September 2018 ~ Duniyarfatawa.com™

вarĸarĸυ da zυwa ĸυcι gaвa da ĸaѕancewa da wannan ѕнaғιn doмιn cιgaвa da ѕaмυn ιnganтaттυn ғaтawa a cιĸιn vιdeo/aυdιo ĸo rυвυтυ daga мalυмa daвan-daвan na aнlυѕ-ѕυnnaн мυngode

Recent Post

Friday 28 September 2018

Labarin Yajuju wa majooju - Zauren Fiqhu



LABARIN YAJUJU WA MAJOOJU


***********************************
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM

Tsira da aminci su tabbata bisa Mafi girman matsayi acikin dukkan halittun Allah, Shugabanmu Annabi Muhammadu Tare da iyalan gidansa tsarkaka da Sahbbansa zababbu.

Yau in sha Allahu muna tare da daliban ZAUREN FIQHU WHATSAPP (3) kuma zamu gudanar da darasinmu akan tarihin wasu Qabilu ne wadanda yanzu haka suna nan da ransu. Amma ba zasu bayyana ba, sai akarshen zamani. Sunansu YAJOOJU WA MAJOOJU.

Acikin Alqur'ani, Allah ya bamu labarin tafiye tafiyen da Sarki Dhul-Qarnaini yayi.

Acikin tafiye tafiyen nasa, yaje wajen da rana take faduwa, sannan yaje yaje mahudarta.

Sannan a tafiyarsa ta uku kuma yaje chan karshen duniya, kusa da bangon duniya.

Achan din ne mutanen wajen suka kawo masa Qara. Suka ce masa :

"YA KAI DHUL QARNAINI, HAKIKA YAJOOJU DA MAAJOOJU MASU 'BARNA NE ADORON QASA. SHIN KO ZAMU SANYA MAKA WANI HARAJI (WANDA ZAMU BAKA) DOMIN KA SANYA WATA KATANGA ATSAKANINMU DA TSAKANINSU?".

Shi kuma sai yace "ABINDA UBANGIJINA YA BANI, SHINE YAFI ALKHAIRI. KU DAI KAWAI KU TAIMAKENI DA QARFI (KARFIN JAMA'A)  ZAN SANYA WATA KATANGA MAI QARFI TSAKANINKU DA TSAKANINSU".

Daga nan Dhul-Qarnaini ya kama aiki, ya gina wata Katafariyar katanga ta Qarfe da dalma, wacce tafi Qarfin wadannan mutanen su haurata.

SHIN SU WANENE YAJOOJU WA MAJOOJU??

Bari mu leka cikin litattafan Tafseeri da hadisan Manzon Allah (saww) domin mu binciko labarinsu.

Al Imam Alqurtubiy (rah) daya daga cikin jerin Manyan Malaman tafseeri, yace "An samo hadisai da labarai dangane da fitowarsu da kuma siffofinsu. Kuma cewa suna daga cikin 'ya'yan YAFITHU ne.

Sayyiduna Abu Hurairah (rta) ya ruwaito daga Manzon Allah (saww) yana cewa:

"An haifa ma Annabi Nuhu ('ya'ya guda uku) SAAMU, da HAAMU, da YAFITHU.

Shi samu shine ya haifi Larabawa da Mutanen Farisa (Iran kenan) da kuma mutanen Ruum (turawa kenan). Kuma akwai alkhairi acikinsu.

Shi kuma YAFITHU shine ya haifi YAAJOOJ da MAJOOJU da Turkawa da mutanen Saqalib, amma babu alkhairi acikinsu.

Shi kuma HAAMU shine ya haifi Qibtawa (mutanen Misra) Da Barbar (berbers, wasu mutanen daji ne, masu tsananin Yaki) da kuma Bakaken fata".

Abu Sa'eed Alkhudriy (ra) ya riluwaito daga Manzon Allah (saww) yana cewa:

"(Su Yajooju wa Majooju) Mutum guda daga cikinsu ba zai mutu ba, har sai bayan ya haifi 'Ya'ya Maza guda dubu daga cikin tsatsonsa.

Imamul Qushairiy ya ambato Abu Sa'eed Alkhudriy yana cewa "SU QABILU ASHIRIN DA BIYAR NE ABAYAN SU YAJUJU WA MAJUJU. MUTUM GUDA DAGA CIKINSU DA KUMA CIKIN YAJOOJU WA MAJOOJU BA ZAI MUTU BA, HAR SAI NAMIJI GUDA DUBU SUN FITA DAGA CIKIN TSATSONSA.

Lallai bisa ga wadannan hadisan zamu iya cewa indai kowanne mutum guda daga cikinsu yana haifar mutum dubu, to lallai ba Qaramin yawa ne dasu ba.

