January 2017 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Tuesday 3 January 2017

Hukuncin MMM Business

Hukuncin MMM Business
An dade ana tambayata hukuncin MMM Business daga ciki akwai tambayar da akayimin a July da ya shude a A.B.U Zaria bayan na kamala wata public lecture, kuma yanzu haka akwai tambayoyi da yawa acikin inbox dina. Ko nace ban saniba ko na kyale saboda bani da cikakken bincike akai, amma yanzu nayi bincike akai. Abubuwan da na bincika kafin wannan fatwa sune:
i) Website din MMM
ii) Website din Securities and Exchange Commission, Nigeria, domin jin ra’ayinsu gameda MMM
iii) Online Videos da documentaries gameda MMM Business ciki harda 41 mins video na kaddamar da business din a Nigeira
iv) Tattaunawar da wasu ‘yanuwa sukayi gameda Bussiness din.
Bayan haka nafito da natija kamar haka:
1) MMM Business kamar yadda matar da tayi presentation din shi a Nigeria ta bada definition shine: “MMM is a platform that links [a] giver to the receiver… and when I give I get rewarded for it.” [ Mai bayarwa ya baiwa mai nema domin wanda yabayar ya samu fa’ida] Wannan shine definition din da kowa yake bayarwa koda yake wani lokacin kalimomin sukan sha ban ban amma ma’anar daya ce.
2) Wannan business din baya halasta domin shine ainihin ﺭﺑﺎ ﺍﻟﻔﻀﻞ ” wanda Musulunci ya hana. Ka bada kudi ga mai nema domin a mayarma ka da fiye da abinda ka bayar. Ko kafin ka bayar za’a baka faidar ko bayan ka bayar duka dayane, ko wanda ka baiwa bashi zai baka ko ta wata hanya za'a karbo maka duka daya ne. Ba dole bane sai lokacin da za’a mayar maka ne za’ayi Karin ba, ko wane lokaci Karin zai shiga haram ne, don wannan aka haramta ﺑﻴﻊ ﺍﻟﻌﻴﻨﺔ ” a Musulunci. A MMM za’a baka faidar 30% tun kafin a karbi kudinka.
3) Wannan Business din yana da hadarin gaske domin haramtaccen business ne a Nigeria da kasashe da yawa. Securities and Exchange Commission, Nigeria sun yi gargadi da hana jama’a shiga wanna business da kiransa illegal kamar yadda suka fada a wani article da sukayi publishing a website din su a ranar 30/08/2016 sukace: “The general public is hereby advised to distance themselves from this online scheme. Please note that anyone that subscribe to this illegal activity does so at his/her own risk.” Irin wanna kadai ya isa ya hana wanna Business din
4) Kasashe dayawa sun haramta wannan Business ga jama'ar su domin ganin cewa ba tabbas akwai rudi aciki. Cikin kasashen da suka hana akwai China da South Africa. Samun rudi ﻏﺮﺭ a business zai iya zama dalilin haramcin sa a musulunci.
5) Duk mai hankali ya dibi Business din yasan akwai rudu ciki maiyawan gaske, kuma yasan karshensa jama’a da yawa zasu rasa dukiyar su. A musulunci idan mutun zai bada bashi saida shaidu guda biyu sai idan ya amince da wanda zaibaiwa, a MMM zaka bayarda dukuyarka ga wanda baka sani ba. Saboda hakane ma hukumomi suke yaki dashi. Duk abinda masana sukace karshen sa akwai hadari mai girma to wanna ma ya isa ya haramtashi a Musulunci.
Allah yayi man jaogora.
Jabir Sani Maihula, Nottingham, UK.
15/11/2016
Share:

Abubauwa 4 masu matukar riba a rayuwar mu

*ABUBUWA 4 MASU MATUKAR RIBA ARAYUWAR MU.*

1. SHIRU yana kawo Aminci, Annabi (SAW) ya ce, "wanda yayi imanida ALLAH da ranar karshe ya fadi alheri ko yayi shiru".

2. BIYAYYA tana kawo DAUKAKA, Sayyidina Ali R/A yace, "wanda ya kaskantarda kai ga ALLAH, to ALLAH zai daukakashi"

3. KYAUTA tana kawo MATSAYI, Annabi (SAW) ya ce, "kuyi kyauta za kuso juna".

4. GODIYA Tana kawo KARI, ALLAH (SWT) yace, "idan kun gode zan kara muku. Allah yasa mu dace. Ameen summa Ameen.

Share:

Nasihohi 35 zasu taimakeke wurin samun ingantaçciyar rayuwa

*NASIHOHI 35 zasu taimakeka wurin samun ingantacciyar rayuwa*
______________________________________
1- ka fara yininka da sallar asubahi da azkar domin samun rabo da tsira.

2- ka zarce da istgfari har sai shaidan ya debe
tsammanin samun rabo a jikinka.

3-kar ka daina addu'a dumin itace igiyar tsira

4-ka tuna cewa mala'iku suna rubuta maganganunka.

