January 2019 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Sunday 13 January 2019

SHIN YA HALATTA ARNIYA TA YIWA MUSULMA KITSO ? - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum, shin ya halatta Arniyya ta yiwa musulma Kitso ?

*Amsa*

Wa'alaikumus salam
Ya halatta macen da ba musulma  ba ta yiwa musulma kitso, saboda a zancen mafi inganci, al'aurar mace ga 'yar'uwarta mace, shi ne daga guiwa zuwa cibiya, babu bambanci tsakanin kafira da musulma a cikin haka, domin a zamanin Annabi s.a.w. Yahudawa mata suna shiga gidan Annabi s.a.w., kuma ba'a samu suna yin shiga ta musamman ba idan suka ga za su shigo, saidai in kafirar tana da wani sharri da ake jin tsoro, to wannan mace za ta iya suturta daga ita, sannan kuma mutukar akwai musulma to ita ta fi dacewa ayi hulda da ita .

ALLAH NE MA FI SANI

*Dr. Jamilu Yusuf Zarewa*

5/1/2014
Share:

FITINA A KWANCE TAKE, ALLAH YA LA'ANCI MAI TADA ITA ! - Dr Jamilu Yusuf Zarewa



*Tambaya*

Assalamu alaikum. malam ina da tambaya hadisin da yake magana akan fitina tana barci duk Wanda ya tashe ta Allah Yana tsine masa. Hadisin ya inganta ko a'a ? Kuma a Wani littafi da Shafi yake?

*Amsa*

Wa'alaikum salam
tabbas mai Kanzul -ummal da kuma mai jami'ussagir sun rawaito shi a matsayin hadisi, saidai Albani ya raunana shi a Dha'iful jami'i da kuma Silsilatil-ahdithil- dha'ifah a 7\259, saboda a cikin sanadin hadisin akwai mutanen da ba'a san su ba.

Allah ne mafi sani.

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*

2/1/2014
Share:

FATAWAN RABON GADO (192) - Dr Jamilu Yusuf Zarewa



*Tambaya*

Assalamu alaikum.malam mutum ne ya rasu ya bar mata daya bai taba haihuwa ba, kuma iyayen shi duk sun rasu, sai kannan shi maza da mata wadanda suke uwa daya uba daya da kuma wadanda suke uba daya kawai, yaya rabon gadon zai kasance?

*Amsa*

Wa alaikum assalam, Za'a raba abin da ya bari gida hudu, a bawa matarsa kashi daya, ragowar sai a bawa 'yan'uwansa wadanda suke uwa daya uba daya su raba, duk namiji ya dau rabon mata biyu.

'Yan uba ba sa gado mutukar akwai namiji shakiki.

Allah ne mafi sani

*Dr. Jamilu Zarewa*

14/12/2018

Daga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*
Share:

DUK CINIKAYYAR DA ZA'A YANKE RIBAR DA ZA'A KARBA KAFIN A FARA, BATACCIYYA CE ! - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum.
Malam akwai wani cinikayya na hadin-guiwa  da ake yi a DANTATA SUCCESS AND PROFITABLE COMPANY, ga yadda abin yake:

1- Zaki sa kudin ki tsawon wata shida ana biyanki duk wata, Zaki sami 40 percent (kaso arbain cikin Dari) duk wata tsawon wata shida. Misali in kin sa *N300,000* duk wata Zaki sami *N120,000* tsawon wata 6, Uwar kudin ki da riba Zaki sami *N720,000*

2- tsari Na Biyu Zaki sa kudin ki tsawon shekara Zaki dinga karbar 25 percent (kaso 25 cikin Dari Na abinda kikasa) . misali kinsa *N300,000* duk wata Zaki dinga karbar *N75,000* har tsawon wata goma sha biyu, gaba daya Uwar kudi da riba Zaki sami *N900,000*
Idan kin zabi biya daya Ne in kudin ki suka shekara zaa biyaki *N 960,000

Don Allah malam muna so a taimaka mana da hukuncin sharia game da wannan tsari, saboda mutane da yawa suna shiga ?

