaye kala-kala Wannan ya jefa masa Nama wannan yana Shafa Shi yana Dariya😀😀.
sai kare Yace Baban ka yana
Nufin ka-kasance cikin Wadanda suke sonka Kuma, ake ganin
Mutuncinka, kuma Aka san Darajar ka, Kaga misali a kai na.

Allah yasa mu Amfana.

Ameen ya Allah

*Dr. Jamilu Zarewa*

Allah yabamu ikon Aiki da Abinda muka karanta.
Share:

Archive

Unordered List

Support