5-kyawun yatsu shine ka rika qidaya TASBIH dasu.

6- idan ka shiga damuwa da qunci kace" la ila ha illallah".

7- ka sayi addu'ar talakawa da soyayyan marayu da kudadenka.

8-doguwar sujada 1 wanda aka yita saboda tsoron ALLAH yafi maka bene da aka gina na zinari.

9- ka tauna magana kafin kafadeta domin tana iya zama ajalinka.

10- ka guji addu'ar wanda aka zalunta da hawayen wanda aka hana.

11- kafin ka karanta jaridu da mujallu mai zai hana.kafara karanta alqur'ani.

12- ka zama dalilin gyaruwan iyalanka.

13- ka tilastawa ranka wurin bin dokokin Allah ,
domin ita rai tana umarni ne da sabon Allah.

14- kafin tsufar iyayanka ka daure ka samu yardarsu.

15-tsoffin tufafinka sababbi ne a wurin talakawa.

16- kar kayi fushi , domin rayuwa kadan ce ba kamar yadda kake tsammani ba.

17- tare dakai akwai wanda yafi kowa qarfi yafi kowa wadata, shine Allah.

18- kar ka rufe qofar tuba saboda sabon Allah.
19- sallah itace mafi alkhairin abun da zata taimakeka akan musibu da wahalhalu.

20- ka nisanci munanan zato, zaka huta kuma zaka hutar.

21- dalilin kowane damuwa juyawa Allah bayane, ka juyo zuwa gareshi mana.

22-kayi sallah irin wacce kakeso a shigar dakai qabari tare da ita.

23- idan kaji wanda yake gulma , kace dashi: yaji tsoron Allah.

24-ka dawwamar da kanka wurin karanta suratul MULK domin tana tseratarwa.

25- wanda aka hana( yayi hasara) shine wanda aka hanawa sallar dake cike da tsoron Allah , da idon dake zubar da hawaye.

26- kar ka cutar da bayin Allah nagari wadanda suka shagaltu da bautar Allah.

27- ka sanya soyayyar ka duka zuwa ga Allah da manzonsa.

28- ka yafewa wanda yayi gulmarka, domin ya baka kyautar kyakyawan aikinsa ne.

29- Sallah da ambaton Allah da karatun alqur'ani alqawurane masu nauyi akan qirjinka.

30- duk wanda ya tuna da zafin wuta zai iya hakuri akan sabon Allah .

31- indai ana dare gari yana wayewa, to watarana sai labari tsanani zai zama sauqi.

32- ka nisanci ANCE-KACE ( jita-jita) domin kai game da ayyuka kamar dutsene.

33- kayi sallah da tsoron Allah , domin duk abun da zakayi bayan sallar bai kai sallah ba.

34- ka sanya alqur'ani daf dakai , domin karanta aya daya acikinsa yafimaka duniya da abun dake cikinta.

35- rayuwa akwai dadi, mafi dadin rayuwa shine kaganka da iimaninka.
________________________________
ALLAH Yasa Mudace!
____________________________
*TEMAKA KA YADA DOMIN ANFANIN ALUMMA*
Share:

Addu'o'i guda (12) da suka zo a hadisai

ADDU'O'I GUDA (12) DA SUKA ZO A HADISAI:

1. LA'ILAHA ILLAHUWA WAHADAHU LA SHARIKA LAHU LAHUL MULKU WA LAHUL HAMDA WA HUWA ALA KULLI SHAY'IN QADIR (10 ko 100)

Manzon Allah (S.A.W) yace wanda ya fadi wannan 100 za'a kankare masa zunubai dari, kuma za'a rubuta masa kyawawan aiki dari, kuma a wannan rana bawani da zaizo da wani aikin alheri kamar nasa sai wanda ya fadi fiye da abinda ya fada kuma za tsareshi daga sharrin shaidan da duk wani abun qi kuma yace babu wani zikiri ko addu'a kamar Hailala..

2. LA'ILLA HA ILLAHUWA MALIKUL HAQQUL MUBIN. (100)

Manzon Allah(S.A.W) yace duk wanda ya fadi wanann sau dari a rana bashi ba talauci kuma za'a tsareshi daga fitinar kabari

3. BISMILLAHI RAHAMANI RAHEEM, LA HAULA WALA QUWATA ILLA BILLAHIL ALIYUL AZEEM. (100)

Manzon Allah(S.A.W) ya cewa da Sayyadina Aliyu ba wanda zai fadi wannan kalmomi duk wata masifa ko bala'i duk rintsi sai ya fita.

Annabi Alaihisalam yace wanda yake karanta Lahaula bashi ba talauci kuma kanzi ce daga kanzi na aljanna tana toshe kofofi saba'in na bala'i da cuta mafi kankanta ciki shine bacin rai da damuwa kuma yace: duk wanda samun arziki yayi masa wuya to ya yawaita yin LAHAULA...