*Amsa*

Wa alaikum assalam
Irin wannan ciniki shi ake cewa (Mudharaba) ko kuma (Kiradh)a wajan Malikiyya, wato mutum ya bada kudi wani ya juya masa.

Saidai Wannan sigar da aka yi bayani  batacciya ce kuma haramtacciya a wajan malaman musulunci saboda ta kunshi zalunci da kuma rashin tabbas wato (Garar), da yiwuwar  cutar da daya daga cikin abokan tarayya, saboda an sanya ribar ne ta Uwar-kudi ba daga ribar da za'a samu ba.

Duk lokacin da aka shardanta riba daga cikin Uwar kudi za'a cutar da daya daga cikin abokan tarayya a ciniki saboda ribar in ta yi yawa an zalunci mai uwar kudin, idan kuma ribar ta karanta an zalunci mai juya kudin, Ibnu Taimiyya a cikin Majmu'ul fatawa (28/83) ya nakalto Ijma'in Malamai akan haramcin duk Mudharabar da ta kunshi shardanta riba daga Uwar kudi.

Ingantaccen hadin guiwa a wannan tsarin shi ne wanda za'a cimma daidaito wajan bada wani sashe na daga  abin da aka samu na riba, ba daga Uwar kudi ba.

Duk wanda ya ji tsoran Allah, tabbas zai azurta shi ta inda ba ya zato kamar yadda Allah ya fada a suratu Addalak aya ta:( 3)

Don neman karin bayani duba Al-mugni (5/28) da kuma Almausu'a Alfiqhiyya (8/116).

Allah ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR.JAMILU YUSUF ZAREWA*

17/12/2018
Share:

Zan Iya Tashin Abokina Daga Bacci Saboda Sallah - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu Alaykum wa rahamatullahi wa barakatuhu. Da fatan mallam da duka jama'ar wannan fili na cikin ƙoshin lafiya. Tambaya ta, mallam, ita ce, mutum ne ya ke bacci, ya na cikin baccin nan har lokacin sallah ya yi, shin za'a tashe shi ne daga baccin ya yi sallah? Ko kuwa barin shi za'a yi har sai lokacin da ya tashi da kan shi, sannan ya yi ramuwar sallah?

*Amsa*

Wa alaikum assalam
Za'a tashe shi mana, in har ba lalura ce da shi ba, da zai cutu in ya farka, saboda a taimaka masa wajan aikata Alkairi, da yin sallah a lokacinta.

Allah ya umarci Muminai da taimakekeniya wajan biyayya ga Allah a aya ta (2) a suratul Ma'idah.
Annabi SAW a cikin hadisin Abu-dawud ya yi adduar Rahma ga mutumin da ya ta shi da daddare don ya yi sallah ya ta shi matarsa, in ba ta tashi ba ya yayyafa mata ruwa.
In har bai samu wanda zai tashe shi ba, ya yi sallah bayan lokacinta ya wuce, to Allah ya dauke Alkalami akansa kamar yadda ya zo a hadisi tabbatacce.

Allah ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*

14/12/2018
Share:

Fatawar Rabon Gado 191 - Dr Jamilu Yusuf Zarewa





*Tambaya*

Assalamu alaikum Allah ya gafarta mallam mutum ne ya mutu ya bar
 mahaifiyarshi da yara maza biyu
da mace guda daya da matarshi ya za’a raba gadon. ?

*Amsa*

Wa alaikum assalam Za'a raba abin da ya bari gida (24) a bawa mahaifiyarshi kashi (4) Matarshi kashi (3) ragowar sai a bawa yaran, duk namiji ya dau rabon mata biyu.