Abdullahi bn Mas'ud (ra) yace: "Na tambayi Manzon Allah (saww) dangane da Yajooju wa Majooju, Sai shi Mai tsira da aminci) yake cewa :

"SU YAJUJU WA MAJOOJU AL'UMMATAI NE GUDA BIYU. (WATO YAJOOJU DABAN, MAJOOJU MA DABAN).

Kowacce Al'ummah daga cikinsu tana Qunshe da wasu Al'ummatai (ko Qabilu) guda dubu dari hudu (400,000 tribes). Kuma kowacce al-ummah babu wanda yasan iyakar yawansu sai dai Allah".

"KUMA MUTUM GUDA DAGA CIKINSU BA ZAI MUTU BA, HAR SAI BAYAN AN HAIFA MASA MAZAJE GUDA DUBU DAGA CIKIN TSATSONSA, KOWANNENSU YANA DAUKE DA KAYAN YAQI".

Sai wani Sahabi yace "Ya Rasulallahi, Siffanta mana su mana!".

Sai yace : "SU NAU'I UKU NE (KAMANNIN HALITTARSU).

1. AKWAI WADANDA SUKE (DA TSAWO) MISALIN BISHIYAR NAN TA URZU. WATA BISHIYA CE NAI TSAWON ZIRA'I 'DARI DA ASHIRIN.

2. SAI KUMA WASU NAU'I WADANDA TSAYINSU DA KAURINSU DUK 'DAYA NE - WATO ZIRA'I GUDA. (TSAWONSU ZIRA'I DAYA, KAURINSU MA HAKA).

3. SAI KUMA WANI NAU'IN WADANDA SUKE (DA MANYAN KUNNUWA) SUNA SHIMFIDA KUNNE 'DAYA SUYI KAFITA DASHI.

'DAYA KUNNEN NASU KUMA SUYI MAYAFI DASHI".

BA ZASU WUCE TA KUSA DA WATA GIWA KO NAMAN DAJI, KO ALADE (AL-HANZIR) BA, FACHE SAI SUN CINYESHI.

KUMA DUK WANDA YA MUTU DAGA CIKINSU MA, CINYESHI SUKE YI (WATO SUNA CIN NAMAN 'YAN UWANSU).

NA GABANSU SUNA KASAR SHAM, 'YAN BAYANSU KUMA SUNA KHURASAN (WATO AFGHANISTAN).

ZASU SHANYE KOGUNAN GABASHIN DUNIYA, KUMA ZASU SHANYE BUHAIRATUT TABRIYYAH (WANI KOGI NE A KASAR FARISA).

AMMA ALLAH ZAI KANGESU DAGA SHIGA GARIN MAKKAH DA MADINA DA BAITUL MAQDIS".

Sayyiduna Aliyu bn Abi Talib (ra) yace: "akwai wasu nau'i daga cikinsu wadanda tsawonsu kamar kamu guda ne (wato tsawon yatsa guda biyu).

Suna da farata (farce) da kuma Hakora irin na Zakoki. Da jiki irin na dabbobi, suna kuka irin na Kuraye, kuma suba taruwa kamar yadda tattabaru sukeyi.

Suna da gashi duk jikinsu, wanda yake karesu daga Sanyi da zafi.

Suna da manyan kunnuwa guda biyu. Daya kunnen na gashi ne. Suna fakewa daga Sanyi acikinsa. 'daya kunnen kuma na fata ne. Dashi suke fakewa alokacin zafi.

Suna tonon wannan katangar, sai sun kusan tureshi sai kuma Allah ya mayar dashi kamar yadda yake.

Sai sunce gobe zamu tureshi "IN SHA ALLAHU TA'ALA". Sannan zasu tureshi, su fito (zuwa cikin duniya).

Mutane zasu tsere daga garesu acikin manyan katangu da benaye (saboda suna kashewa duk mutanen da suka kama, sannan su cinye namansa 'danye).

Daga nan sai su rika harba kibiyoyinsu zuwa sararin samaniya, sai adawo musu da kibiyoyin chakude da jini.

Daga nan sai Allah ya sanya musu wata chuta (mai kamar tsotsa) a wuyansu, ya hallakar dasu.

Manzon Allah (saww) yace "NA RANTSE DA WANDA NUMFASHINA KE HANNUNSA, DABBOBIN DA SUKE DORON QASA SAI SUN QOSHI SUNYI KITSE SOSAI DAGA CIN NAMAN YAJOOJU WA MAJOOJU DA KUMA JININSU

Imamu Ahmad da Tirmiziy, da Ibnu Maajah ne suka ruwaitoshi.