Kuma duk wanda yake karanta BISMILLAH (21) bayan isha'i cutar annoba ko ta hauka bazata taba kamashi ba kuma bazai mutuwar fuju'an ba..

4. SUBAHANALLAHI WA BI HAMDIHI. (100)

Shine Tasbihin Annabi Nuhu, shi kuma mala'iku suke Allah yake arzuta dukkan halittar shi..

5. HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKIL(450)

Shine Tasbihin da Annabi Ibrahima yayi lokacin da aka jefa shi wuta Allah ya mayar masa da ita sanyi itace sahabbai sukayi lokacin yaqin Badar Annabi yayi nasara kuma basu ji tsoron kafirai ba duk da sunfisu yawa..

6.  LA ILA HA ILLA ANTA SUBAHANAKA INNI KUNTU MINAL ZALIMIN (sau 41 ko 100)

Manzon Allah(S.A.W)  yace: "Addu'ar Annabi Yunusa lokacin da yake cikin kifi babu wani mumini da zai roki Allah wani abu dake damunsa face Allah ya maganata masa. Kuma yace Ismullahil Azeem, sunan Allah ne da in akayi addu'a yake amsawa, kuma idan aka rokeshi yake bayarwa itace addu'ar Annabi Yunusa.

7. ASTAGFURULLAHA LAZI LA'ILA HA ILLAHUWAL HAYYUL QAYYUM WA ATUBU ILAIHI. (100)

Manzon Allah(S.A.W) yace: Ba wanda zai fadi haka fache an gafarta masa duk zunubansa koda sun kai kunfar kogi. kuma Alqawarin Allah ne a cikin suratul hudu, duk wanda ya lazumci Istigfari zai jiyar dashi dadi kuma yabashi arziki kan arziki kuma zai bashi girma da daukaka..

8. SUBAHANALLAHI WABI HAMDIHI SUBAHANALLAHIL AZEEM ASTAGFRULLAH(100 kafin Asubah)

Wani Sahabi yazo wajen Manzon Allah Alaihisalam yayi masa kukan duniya ta juya masa baya(talauci)  yasanar dashi tasbihin Mala'iku sai Annabi yasanar dashi yace ya ringa karantashi bayan raka'a tainul fajar kafin Asuba. Bai gushe ba sai da ya dawo wajen Annabi Alaihisalam yace Allah yabashi duniya (arziki)  har ya rasa inda zai kaita..

9. YA HAYYU YA QAYYUM LA'ILA HA ILLA ANTA(sau41)

Imamu Shafi'i (Rahimahullah) yayita mafarki da Annabi sai watarana sai yace shin kasanar dani wani abu da Allah zai dinga haskaka mani kuma ya raya zuciyata akan imani(ibada) sai Annabi ya sanar dashi wannan. Ya ringa yi kafin Asubah ko bayan Asubah sau 41 (Saboda haka ba wanda zai lazumceta sai yazama mai maida hankali akan ibada kuma yazama wanda mutane zasu dinga jin maganarsa kuma abin so a cikinsu...

10. SUBAHANALLAHI(33) WAL HAMDULLAHI(33) WAL LAHU AKBAR(34) da dare kafin bacci

Wannan shine Tasbihin da Annabi ya bawa Sayyada Fatimah lokacin da ta nemi Annabi ya bata hadimi sai ya sanar da ita wannan tasbihi da ta ringa yi kullum kafin ta kwanta bacci shine mafi alkhairi a gareta da yabata hadimi..

11. SUBAHANALLAHI(10) WALHAMDULLAHI(10) WALLAHU AKBAR(10) bayan Salloli biyar

Watarana Ummu Sulaim tazo wajen Annabi Alaihisalam tace ya sanar da ita wani abu da zata dinga rokon Allah dashi sai yace tayi wannnan tasbihin sai ta roki Allah bukatarta za ace anzartar anzartar (wato an amsa mata abinda ta roka)

12. SALATIN ANNBI (10 ko 100 ko 500 ko 1000 har abinda yayi sama)

Manzon Allah(S.A.W)  yace: "wanda bukatarsa tayi masa wahalar samu to  ya yawaita salati gareni lalle yana tafiyar da damuwa da bakin ciki da kuncin rayuwa kuma yana yawaita arziki da kuma biyan bukatu.

Kuma Imamu Ghazali yace: Duk wanda yake salati Annabi 500 kullum bashi ba talauci kuma bazai mutu ba sai yaga Annabi Alaihisalam.