Allah ne mafi sani

 *Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*

03/12/2018
Share:

SHIN YA HALATTA ARNIYA TA YIWA MUSULMA KITSO ? - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum, shin ya halatta Arniyya ta yiwa musulma Kitso ?

*Amsa*

Wa'alaikumus salam
Ya halatta macen da ba musulma  ba ta yiwa musulma kitso, saboda a zancen mafi inganci, al'aurar mace ga 'yar'uwarta mace, shi ne daga guiwa zuwa cibiya, babu bambanci tsakanin kafira da musulma a cikin haka, domin a zamanin Annabi s.a.w. Yahudawa mata suna shiga gidan Annabi s.a.w., kuma ba'a samu suna yin shiga ta musamman ba idan suka ga za su shigo, saidai in kafirar tana da wani sharri da ake jin tsoro, to wannan mace za ta iya suturta daga ita, sannan kuma mutukar akwai musulma to ita ta fi dacewa ayi hulda da ita .

ALLAH NE MA FI SANI

*Dr. Jamilu Yusuf Zarewa*

5/1/2014

Share:

FITINA A KWANCE TAKE, ALLAH YA LA'ANCI MAI TADA ITA ! - Dr Jamilu Yusuf Zarewa



*Tambaya*

Assalamu alaikum. malam ina da tambaya hadisin da yake magana akan fitina tana barci duk Wanda ya tashe ta Allah Yana tsine masa. Hadisin ya inganta ko a'a ? Kuma a Wani littafi da Shafi yake?

*Amsa*

Wa'alaikum salam
tabbas mai Kanzul -ummal da kuma mai jami'ussagir sun rawaito shi a matsayin hadisi, saidai Albani ya raunana shi a Dha'iful jami'i da kuma Silsilatil-ahdithil- dha'ifah a 7\259, saboda a cikin sanadin hadisin akwai mutanen da ba'a san su ba.

Allah ne mafi sani.

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*

2/1/2014

Share:

FATAWAN RABON GADO (192) - Dr Jamilu Yusuf Zarewa



*Tambaya*

Assalamu alaikum.malam mutum ne ya rasu ya bar mata daya bai taba haihuwa ba, kuma iyayen shi duk sun rasu, sai kannan shi maza da mata wadanda suke uwa daya uba daya da kuma wadanda suke uba daya kawai, yaya rabon gadon zai kasance?

*Amsa*

Wa alaikum assalam, Za'a raba abin da ya bari gida hudu, a bawa matarsa kashi daya, ragowar sai a bawa 'yan'uwansa wadanda suke uwa daya uba daya su raba, duk namiji ya dau rabon mata biyu.

'Yan uba ba sa gado mutukar akwai namiji shakiki.

Allah ne mafi sani

*Dr. Jamilu Zarewa*

14/12/2018

Daga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*

Share:

DUK CINIKAYYAR DA ZA'A YANKE RIBAR DA ZA'A KARBA KAFIN A FARA, BATACCIYYA CE ! - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum.
Malam akwai wani cinikayya na hadin-guiwa  da ake yi a DANTATA SUCCESS AND PROFITABLE COMPANY, ga yadda abin yake:

1- Zaki sa kudin ki tsawon wata shida ana biyanki duk wata, Zaki sami 40 percent (kaso arbain cikin Dari) duk wata tsawon wata shida. Misali in kin sa *N300,000* duk wata Zaki sami *N120,000* tsawon wata 6, Uwar kudin ki da riba Zaki sami *N720,000*

2- tsari Na Biyu Zaki sa kudin ki tsawon shekara Zaki dinga karbar 25 percent (kaso 25 cikin Dari Na abinda kikasa) . misali kinsa *N300,000* duk wata Zaki dinga karbar *N75,000* har tsawon wata goma sha biyu, gaba daya Uwar kudi da riba Zaki sami *N900,000*
Idan kin zabi biya daya Ne in kudin ki suka shekara zaa biyaki *N 960,000

Don Allah malam muna so a taimaka mana da hukuncin sharia game da wannan tsari, saboda mutane da yawa suna shiga ?