Abu Sa'eed Alkhudriy (ra) yaji Manzon Allah (saww) yana cewa:

"Za'a bude ma Yajooju wa Majooju Qofa su shigo cikin duniya, kamar yadda Allah ya fada, "SUNA TAFIYA DA SAURI TA CIKIN DUKKAN SASANNI".

Mutane zasu firgita su gudu daga garesu, zasu fake daga garesu acikin katangu da birane. Kuma zasu taho da dabbobinsu ma tare dasu.

Mutanen Yajooju wa Majooju din zasu yi yawo adoron Qasa, zasu shanye duk ruwan dake doron Qasa.  Wani daga cikinsu zai wuce ta kusa da wani kogi, sai yace "Da chan kuwa, akwai ruwa anan wajen".

Bayan kowanne mutum ya riga ya buya daga garesu, sai wani daga cikin YAJOOJU WA MAJOOJU yace : "Wadannan duk Mazaunan doron Qasa ne, mun gama dasu. Saura yanzu mazauna cikin Sammai".

Sai wani daga cikinsu ya harba kibiyarsa zuwa sama, sai adawo masa da ita, tana jike da jini. Suna cikin wannan halin sai Allah ya turo musu da wata irin chuta awuyansu, kamar tsutsotsin nan na Aljaraad zasu kama wuyansu. Zasu mutu, ko motsinsu ba Za'a ji ba.

(Imamu Ahmad ne ya ruwaito).

Awata ruwayar kuma, Annabi Eisa (as) shine zai yi addu'a sai Allah ya turo da Mala'iku suzo su kawar da Gawarwakin YAJUJU WA MAJUJU din, bayan sun cika duniya da warinsu.

Anan zamu tsaya sai a karatu na gaba. In sha Allahu zamu dauko wani batun mu tattauna akai.

DAGA ZAUREN FIQHU WHATSAPP (3). 05/09/2015.
Share:

Sunday 23 September 2018

Shin ko kunsan Cewa Sallar Jana'Iza kabbarorinta suna wuce 4

*JANA'IZA A MAHANGAR SUNNAH??-07!!*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*KITABU WAS SUNNAH*
.
.
*ﻣﺠﻠﺲ ﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ*
📓📔
Watsaps
08036222795
09031200070
.
.
...
Yau 09-04-1439 wacce tayi dai dai da, 27-12-2017, Cigaban Lekca mai taken *JANA'IZA A MAHANGAR SUNNAH:*
...
=
Wannan shine bayani na Bakwai:
=
=
*«ﺇِﻥَّ ﺍﻟْﺤَﻤْﺪَ ﻟِﻠَّﻪِ، ﻧَﺤْﻤَﺪُﻩُ ﻭَﻧَﺴْﺘَﻌِﻴﻨُﻪُ، ﻣَﻦْ ﻳَﻬْﺪِﻩِ ﺍﻟﻠﻪُ ﻓَﻠَﺎ ﻣُﻀِﻞَّ ﻟَﻪُ، ﻭَﻣَﻦْ ﻳُﻀْﻠِﻞْ ﻓَﻠَﺎ ﻫَﺎﺩِﻱَ ﻟَﻪُ، ﻭَﺃَﺷْﻬَﺪُ ﺃَﻥْ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻟَّﺎ ﺍﻟﻠﻪُ ﻭَﺣْﺪَﻩُ ﻟَﺎ ﺷَﺮِﻳﻚَ ﻟَﻪُ، ﻭَﺃَﻥَّ ﻣُﺤَﻤَّﺪًﺍ ﻋَﺒْﺪُﻩُ ﻭَﺭَﺳُﻮﻟُﻪُ*
_Bayan haka yanzu kuma kai tsaye zamu shiga bayanine gameda Sallar jana'iza, Ita sallar gawa fardu kifaya ce wato wasu suna dauke ma wasu, idan akayi mutuwa a gari ko unguwa sai wasu jama'a koda 'yan kadanne daga cikin mutanen wannan unguwar suka tsayu sukaima wannan gawar sallah to shikenan babu zunubi ko laifi akan sauran jama'a wadanda basuzo akayi wannan sallar dasu ba, Amma mutane guda biyu sukuma ba dole bane sai anyi musu sallar gawa. Nafarko shine yaro qarami wanda bai balaga ba, idan yaro karami ya rasu to ba dole bane sai kunyi mishi sallah, kuna iya rungumar gawar kawai kuje ku birneta ba tareda kunyi mata sallah ba, amma dai babu laifi idan kunyi sallar saboda akwai gagarumin lada wanda ake samu idan akayiwa gawa sallah kunga sai ku rabauta da wannan ladan, na biyu kuma shine shahidi wanda ya mutu a fagen jihadi shima wannan ba dole bane akanku sekunyi masa sallah, amma dai shima din kuna iya yin masa sallan dan ku samu ladanda ake samu bawai saboda yin sallar wajibi bane****_
      _Sannan kuma wannan sallar anso yazama ansamu a qalla sahu uku koda kuwa mutanen basuda yawa koda basu wuce mutane gomaba inso samune arabasu zuwa sahu uku, inkuma sunyi yawa to ana iya qara yawan sahun yafi uku*****_
      _Kuma ya halasta ayima gawa sallah acikin masallaci, amma bai halasta ayi sallar a tsakanin qaburbura ba, wato qabarine guda biyu ko sama da haka sai a ajjiye gawa a tsakaninsu sai ayimata sallah anan wajan wannan bai halastaba kenan dai zamuce baya halasta ayima gawa sallah acikin maqabarta****_
     _Sannan kuma idan gawar namijine to limamin zai tsayane saitin kansa idan kuma mace ce liman zai tsaya tsakiyarta daidai saitin qugunta****_
      _Yadda akeyin sallar kuwa shine: Anayin kabbara hudu, ko biyar ko shida ko bakwai ko takwas ko tara, amma anfi yin guda hudu sedai ana duba darajar mamacin da irin gwagwarmayar da yayi wajen cigaban addini sai ayi masa kabbarorin gwargwadon yadda akaga ya kamata walau biyar ko shidan har zuwa tara****_
       _Amma yanada kyau shi liman kafin afara sallah ya gayawa mutane cewa kabbara kaza zamuyi, sedai kuma fadin hakan ba dole bane akan liman amma dai kyautatawace dan susan abinda zakayi, sannan kuma yanada kyau kagaya musu bayan kowacce kabbara ga abinda ake karantawa saboda mafiya yawan mutane sallar kawai sukeyi amma basusan mene ake fadi abayan kowacce kabbara ba, wannan kuma yafarune saboda irin yadda mutane mukayi sakaci da karatu muka kauracewa malamai babu ruwanmu da yin sallah kamar yadda Annabi (s.a.w) ya koyar kawai dai munayin sallah ne kamar yadda mukaga wadansu mutane sunayi, wanda kuma hakan babu shakka kuskure ne yazama wajibi akanmu lallaine mutashi munemi ilimin addininmu saboda yazama duk ibadarda zamu aikata to munayintane akan basira dakuma haske na ilimi****_
        _Hujja kuwa akan cewa ana yin kabbarori sama da hudu a sallar gawa daga ciki akwai hadisi wanda Imamu Muslim ya ruwaito acikin littafinsa hadisi mai lamba 957, Abu Dawuda 3181, Tirmizi 1028, Ibnu Majahi 1505****_
       _Hujjarmu kuma akan cewa anayin  kabbarbari masu yawane da gwargwadon irin gudun muwarda mamacin yaba addini, Akwai hadisin Sallar gawar Imrana Dan Hussaini wanda Aliyu dan Aby Dalib ne yayi masa kabbarori tara, gakuma sallar gawar Sahlu dan Hanif wanda shima dai Aliyu dinne yayi masa sallah da kabbarori shida, sannan ya fuskanci mutane yace aishi Sahlu ya halarci yaqin badar, wannan hadisin yana cikin Ahkamul Jana'iz shafi na 113, Har ila yau kuma akwai sallar gawar Abu Qatada wadda itama dai Sayyidina Ali ne yayi kuma yaimasa kabbara bakwai shima Abu qatada ya halarci yaqin badar****_
      _Hakadai sayyidina Aliyu yakasance yanayin kabbarori shida zuwa sama akan duk sahabinda ya halarci yakin badar, amma sahabinda baije badar ba Aliyu yanayin masa kabbara biyar ne, Tabi'i kuma wanda ba sahabi ba Aliyu yanayi masa kabbara hudu****_
      _Kankat kuma idan muka duba hadisin Sallar gawar Sayyidina Hamza Annabi (s.a.w) yaimasa kabbarori guda tara shima, Imamu Dahawi ya ruwaito wannan acikin Sharhu Ma'anil Athar mujallad na farko shafi na 290*****_
=
=
_Zan tsaya anan saikuma darasi nagaba idan Allah yakaimu***_
.
_Almajirinku ne kamar kullun_
.
```Jameel Alhassan Haruna kabo```
.
_(Abu khausar)_
.
 .
Allah ta,ala ya tsaremu
.
.
.
Zaku iya samun shafinmu na facebook tawannan hanyar
https:/t/m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-1522000298067561/
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Subhanak Allahumma wabi hamdika ash hadu anla ila ha illa h anta astagfiruka  Wa,atubu ilaika
Share:

Archive

Unordered List

Support