SHIN YA HALATTA ARNIYA TA YIWA MUSULMA KITSO ? - Dr Jamilu Yusuf Zarewa ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Sunday 13 January 2019

SHIN YA HALATTA ARNIYA TA YIWA MUSULMA KITSO ? - Dr Jamilu Yusuf Zarewa


*Tambaya*

Assalamu alaikum, shin ya halatta Arniyya ta yiwa musulma Kitso ?

*Amsa*

Wa'alaikumus salam
Ya halatta macen da ba musulma  ba ta yiwa musulma kitso, saboda a zancen mafi inganci, al'aurar mace ga 'yar'uwarta mace, shi ne daga guiwa zuwa cibiya, babu bambanci tsakanin kafira da musulma a cikin haka, domin a zamanin Annabi s.a.w. Yahudawa mata suna shiga gidan Annabi s.a.w., kuma ba'a samu suna yin shiga ta musamman ba idan suka ga za su shigo, saidai in kafirar tana da wani sharri da ake jin tsoro, to wannan mace za ta iya suturta daga ita, sannan kuma mutukar akwai musulma to ita ta fi dacewa ayi hulda da ita .

ALLAH NE MA FI SANI

*Dr. Jamilu Yusuf Zarewa*

5/1/2014

Share:

0 comments:

Post a Comment

Archive

Unordered List

Support