Ubangiji ALLAH ya sa mu dace duniya da lahira, 😭😭😭

Don Allah ina roqon ku da ku saka ni cikin addu'ar ku, Allah yabamu lafia, arziqi da wadata, ya albarkaci rayuwar mu, ya amince mana duniya da lahira, ya kuma magance mana duk abinda yake damun mu, ya biya mana dukkan bukatun  Dan shiga group din mu mai tarin Albarka na🕌THE HOLY RAMADAN 🕋 sai katura slm tare da rubuta Ramadan ta wannan number 08037902332  pls share it to others groups
Share:

Yadda ake wankan janaba dana haila

*YADDA AKE WANKAN JANABA DANA HAILA*
.
.
*A ciki zamuga Bayanin Maniyyi da Maziyyi da Wadiyyi da Jinin haila* inkayi seka turama wani
:
DAGA ZAUREN
*Khulafa'ur-rashiidun*
:
Lucture 8
.
Muna me farawa da sunan ALLAH m rahama me jinqai, Tsira da amincin ALLAH su tabbaga ga shugaban halitta Annabi Muhammad (ﷺ).  Tare dashi da iyalansa da wadan da suka biyo bayan shi da kyautatawa irin au Sayyidina Abubakar, umar, usman, aliyu, dalha, zubair ibin auwam da sauran su.
;
A har kullum muna bada hakuri ga masu chanjamana  post suyi hakuri dan girman ALLAH kada ku chanja mana wannan post in, idan ka chanja ka cuci wanda ze karanta na gaba, ka hanashi  sauraron darasin baya dakuma nagaba wanda zamu gabatar da yaddan ALLAH,  Idan bazaka iya tura ma wani ba, ka hakura kada ka chanja mana post in mu dan ALLAHU.
°°°°°°°°°°°
*
*BABBANCHI TSAKANIN MANIYI DA MAZIYI DA WADIYI, DA RUWAN CIWON SANYI!!*
*
🚩MANIYYI-Yana fita ayayin babban sha'awa, kokuma ta hanyan mafarki, ko saduwa,ko wasa da Al-aura, kalan shi fari ne, yana da kauri sannan yana dan wari haka,  yayin fitan shi yana tunkudan juna, inyafiata kuma yana sa kasala./ kalan maniyin mace  yana daukeda launin yellow.
:
🚩MAZIYYI-wani kalan ruwan ne shima dayake fitowa daga Al-aura yayi qaramar sha'awa, maziyyi baida kauri yana nan da yaukie, yana fita yayina baligi yafara tinanin kusantan mace komace tayi sha'awa  namiji, idan ya fito tsarki kawai akemar sannan a wanke gurin.
:
🚩WADDIYI- Wani ruwa ne makaman cin maniyyi amma baya fita se bayan mutum ya girma wato ya tsufa, yawanci kuma yafi fitowa bayan gama fitsari
:
🚩CIWON SANYI-  wani ruwa ne me kauri da wari-wari dayake kwaranya kullum a farjin mata,  batare da wani sha'awa ba, kalan shi yakusa kama da maniyyi, yana fitane sanadiyan cuta, shi wannan yana buqatan inmace ta gani taje asibiti a bata magani!!
🚩
JININ HAILA
*
HAILA
     Shine wani jinin dake fita a farjin mace alhani lafiyarta qalau ba haihuwa tayi ba. Kuma ba kwanciya da wani na miji da yafi qarfinta ya fasa ta ba. Toh wannan shine jinin HAILA.
*
*
Duk sanda aka ga jini a farjin 'ya mace mai shekaru 7,8,9,10,12 ba tare da wani matsala a farjinta koh mahaifarta ba, ba kuma wani na miji da dafi qarfinta ya fasa ya ba toh wannan za abashi hukuncin jinin HAILA.
*
*
Balagar mace yana da alaqa da irin wajan da take rayuwa, yanayin halittar, jin dadinta. Shiyasa wasu suke fara jinin HAILA da wuri wasu koh nasu yake jinkiri.
*Misali;  Mazauna qasashen yammacin duniya inda akwai zafi baza a hada su da wurare irin su qasashen Russia da Afganistan ba sabo da wajene mai sanyin gaske.
.
.
Haka kuma mata masu cin abubuwan gina jiki da 'ya'yan itatuwa dole yanayin jinin su ya bambamta da na wa'yanda basu samu damar cin wa'yannan abubuwa ba.
.
.
LAUNUKAN JININ HAILA
*
(1) BAQI:
      (ba ana nufin baqi kalar gashi ba) ana nufin Ja mai duhu tare da qarni
   [Imam Abu dawud Nisa'e, Imam daru kudini, Ibn Hibban acikin sahihu muslim]
*
*
(2) JA JAWUR A
        Shine asalin launin jini. Yana dauke da qarni
*
*
(3) FATSE- FATSE
        (Kamar gwaiduwar kwai)
*
*
(4) RUWAN QASA
        Yana nan ne kamar qasa da aka kwaba da ruwa., yana da dan duhu duhu.
:
🚩KWANA KIN HAILA
.
.
Kwana kin haila ba a gayyade adadin sa, galibi wasu mata basa wuce kwana 5 zuwa 7 sai dai-daiku daga cikin su da suke zarce hakan.
.
.
ALAMUN DAUKEWA JININ HAILA
*
*Bushewar fargi qarqaf
        Idan farji ya bushe ba wani alama na jini koh kadan. Toh tsarki ya samu sai ayi wanka.
    Anaso a tanadi auduga mai kyau koh wani faril gyalle yadda za asa a farjin a duba domin tabbatar da tsarkakuwar
.
.
*CHANJAWAR KALAR JINI
   Mun riga munyi bayanin kalolin jini, Idan jinin hailarki baqi ne toh randa ya chanja kala ya koma Ja koh fatsi-fatsi bayan kuma kin cika adadin kwanakin da kika saba yi na hailar toh kin samu tsarki. Sai kiyi wanka ki ci gaba da ibadodin ki.
    SAI DE
       Idan wannan kalar jinin da ya chanje wato (istihada, ana qiran sa jinin ciwo koh jinin jijiya) bai dauke ba toh zaki riqa sake alwala a kowacce sallah, ki wanke inda jinin ma ya ta6a. Har sai sanda jinin ya dauke.
Amma idan ya fito bayan kin riga kin fara sallah toh shikenan ki ci gaba da sallarki.
*
🚩JININ BIKIE-/jinin haihuwa, shima kalanshi daya da na Haila, Sedai shimafi tsawon kwanakinshi shine kwana 60.
:
*MIYAKE WAJABTA WANKAN  JANABA?*
:
fitan maniyyi ta  kowacce hanya, in ma ta hanyan biyan buqata da matar ka, ko ta hanyar mafarki, ko kuma ta hanyan jin babban sha'awa da yayi sanadiyan fitan maniyi.
:
Shigar da kan kachiya cikin farji, yana wajabbata wanka koda kuwa baku fitar da maniyyi ba, wanka yawajaba agare ku.
:
Idan mace ta gama jinin Al-ada, da wance jinin haihuwa ya  dauke mata, wannan duka wajibi ne da suyi wanka.
*
Sekuma wankan shiga musulunchi, da wankan daukan harami. sannan se wankan gawa, gawanda ba'a filin yakie ya mutu ba, kokuma wanda ya qone sanadiyan gobara, ko lalacewan gaggan jiki. Sannan anso wanda yayi wankan gawa yayi wanka shima.
*
Wannan kusan sune wajiban wanka Da nasani.
:
*YA AKE WANKAN JANABA?*
*
Daga nana Aisha uwar muminai ALLAH yaqara mata yadda, tace:- "Manzon ALLAH(ﷺ) yakasance idan zaiyi wankan janaba, sai ya wanke  hannayen sa, sannan yayi wanka, sannan ya duddurza, ya tsattsefe gashinsa da hannayen sa, har inda ya tabbatar cewa ya jiqa fatar sa (kai) sai ya kwaranya masa (shi kan) ruwa sau uku, sannan ya wanke sauran jikn sa" tace;  na kasance ina yin wanka nida manzon  ALLAH (ﷺ) A kwary(baho) daya muna kamfata daga cikin ta baki daya"
(bukari da muslim)
:
_Dan uwa ka ta6ayin wankan janaba da matar ka bayan ta haihu sama da yara uku?  ina tinanin tinda kukayi lokacin kuna shekaran farko baku sake yiba_
*
Daga maimuna 'yar haris (R.A) matar Annabi (ﷺ) uwar muminai tace : "naje wajen Manzon ALLAH (ﷺ) da ruwan wanka janaba, sai ya  zuba ruwa da damansa aan hagunsa sau biyu k sau uku, sannan ya wanke hannunsa sau biyu ko sau uku, sannan ya wanke Al-auran sa, sannan ya daki qasa ko bango (in ba qasa a gefan ka zaka iya wanke hannunka da sabulu)  da hannun sa, sau biyu ko sau uku, sannan ya kurkure baki, ya shakie ruwa, ya wanke fuskar sa da damatsan sa, sannan ya kwaranya ruwa a bisa kansa, sannan y wanke jikinsa, sannan ya koma gefe ya wanke qafafunsa" tace " saina zo masa da kyalle (tawul) sai bai kar6e ba, sai ya riqa sharce ruwan da hannayen sa"
:
(Bukari da muslim)
:
_Anan zamu danyi bayani akan goge jiki da hannu, idan ka goge jikinka da hannu sekafi jin dadin wannan wankan, ba'a musu kusa da gida ka jarraba yauinkaje wanka koda kuwa bana janaba ba_
*
Wannan wanka👆🏽👆, haka akeyi idan mutum zeje sallan juma'a, idi, qarama ko babba, haka zalika anayi a wankan haila. idan kayi baka buqatan se ka sake Al-wala kawai sallah zakayi. sabda wankan karan kanshi Al-wala ne.
:
*YA AKE WANKAN HAILA?*
*
An karbo daga Aishata Allah Ya yarda da ita. Lallai Asma'a ta tambayi Manzon Allah (ﷺ)game da wanka haila, sai Yace: Dayarku ta dauki ruwanta da magaryarta tayi tsarki kuma ta kyautat tsarki sa'annan ta zuba ruwa a kanta, kuma ta cuda shi.., cudawa mai tsanani har sai ta sadar da ruwa ga asalin gashinta (tushen sa) sa'annan ta game jikinta da ruwa, sa'annan ta sami wani yanki na auduga mai kanshi ta tsarkaka da ita.
Sai Asma'a tace: Ya ya zata tsarkaka da ita? Sai Manzon Allah (ﷺ) yace: Subhanaallah! Nace tayi tsarku da ita. Sai Aisha tace: Kamar ita (Asma'a) tana boye wannan. Tace ma ta, "Abinda Annabi  (ﷺ)yake nufi shine ki bi gurbin jinin da ita.
:
(Malamai sun hadu akan shi)
*
Batare da tsawai tawa ba idan mace tana jinin haila bayan ta qare zatayi wanka, to wajibi ne akan ta da ta war ware gashin kanta kaman yadda hadisi ya tabbata a bukari hadisi na317  da Annabi (ﷺ) yace ma nana Aisha ta koma ta dakko miqati sannan ta warware gashinta..
:
An fani da magarya da miski  ba qaramin amfani yake dashi ba wajen taimakawa mace,  ki jarraba  baiwar ALLAH.
;
Dangane da wadan da jinin janaba ta same su a lokacin suna jinin Al-aada,  Abinda yafi shine tayi wanka biyu, daga janaba tasameta tayi wankan janaba, sanna idanjini ya dauke tayina haila. Wallahu a,alamu.
;
HARAMCHIN YIN WANKA DA RAGOWAN RUWAN WANKAN DA WANI YAYI AMFANI DASHI.
:
hadisi Sahihi  ya tabbata a cikin  littafin Bulugul maram Annabi ya hana wanka da ragowan ruwan wankan da wani ya rage haka ya hana wanka da ragowan ruwan mace"
*
 A hadisin dake jikin shi kuma an rawaiyo Annabi (ﷺ) yayu wanka da ragowan ruwan wankan matar shi maimuna":/
:
Wannan kusisiyace ta Annabi muhammad (ﷺ)   amma kai bai halatta kayi wanka da ragowan ruwan wankan matarka ba koitatayi da na ka.  Amma ba laipi kuyi wanka tare.
:
********
Idan ka sanar da wani kaima kayi da'awa kuma kayi taimakekkeniya akan biyayya wa ALLAH, Abin da mamaki sosaiakwai wadanda basu sani ba, yakamata kaisar musu,  sedai a kiyayi turawa  a groups inda suke da Dokan hana tura post, idn ka turabaka cire ka, kai kaso.
;
ANAN ZAN DAKATA  SE KUMA IN ALLAH YAKAIMU WANISHIRIN KUMA,  IDAN ALLAH YASO ZAMUYI BAYANI AKAN YADDA AKE WANKAN GAWA IN SHA ALLAHU
-------***-----------
MUHAMMAD AUWAL ABU JA'AFAR AL-POTISKUMAWI
•°°°°°°°°•
02/01/1438-03-10/2016
_________________
masu buqatan kasancewa damu, se su turo da suna da kuma sunan qasar su, a daure ayimana sallama cikakka dan samun lada cikekke.
*
→ MasU buqatan kasan cewa damu a whatsapp.
+2347035269582
+2348063796175
 tare da cikakken suna da kuma cikakkiyar sallama. don samun karatuttukan mu a facebook, saikubi, mobile.facebook.com/Khulafaur-Rashiidun-1812718708973541/ Subhanak Allahumma wabi hamdika Nash hadu anla ila ha illah anta nastagfiruka
Wana tubu ilaik.
Share:

Maganin istihada (zuban jinin haila sama da kanaki, masu yawa !!!)

*MAGANIN ISTIHADA ( ZUBAN JININ HAILA SAMA DA KWANAKII, MASU YAWA!!!)*
:
Daga Zauren
*Khulafa'ur-rashiidun*
:
Assalamu Alaikum warahamatullah  Haqiqa mata dayawa suna fama da cutan ISTIHADA (wato zuban jini sama da kwanakin haila, wata ma nata yanakai wata 3) da lilin haka yasa muka binciko maganin wannan  matsalan.
.
Wasu nasu matsalace ta aljanu, ko sihiri, idan kunyi baiyi amfani ba, ku jarraba yin ruquyya!!.
.            hanya kadan da zaku gane cewa sihirine, idan mijinki yazo miki, sekiga jini ya fara kwaranya!!!  
.
Wata kuma nata jijiya ne yake samun matsala, seya fara zubar dajini!!
________________________________
📍- Ta samu Saiwar magarya ta tafasa da 'yar jar kanwa seta rinqa sha kamar so uku a rana
.
📍 *Ta samu ganyen runhu, balma se ta hade guri daya ta jiqa ya kwana seta riqa Sha.*

📍 Ko kuma ta tafasa' ya'yan kabewa tare da madara ko nono, amma ta tafasa su a tare seta riqa sha insha Allah ze tsaya.