*Amsa*

Wa alaikum assalam
Irin wannan ciniki shi ake cewa (Mudharaba) ko kuma (Kiradh)a wajan Malikiyya, wato mutum ya bada kudi wani ya juya masa.

Saidai Wannan sigar da aka yi bayani  batacciya ce kuma haramtacciya a wajan malaman musulunci saboda ta kunshi zalunci da kuma rashin tabbas wato (Garar), da yiwuwar  cutar da daya daga cikin abokan tarayya, saboda an sanya ribar ne ta Uwar-kudi ba daga ribar da za'a samu ba.

Duk lokacin da aka shardanta riba daga cikin Uwar kudi za'a cutar da daya daga cikin abokan tarayya a ciniki saboda ribar in ta yi yawa an zalunci mai uwar kudin, idan kuma ribar ta karanta an zalunci mai juya kudin, Ibnu Taimiyya a cikin Majmu'ul fatawa (28/83) ya nakalto Ijma'in Malamai akan haramcin duk Mudharabar da ta kunshi shardanta riba daga Uwar kudi.

Ingantaccen hadin guiwa a wannan tsarin shi ne wanda za'a cimma daidaito wajan bada wani sashe na daga  abin da aka samu na riba, ba daga Uwar kudi ba.

Duk wanda ya ji tsoran Allah, tabbas zai azurta shi ta inda ba ya zato kamar yadda Allah ya fada a suratu Addalak aya ta:( 3)

Don neman karin bayani duba Al-mugni (5/28) da kuma Almausu'a Alfiqhiyya (8/116).

Allah ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR.JAMILU YUSUF ZAREWA*

17/12/2018

Share:

Zan Iya Tashin Abokina Daga Bacci Saboda Sallah - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu Alaykum wa rahamatullahi wa barakatuhu. Da fatan mallam da duka jama'ar wannan fili na cikin ƙoshin lafiya. Tambaya ta, mallam, ita ce, mutum ne ya ke bacci, ya na cikin baccin nan har lokacin sallah ya yi, shin za'a tashe shi ne daga baccin ya yi sallah? Ko kuwa barin shi za'a yi har sai lokacin da ya tashi da kan shi, sannan ya yi ramuwar sallah?

*Amsa*

Wa alaikum assalam
Za'a tashe shi mana, in har ba lalura ce da shi ba, da zai cutu in ya farka, saboda a taimaka masa wajan aikata Alkairi, da yin sallah a lokacinta.

Allah ya umarci Muminai da taimakekeniya wajan biyayya ga Allah a aya ta (2) a suratul Ma'idah.
Annabi SAW a cikin hadisin Abu-dawud ya yi adduar Rahma ga mutumin da ya ta shi da daddare don ya yi sallah ya ta shi matarsa, in ba ta tashi ba ya yayyafa mata ruwa.
In har bai samu wanda zai tashe shi ba, ya yi sallah bayan lokacinta ya wuce, to Allah ya dauke Alkalami akansa kamar yadda ya zo a hadisi tabbatacce.

Allah ne mafi sani

*Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*

14/12/2018

Share:

Fatawar Rabon Gado 191 - Dr Jamilu Yusuf Zarewa





*Tambaya*

Assalamu alaikum Allah ya gafarta mallam mutum ne ya mutu ya bar
 mahaifiyarshi da yara maza biyu
da mace guda daya da matarshi ya za’a raba gadon. ?

*Amsa*

Wa alaikum assalam Za'a raba abin da ya bari gida (24) a bawa mahaifiyarshi kashi (4) Matarshi kashi (3) ragowar sai a bawa yaran, duk namiji ya dau rabon mata biyu.

Allah ne mafi sani

 *Amsawa*✍🏻

*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*

03/12/2018

Share:

Archive

Unordered List

Support