February 2018 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Saturday 24 February 2018

AUDIO : Falalar Boye Fushi Daga Sheikh Ja'afar Mahmud Adam Kano


Manzon Allah s.w.a Yana cewa duk wanda yake da damar nuna fushi amma boye  fushi a gobe kiyama Allah zai sashi aljannah yace zabi  wanda kake so a cikin Hurul'ini

Boye fushi kamar sadaki ne na hurul'ini a gobe kiyama.


Manzon Allah yasan abu ne mai matukar wuya mutum yana da damar nuna fushi amma hadiye shi saboda abu ne  mai matukar kuna a wajen hadiyewa balanata yanzu mutum na neman zalunci su kadai balanta an tabashi.

Kaji kamar baka ji ba, ka gani kamar baka gani ba lallai abu ne mai samama mutum daraja a gobe kiyama.

Babu masu boye wannan boye fushi sai masu hakuri da imani.

Ga Audion nan domin saurare

Download Audio here
Share:

Thursday 22 February 2018

Wanda ya rasa wani Bangare na sallar janaza, ya zaiyi??



*WANDA YA RASA WANI BANGARE NA SALLAR JANAZA, YA ZAI YI?*

*TAMBAYA*
Assalamu alaikum, Allah ya karawa wannan zaure albarka inada tambaya kamar haka shin sallah Jana,iza Ana rama kabbarar da aka rasa, misali kamar idan ba,a Fara sallah da mutum ba har yayi missing din wani bangare daga cikin sallah idan liman ya sallame shima sai yarama.

*AMSA*
Wa alaikumus salaam, Dukkan wanda ya rasa wani bangare na sallan jana'iza zai dauki raka'ar da ya tarar a matsayin raka'ar shi ta farko, idan liman ya idar sai shi ya ciko.

Babban Malami, Sheikh Abdulaziz Bn Baaz, Rahimahullah, ya ce:

*_Sunna ga dukkan mutumin da ya rasa wani bangare na kabbarbari na sallan jana'iza, shi ne ya biya wadannan kabbarbari, saboda fadin Manzon Allah, sallallahu 'alaihi wa sallama: "Idan an tsayar da salla, to ku zo mata kuna tafiya kuma ku kasance masu natsuwa, duk abun da kuka riska ku sallata, abin da kuma ya kubuce muku to ku ciko"..._* A duba مجموع الفتاوى 13/149.

An tambayi Malaman لجنة الدائمة للإفتاء cewa:

Mene ne hukuncin mutumin da ya rasa kabbarori uku a sallan janaza sai ya riski kabbara daya?

Sai suka bayar da amsa da cewa:

*_Zai cike sallan janazan ta yanda zai yi kabbarori uku a matsayin ramuwa kafin a dauke janazar daga inda take..._* a duba fatawa ta 8/399.

Wallahu A'alam.

21/02/2018

Daga: *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*
Share:

Archive

Unordered List

Support