📍 *Ko ta samu garin habbatus sauda da ganyen na'a na'a a tafasa asha*
~_____________________________~          
         
:
A lokacinda kikaga Jini ya miki yawa wato ya wuce iyaka to kinemi wannan maganin, sauki kuma yana wajan ALLAH.
.
Kusani ba wata cuta face Seda ALLAH ya sauke mata Maganin ta, sekuma ya bar Saukin a gurin shi, ka nemi magani ka sha wanda ya dace da sunnah.
______________________________
*Hakan koda bakya fama da wannan matsalan to kiyi Qoqarin haddace wa, saboda mata dayawa suna fama da wannan matsalan.*.
.
.         hukuncin me fitar da wannan jinin, na wuce iyaka(JININ CUTA), fatawa mafi saukie shine  tayi alwala a kowacce sallah Tare dayin tsarki, kaman yadda takeyin tsarkin fitsari.
.
Wannan jinin baya haramta mijinkibya sadu dake. Kaman yadda baya hana sallah da karatun qur'ani da sauran ibadu, wallahu a,alamu
.
*Kutayamu yadashi  amma dai a kiyayi turawa zauren da kukasan zasu cire ku.  Fatan mu ALLAH  ya daura mu akan dai-,dai yasa mu gama da duniya lapiya, yasa wannan aikin danshi mukeyi.*
_______________________________
*MUHIMMIYAN SANAR WA*
      _Muba masu bada magani bane sannan ba kowacce cuta bane, muka sani maganin ta, idan munce bamu sani ba, to bamu saniba shiyasa, mukace bamusani ba!!…_
~;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;;~
*29-01-1438*-31/10/2016
.
→ MasU buqatan kasan cewa damu a whatsapp.
+2347035269582
+2348063796175
 tare da cikakken suna da kuma cikakkiyar sallama. don samun karatuttukan mu a facebook, saikubi, mobile.facebook.com/Khulafaur-Rashiidun-1812718708973541/ Subhanak Allahumma wabi hamdika Nash hadu anla ila ha illah anta nastagfiruka
Wana tubu ilaik.
Share:

Sayyidul istigfar

*بسم الله الر حمن الر حيم*

*SAYYIDIL ISTIGFARIN*
 (shugan Istigfari)
.
.
.DAGA ZAUREN
*Khulafaur-rashiidun.*
.
Lucture (13)
                          Assalamu alaikum    warahamatullah    innal hamdulillah nahamaduhu wanasta inuhu Wana uzubillahi minash shaidanur rajim.
.
*wassalatu wassalamu ala nabiyyina muhammad (ﷺ) wa'alihi wa sahabihi waman tabi ihsani ila yaumin din,*  godia ya tabbata ga ALLAH ubanigiji ma madukakin sarki daya azurtamu da manzon rahama(ﷺ), wanda yadamu da damuwar mu, meson kowa ya shiga Aljannah, ALLAH  ka sanya muna ciki.
.
*'yan uwa dukkan wani me zunubi, a ranan gobe qiyama se an mar hisabi, koya shaa! ko a kama shi!!, sakamakon kasancewan mu Yan adam masu rauni, hakan yasa kullum muna cikin zunibi!! se ALLAH yace;-*
 "...LALLE ALLAH YANASON MASU TUBA KUMA YANASON MASUTSARKI"   awani gurin yace  ''DA ANBATON ALLAH AKE SAMUN NUTSUWA".
.
Annabi alaihissalam ya koyar da sahabbai istigarai me girma, wanda harta kai ana kiranta da shugaban istigfari.
.
Tabbas badan muna tuba ma ALLAH ba, da tuni an shafar damu daga doron qasa.
.
Kasancewar zunuban mu sunyi mana yawa!!
.
shiyasa nayi tinanin tuna tar damu wannan addu,an dan mu sake hadda ce ta, wato *sayyidil istigfari*
_________________________________________
.
*اللَّهُمَّ أَنْتَ رَبِّي لَّا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ، خَلَقْتَنِي وَأَنَا عَبْدُكَ، وَأَنَا عَلَى عَهْدِكَ وَوَعْدِكَ مَا اسْتَطَعْتُ، أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا صَنَعْتُ، أَبُوءُ لَكَ بِنِعْمَتِكَ عَلَيَّ، وَأَبُوءُ بِذَنْبِي فَاغْفِر لِي فَإِنَّهُ لَا يَغْفِرُ الذُّنُوبَ إِلَّا أَنْتَ*
.
*Allaahumma 'Anta Rabbee laa 'ilaaha 'illaa 'Anta, khalaqtanee wa 'anaa 'abduka, wa 'anaa 'alaa 'ahdika wa wa'dika mas-tata'tu, 'a'oothu bika min sharri maa sana'tu, 'aboo'u laka bini'matika 'alayya, wa 'aboo'u bithanbee faghfir lee fa'innahu laa yaghfiruth-thunooba 'illaa 'Anta.*
_____________________________________________

_*"YA ALLAH kaine ubangiji na, babu abin bautawa da gaskiya SAI kai. Kai ka halicceni, kuma ni bawanka ne, kuma ina kan alqawarin dana yimaka ( na kadaitaka da bauta)  akuma alqawarin d kayimin ( nashigar da wanda baiyimaka shirk ba, gidan Aljannah) gwargwadon ikona. Ina neman tsarin-ka daga sharin abinda na aikata, ina tabbatar da ni'imar ka gare ni, kuma ina tabbatar da zunubi na; ka gafartamini, domin ba bai gafarta zunubi se kai)"*_
.
_(Bukhari 7/150, -Nasa'i, da-Tirmizi.}_
_________________________________________
 Karka 6ata lokacin ka akan ibadan da ba daga Annabi  (ﷺ) take Ba.
dan haka yanada kyau duk abinda zamuyi in ya shafi addini to mu tabbatar munada hujja me kyau.
.
*Manzon ALLAH yace duk wanda ya karanta ta, da safe ba abinda ze hanashi shiga aljanna sedai mutuwa* (in baka shigaba to baka mutu ba, matuqar kana kan aqida ingan tacciya).
.
Haka zalika inka karanta da yamma, *amma duk dahaka anason ka  karantata da kowana lokaCi bayan kayi na safe da yamma.*
.
Sannan daga cikin falalan ta tana kankare zunubi me tsoka  wanda ya guda na tsakanin ka  ALLAH.
.
_Kasani me karatu Allah fa baya yafe lefin wani akan wani idan ka cuci wani to Allah ze bi masa hakkinsa koda kayi wannan Adu,ar bazata hana a tambayeka hakkin wani ba a lahira dan haka ka gyara tsakanin ka da Allah sannan kadawo ka gyara tsakanin ka da mutane._
.
_Sannan akwai wani hadisi shima a cikin bulugul maram inda Annabi   (ﷺ) yace: duk wanda yake karanta *Ayatul kursiyu* da *Kul'huwallahu* qafa uku a ko wace salla ta farilla to babu abinda ze hanaka Shiga Aljanna sedai in baka mutuba._
.
_Bukhari da Muslim ne suka rawai to shi ibn Hibbana ya ingantashi._

*Yan uwa akwai addu'oi dayawa ,idan mundage dayinsu zasu rabamu da fadawa bidi,a dakuma shirka da kuma dena ziyar tan bokaye..*
_______________________________________
     _lucture mu nagaba in sha ALLAHU 👉🏿(KIYI HANKALI DA QAWA YENKI DANGANE DA NEMAN MAGANI)  tsokaci duk wanda yaje wajen boka ko dan duba hakiqa ya kafurta inbaiyi imandashi ba baza,a kar6i sallan sa na kwana 40 ba!!!_
________________________________________
Dan uwanku a musulunci
.
*Muhammad Auwal Abu-Ja'afar*
*Al-potiskumawi*
.
08/03/1438;:;: 08/12/2016
.
→ MasU buqatan kasan cewa damu a whatsapp.
+2347035269582
+2348133238265
 tare da cikakken suna da kuma cikakkiyar sallama. don samun karatuttukan mu a facebook, saikubi, mobile.facebook.com/Khulafaur-Rashiidun-1812718708973541/ Subhanak Allahumma wabi hamdika Nash hadu anla ila ha illah anta nastagfiruka
Wana tubu ilaik.
.
Kuna iya samun mu ta wannan addreshin
http://Www.khulafaurrashidun.blogspot.com
Share:

Wasiyan mala'ika jibrilu ga annabi S A W

WASIYYAR MALA'IKA JIBRILU GA ANNABI S.A.W

Wata rana Mala'ika Jibrilu S.a.w yazo wajan Ma'aikin Allah s.a.w sai yace dashi;

{Ya Muhammad, ka rayu aduniya duk yanda ka keso,watan wata rana kai mai mutuwane, kayi duk aikin da kakeso watan wata rana za'a sakamaka abinda ka aikata,Kuma kaso duk wanda kaso,watan watarana zaku rabu dashi.

Lallai kasani, mafificiyar daukakar Mumini itace Sallar dare,Kuma mumini yana samun daukakane gwargwadon yin afuwarsa ga yan uwansa Mutane.

#SaheehuT Targheeb~824

Fadakarwa.

Acikin wannan wasiya mai tsada zamu dauki guziri guda biyar~5

1-Duk yanda ka zauna aduniya watarana sai ka mutu, da akwai wanda zai zauna aduniya bai mutuba da Annabi s.a.w

2-Dukkan ayyukan da ka aikata anan duniya sune Allah zai saka maka agobe alkiyama.

3-Kuma duk yanda kake so ko kaunar mutum wata rana sai mutuwa ta rabaku.

4-babban aikin da yake sanya mumini ya samu mafi daukakar matsayi awajan Allah,itace Sallar dare.

5-Idan kana yawan yafiya ga Yan uwanka mutane zaka sami izza da buwaya.

Allah ka bamu ikon kiyaye wannan wasiyaa.
Share:

Archive

Unordered List

Support